Sashe 83
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
59&60. Haka al'amuran suka ci gaba da gudana. Aka ciro wa Ubaida kyakkawar jaririyarsu mai cike da koshin lafiya. Ita kam gida aka tafi da ita. Tunda bata da lafiya. Sai da aka yi sati biyu da haihuwar sannan aka yi taron suna. Ranar sunan na ga dukkan y'anmata da muka taso har ma da k'anwata kowa da d'a ko y'a a hannunta amma ban da ni. Na shige d'akinmu na dinga kuka. Yaya Ummi ce kawai ta gano ni. Dan kuwa ita Gwaggo ma bata dauki hakan a matsala ba ne. Yaya Ummi ce ta dinga ba ni hakuri tare da cewa gaba'daya ma auren naku wata shad'aya ne fa Yabi. Sannan shekarunki shabakwai. Ban da an miki auren wuri ai har yanzu baki isa auren ba, bare aje ga zancen haihuwa. Wadanda suka zarce shekaru goma babu haihuwa fa sai su ce da Ubangiji me? Ki shiga a hankalin ki fa". Sai da ta shawo kaina sannan muka fita cikin jama'a. Watanni uku bayan haihuwar Ubaida mai gidan burodi da Tijjani yake zuwa ya rasu. Magada sun yi yawa a kai dan hakan suka siyar da shi. Wanda ya siya kuwa kabila ne dan haka ya sallami galibin ma'aikatan ya debo nasa y'anuwan ya zuba. Cikin wadanda aka sallama kuwa har da Tijjani. Ban gane aikin da burodin da yake yi rufin asiri ne mai yawa ba, sai bayan an rasa shi. Domin ba'a dauki kwanankin sati ba sai da muka ga gurbinsa. A da bamu da matsalar abin karya wa tunda burodi har yawa yake yi mana. Ga kuma donougt da ita ma bata yanke mana. Ko baki na yi zan basu. Sannan da daddare ba kasafai muke cin abinci ba, sai kawai muci da shayi mu yi kwanciyarmu. Sannu a hankali rashin samun ku'di ya dabaibaye shi k'warai da gaske. Tunda aikin saka tiles sai an samu. Haka na satellite shima hab'o ne. Tsawon wata biyu muna cikin wannan yanayin. Ga shi ya k'i yarda na taimake shi, tunda ni kullum kasuwancina tamkar ba iya mutane ne suke zuwa mini kitso da lalle ba. Saboda yadda Ubangiji ya ba ni jama'a. Tunda kayan abincinmu suka k'are kullum cikin dirka mana garin rogo ko wainar fulawa yake. Tausayi yake ba ni saboda gaba'daya ya zama desperate kullum cikin yawon neman abin da zai yi yake. Wani lokacin na ga ya fita da takardunsa, wani lokacin idan ya fita tun safe sai azahar zai dawo, haka kuma yake dawowa sai dai na gan shi da garin rogo da siga a leda. Ni kuwa sai ya bani filawa a farar leda ya ce ki yi abin da zai samu da ita, ki mini hakuri dan Allah" Rannan na gaji da bin ra'ayinsa muna kwana da yini cikin yunwa. Na ha'da kan ku'din da na samu na kwanaki biyu na rubuta koamai da nake bu'kata a takarda na bawa almaajirina na ce ya je ya ce nawa ne kudinsu. Jimawa ka'dan ya dawo ya ce "Wai dubu sha bakwai da dari shida". Na kirga na ga har da canjn dubu uku ya rage mini. Dan haka na cire canjin na ba shi ya tafi ya karbo mini. Na duba na ga komai ya cika. Na kinkima na kai kicin na shiryasu. Na ba shi gudar dubu akan ya siyo mini gawayi rabin buhu, da kuma danyar kubewa. Domin na tsani siyan abu dan tsurut a leda kullum. Ina da gas amma na bar shi sai iya da safe zamu dinga amfani da shi. Ya siyo mini bushasshe kuma manya dan jos haka ma kubewar. Na ce "To je ka dawo anjima ka'dan." A lokacin kuwa yammaci ne sosai. Dan haka na ha'da wuta na dora tuwon garin masara wanda yana cikin siyayyar da na yi d'azun. Na gama na kwashe na mayar da miya. Magariba tana yi ina kammala wa. Sai da na yi sallah, na yi wanka sannan almajirin ya dawo. Na zuba masa ya tafi. Sai ga Tijjani ya dawo. Ya kalle ni na ci kwalliya ko'ina kamshi ke tashi. Ya kalle ni da alamun tausayi ya ce "Sannu da gida. Ya mik'o mini ledar hannunsa wacce awara ce. Na kar'ba tare da godiya. Na tashi na gabatar mana da abinci, na zuba mana a plate guda. Na ce "Bismillah". Ya girgiza kai ya ce "Na gode". Na zuba masa ido murya na rawa na ce "Ba zaka ci ba, bayan na tabbatar da yunwa a tare da kai! Da rauni sosai ya ce "Ni ni ne mai ciyar da ke, ba wai na zauna ki ciyar da mu ba". Na tashi na koma kusa da shi na ru'ko dukkan hannuwansa na sassauta murya na ce "Ba ciyar da mu zan yi ba. Ubangiji zai buda maka k'ofofin da zaka samu ka sauke nauyin rik'on iyali tunda shi ya wajaba maka. Kana kuma da niyyar yi d'in. Abin da nake so ka fahimta ko aure bai ha'da mu ba, ai jini ya ha'damu. Ko ina wani gidan idan ina da ikon