Sashe 78
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
55&56.
Ranar asabar ya dawo da rana. Sai ga shi da macaroni guda biyu hakan ma taliya, da shinkafa mudu guda. Sai sauran kaya danginsu maggi da sauransu.
Na karb'e shi da walwala kasancewar ba kasafai nake yin k'unshi asabar da lahadi ba. Sai kitso ne yafi yawa a wadannan kwanakin, saboda ana hutun karshen mako.
Doguwar riga ce ta yadin material din *Umm Nihla collection*
*07020695644*
A lokacin kuwa watanmu kusan bakwai da aure.
Da na lura sai na ga kamar ba a cikin nutsuwarsa yake ba.
Na gabatar masa da ruwa da abinci.
A hankali ya ce "sai na dawo zan ci. Dauko mayafinki mu je gida".
Gabana ya takarkare ya buga. A ki'dime na ce "Me ya faru?"
Ya numfasa ya ce"Dada ce ta.."
Kafin ya karasa na katse shi ta hanyar saka salati mai tsananin gaske. Tare da ce wa "Ta rasu?" Na fara k'walla ina cewa "Dada yau kwana ya k'are Innalillahi wa inna ilaihir rajiun". Allah ka gafarta wa Dada!
Ya bu'de baki ya ce "Yaushe na ce "Ta mutu? Kin san yanzu damina ta tsananta. Ta je zagaya wa ne sai shaddar ta rufta da ita. Allah ya sa an ji k'arar ruftawar, da ba haka ba kam, da tuni ba wannan maganar ake yi ba. An ciro ta amma baki ga ba, duk ta daddauje sosai."
Bansan ya aka yi ba dariya ta sosai ta k'wace mini.
Na dinga k'yal-k'yale wa. Ya yi sak'are yana kallo na. Can ya kasa jurewa dariyar da nake faman yi babu k'ak'kautawa.
Ya kalle ni ya ce "Ban da dai lamarinki akwai k'uruciya mene ne abin dariya a ciki? Dada fa na ce miki ta fa'da shadda. Da kuma rai ya yi halinsa me zaki yi?"
Cikin dariyata na ce "Kuka zan yi mana. Baban Kasuwa nake yiwa dariya da ya kasa gyara band'akin gyatumarsa da take nuna masa soyayya ta daban shi da ahalinsa."
Gau na ji ya hambare mini baki. Ya d'aure fuska ya ce "Idan zaki iya yiwa k'anin ubanki rashin kunya, to amma kuwa ba a gabana ba. Domin kawuna ne k'anin uwata na kuma yarda k'aninta ne. Da zuwa na yi na dauke ki, ki gaisheta ganin kusan kowa na gidan har Ubaida. Amma tunda zaki dawo da rashin kunyar ki, sai ki zauna ki yi ke ka'dai".
Ya mike ya fice. Na bishi da gudu. Murya a marairaice na ce "Zan bika Tijjani dan Allah".
Ya zuba mini ido yana yi mini kallo mai tsananin gaske. Na sani so yake na ba shi hakuri, ni kuwa ban ga me na yi ba. Ai gaskiya na fa'da. Bayan haka ai ya buge mini baki, dan haka na waske na k'i ban bada ha'kurin.
Kallon ya shige ni, na fara bubbuga k'afa. Ina ce wa "Saboda Allah me na yi maka?"
Ya jijjiga kai ya yi tafiyarsa, ba tare da ya ce uffan ba.
Ni kuwa da na hasaso Dada a masai sai na sake tuntsire wa da dariya.
Sai yamma lis ya dawo. Kai tsaye falo ya shiga. Na bi shi ina masa sannu. Na zauna. Ya ce "zubo mini abincin".
Na fita na kawo masa, ban zauna ba sai da na dauko masa ruwa a fridge.
Sai da ya gama cin abincin. Sannan na kalle shi bayan na d'aure fuska na ce "Ya jikin Dadan kuwa?"
Kai-tsaye ya ce "Da sau'ki. Amma ta samu tagarde a hannunta."
Na sake yin kalar tausayi na ce "Ayyah! Allah ya bata lafiya."
Ya amsa da "ameen" yana daddana wayarsa.
Can na nisa na ce "Tijjani wa ya yiwa Dada bik'in kashin da ta kwaso?"
Kamar ba zai yi magana ba. Sai kuma ya ce "Gwaggo ce".
Na zabura na dafa k'irjina na ce "Gwaggota?"
Kansa na k'asa ya ce "ita fa".
Kawai sai na fara kuka ina cewa "Na rantse da ina nan bazan bari ba. Duk yadda take tsangwamar ta sai kuma ta zo ta yi mata irin wannan wahala alhalin tana da y'ay'anta birjik?"
Kansa na kan wayarsa dai, ya ce "Ai da yake tana mutunta mijinta ne. Baban Marina aikin ya kama, da yake ita mace ta gari ce, sai ta fanshi mijinta".
Na zabura na ce "Wallahi ba shi ya kama ba. Ina ce ga Baban Tsakiya nan, ga kuma dan k'wai Baban kasuwa, dukkansu suna da matan auren kuma".
A fusace ya ce "To basu yi ba, ita Gwaggo ita ce ta yi domin tafi dacewa ta yi aikin".
Na harzuka na ce "Ban gane ba Tijjani. Wato ita ce kaskantacciya kake nufi ko me? Ai ba ita ce babba ba, ga Mama nan".
Ya dago ido cikin ido ya ce "Asiya na ce miki da ita aikin yafi dacewa shiyasa ta yi d'in".
Na mike na ce "Wallahi aikin bai dace da ita ba kai ma ka sani. Y'ay'an cikinta ne a hak'ku. Baba Maryo fa?" Ga mamakina sai na kasa ambato Baba ta Bulkachuwa.
Shima ya mike ya ce "jikinki na yi miki k'aik'ayi Asiya Toro. Bilhiillazi kika yi gigin zaginsu a gabana sai jikinki ya fa'da miki. Bazan dauki wananan mugun halin ba. Ke abu ba zai wuce a wajen ki ba? D'azu dukkansu sai da suka tambaye ki, amma ke kin k'wafesu a cikin zuciyarki".
Na ja tsaki na ce "Kana yi mini dukan da jikina ya fa'da mini. Ka tabbatar kai ma sai naka jikin ya fa'da maka. Domin kuwa dai ka daki aurenka tunda shine lasisinka na dukan jikin nawa".
Ya kasa ce wa komai. Amma na lura ba k'aramin b'acin rai ya shiga ba.
Ya kewaye ni ya fice. Bai dawo gidan ba. Sai wajen goma. Ni kuma tuni na sake fusata. Dan haka da ya dawo ya shigo d'akina ban ko kalle shi ba, bare nasan me yake ciki.
Ga mamakina shima bai kalle ni ba, ya koma k'arshen gado ya kwanta.
Washagari ma da asuba ya fice, k'ofar d'akin ya buga da k'arfi. Wanda na gane tashina ya yi dan na yi sallar asuba.
Ya dawo ya ajiye burodi. Ya ha'da nasa shayin ya karya ya fice.
Na yi abinci na ajiye masa na rana, amma bai dawo ba.
Da yake lahadi ne. Mutum biyu sun zo lalle, haka kitso ma mutum uku na yiwa. Kafin la'asar babu kowa.
Duk da zuciyata babu da'di a dalilin yadda na lura Tijjani ya tsananta fishin da yake yi.
Wayata na dauka na shiga manhajar WhatsApp. Sai ganin Umm Nihla ta yi posting hadaddun materials daga Malaysia. Ina matu'kar son irin yadukan. Ba don komai ba, sai dan basu da nauyi, sannan gasu da taushi, ga kuma sau'kin ku'di ainun. Abin burgewa kuma basa kodou sai da ka gaji da su ka bayar.
Wani yellow da blue suka tafi da ni. Kai tsaye na ce mata ina sonsu. Ga mamakina duk ku'din basu yi tsanani ba.
Ta tambayi a wanne garin nake? Na bata amsa da Toro. Ta ce to sai a saka miki a motar Jos kenan?. Tunda kunfi kusa akan Bauchi.
Na ce "A a akwai sister ta Aisha Lame jakadiyar oriflame. Ita zaki aikawa zasu same ni.
Ta yi mamakin cewar nasan Aisha Lame.
Na ce "To ai yar garinmu ce. Sannan muna da alaka ta wajen kakata da ta haifi Babana.
Umm Nihla ta turo emojin mamaki ta ce "Ai kuwa Aisha na da kirki, kafin na bar Nigeria a wajenta nake siyayyar kayan kwalliya da spices. Farashin kayanta mai sau'ki ne ainun".
Cikin alfahari na ce "Ai ko anan haka ahalinsu suke, mutane ne masu kirki kwarai da gaske. Nima da aurena ta bani kyautar fame wash. Yanzu kuwa na tura mata ku'din wani zan siya saboda na gane muhimmancinsa".
Daga haka ta turo mini asusunta da zan tura ku'din.
Sai mamakin yadda duniya ta samu cigaba nake yi. Ina Toro amma na sayi kaya a hannun wacce take zaune a Malaysia. Har na tura ku'din, ta tabbatar mini ta ga ni. Nima kuma ina da tabbacin zuwa gobe zan ji Aisha Lame ta karba mini. Na saki gauron numfashi.
Na fara lissafin ku'dina domin so nake na yi k'undubalar fara shafa man oriflame. Idan nafi haka sheki da d'aukar ido zan fi daukar hankalin Tijjani fiye da yanzu.