kula wa da iyalinka ai zan yi, bare kuma ni ce iyalin naka, to mene ne amfanin sana'ar da ka bar ni nake yi alhalin ba zata yi maka rana ba?" Ya yi shiru bai ce komai ba, na sake sassauta murya na ce "Dan Allah ka yarje mini na yi iya abin da zan iya yi". Ya saki gauron numfashi ya ce "Idan na amince ya tabbata dai da aka ce ke ce zaki ciyar da mu Asiya. Shike nan zan rasa yancina na mai gida, shike nan zan zama mata, ke ki zama mijin". Ya fa'da murya na rawa ainun. Na durk'ushe a gabansa na ce "Wallahi ba zaka zama ba. Yadda muke hakan zamu cigaba da tafiya kai ne miji. Ni ce mata, zan dinga karban umarni daga gare ka, abin da kake so hakan za'a yi.". Ya yi shiru yana nazari bai ce komai ba. Na matse hannunsa na ce "Pls mana" cikin sigar shagwaba. Ya zuba mini idonsa da ya kad'a sosai ya ce "Asiya zuciyata ba zata nutsu ace kina siya mini abinci a gidan nan ba. Gara dai ki bari na dinga baki abin da aka yassare mini, idan ma zaki kara da abin da kike so to bazan hana ki ba, tunda ban wadatar da ke ba. Amma ni kada ki yi da ni. In sha Allah ko da bashi ne dai bazan kasa baki abin da zaki saka wa ba'kin salatinki ba. Sai idan kin raina". Na kalle shi na gane da gaske yake yi. Na yi k'asa da murya na ce "Anya kasan kalubalen da yake tare da cin bashi kuwa mussaman a waje? Kawai ka yi hakuri tunda dai Ubangiji ya baka matar da ya bata sana'ar hannu mai k'arfi. Ina fatan Ubangiji ya kawo maka aiki ko sana'ar da zaka dogara da ita." Ya girgiza kai tabbacin bai gamsu ba. Na ce "To shike nan ka dinga karban bashin a wajena." Ya gyara zama ya ce "Nawa kika kashe a hidimar tuwon?" Na ce "mu je kicin a lissafa. Ya mike muka je. Na nuna masa komai da aka siyo wanda a k'alla zamu kai wata muna ci a talau ce. "Nawa kika kashe a wannan siyayyar? Na ce dubu sha bakwai da dari shida na. Sai gawayi na dubu daya." Ya ce "To kub'ewar fa?" Na ce "A bar wannan". Ya girgiza kai. Da sauri na ce "Ta naira dari ce." Ya ce "Sha takwas da dari bakwai ke nan ko?" Na ce "Eh" ya ce "In sha Allah zan biya ki, matu'kar ina shakar numfashi." Muka koma falon muka ci abinci ina ta yi masa hira dan ya ware sosai. Wannan kayan abincin da muke da shi sai ya rage masa damuwa mai yawa. Duk da hakan kuma bai yarda ya zauna a gida ba. Kullum sai ya fita. Rannan ya yi sa'a ya samu hada saltelite har gida uku. Da k'arfinsa ya dawo ya mik'o mini dubu biyar ya ce "Ga shi, na rage miki bashin ki. Ya fita ya dawo da leda mai d'auke da soyayyen kifi. Na kar'ba tare da addu'ar Allah ya kara budi. A wannan tsukun gaba'daya a takure nake domin maimakon na samu ninkin tattalin da yake yi mini kafin mu shiga tsananin da muke ciki. Sai ya zamana ni ce nafi rawar kai a kansa domin dai na samar masa nutsuwar shine mijin. Tunda na lura yana kame wa ne dan kada na samu dama a kansa. Na dinga mamakinsa domin gaba'daya ban yi zaton zai mini kallon zan raina shi dan ya shiga halin babu ba. Ya takura kansa sosai, komai kaffa kaffa yake yi. Idan na yi kamar zan yi masa magana sai na ha'diye. Na dinga hakuri ina lallabawa ina binsa a hankali. Hidimar da ta karu a kaina sai ya zama ina ta kokarin fa'dada kasuwancina. A dalilin an kawo wa Tijjani takardar biyan ku'din gida tun kwanakin baya. Na fara tunanin yin Home service domin na samu na tara masa ku'din kafin lokacin da suka diba mana ya cika. Na kalli yatsun hannuna guda biyu gold ne. Daya na wajen kwamishina ne, dayan kuwa da sana'ar tawa na siya. Jiya na bashi daya na ce ya siyar ya biya ku'din ya ce "Ba ya so, kada na sake na siyar da kadarata akan al'amarin da ba hakkina ba ne. Idan kuma na siyar to ba zai karba ba. Da zai fita na tambaye shi zan fita, zan je bayan layinmu. Bai hana ba. Tunda na fita da hantsi ban dawo ba sai yamma lis tunda asabar ce ban cika samun k'unshi a ranar ba sai kitso. Na dawo na tarar da shi a gida. Ya gyara ko ina. A falo na tarar da shi yana kallo. Na yi masa murmushi ya mayar mini a gajarce. Ya kalle ni ya ce "Daga ina kike na ji sai k'amshin muhallibiya kike yi" Zuciyata daya na ce "Wallahi lalle na yiwa wata babbar mace da ahalinta zasu je biki Abuja. Na fito da kudina dubu sha biyar na ajiye masa na ce "Idan Allah ya yarda a satin nan zamu ha'da ku'din da zaka biya gidan". Ya zuba mini ido galala sai kuma ya