Haka na lalubo lambar Aisha Lame cikin sa'a tana online, ita da kanta ta za'ba mini Wanda yafi dacewa da farare. Itama take na tura mata ku'dinta. Na fa'da kuma za'a kawo mata material d'ina ta ha'do ta aiko aiko mini. Muka yi sallama.
Ranar asabar ya dawo da rana. Sai ga shi da macaroni guda biyu hakan ma taliya, da shinkafa mudu guda. Sai sauran kaya danginsu maggi da sauransu.
Na karb'e shi da walwala kasancewar ba kasafai nake yin k'unshi asabar da lahadi ba. Sai kitso ne yafi yawa a wadannan kwanakin, saboda ana hutun karshen mako.
Doguwar riga ce ta yadin material din *Umm Nihla collection*
*07020695644*
A lokacin kuwa watanmu kusan bakwai da aure.
Da na lura sai na ga kamar ba a cikin nutsuwarsa yake ba.
Na gabatar masa da ruwa da abinci.
A hankali ya ce "sai na dawo zan ci. Dauko mayafinki mu je gida".
Gabana ya takarkare ya buga. A ki'dime na ce "Me ya faru?"
Ya numfasa ya ce"Dada ce ta.."
Kafin ya karasa na katse shi ta hanyar saka salati mai tsananin gaske. Tare da ce wa "Ta rasu?" Na fara k'walla ina cewa "Dada yau kwana ya k'are Innalillahi wa inna ilaihir rajiun". Allah ka gafarta wa Dada!
Ya bu'de baki ya ce "Yaushe na ce "Ta mutu? Kin san yanzu damina ta tsananta. Ta je zagaya wa ne sai shaddar ta rufta da ita. Allah ya sa an ji k'arar ruftawar, da ba haka ba kam, da tuni ba wannan maganar ake yi ba. An ciro ta amma baki ga ba, duk ta daddauje sosai."
Bansan ya aka yi ba dariya ta sosai ta k'wace mini.
Na dinga k'yal-k'yale wa. Ya yi sak'are yana kallo na. Can ya kasa jurewa dariyar da nake faman yi babu k'ak'kautawa.
Ya kalle ni ya ce "Ban da dai lamarinki akwai k'uruciya mene ne abin dariya a ciki? Dada fa na ce miki ta fa'da shadda. Da kuma rai ya yi halinsa me zaki yi?"
Cikin dariyata na ce "Kuka zan yi mana. Baban Kasuwa nake yiwa dariya da ya kasa gyara band'akin gyatumarsa da take nuna masa soyayya ta daban shi da ahalinsa."
Gau na ji ya hambare mini baki. Ya d'aure fuska ya ce "Idan zaki iya yiwa k'anin ubanki rashin kunya, to amma kuwa ba a gabana ba. Domin kawuna ne k'anin uwata na kuma yarda k'aninta ne. Da zuwa na yi na dauke ki, ki gaisheta ganin kusan kowa na gidan har Ubaida. Amma tunda zaki dawo da rashin kunyar ki, sai ki zauna ki yi ke ka'dai".
Ya mike ya fice. Na bishi da gudu. Murya a marairaice na ce "Zan bika Tijjani dan Allah".
Ya zuba mini ido yana yi mini kallo mai tsananin gaske. Na sani so yake na ba shi hakuri, ni kuwa ban ga me na yi ba. Ai gaskiya na fa'da. Bayan haka ai ya buge mini baki, dan haka na waske na k'i ban bada ha'kurin.
Kallon ya shige ni, na fara bubbuga k'afa. Ina ce wa "Saboda Allah me na yi maka?"
Ya jijjiga kai ya yi tafiyarsa, ba tare da ya ce uffan ba.
Ni kuwa da na hasaso Dada a masai sai na sake tuntsire wa da dariya.
Sai yamma lis ya dawo. Kai tsaye falo ya shiga. Na bi shi ina masa sannu. Na zauna. Ya ce "zubo mini abincin".
Na fita na kawo masa, ban zauna ba sai da na dauko masa ruwa a fridge.
Sai da ya gama cin abincin. Sannan na kalle shi bayan na d'aure fuska na ce "Ya jikin Dadan kuwa?"
Kai-tsaye ya ce "Da sau'ki. Amma ta samu tagarde a hannunta."
Na sake yin kalar tausayi na ce "Ayyah! Allah ya bata lafiya."
Ya amsa da "ameen" yana daddana wayarsa.
Can na nisa na ce "Tijjani wa ya yiwa Dada bik'in kashin da ta kwaso?"
Kamar ba zai yi magana ba. Sai kuma ya ce "Gwaggo ce".
Na zabura na dafa k'irjina na ce "Gwaggota?"
Kansa na k'asa ya ce "ita fa".
Kawai sai na fara kuka ina cewa "Na rantse da ina nan bazan bari ba. Duk yadda take tsangwamar ta sai kuma ta zo ta yi mata irin wannan wahala alhalin tana da y'ay'anta birjik?"
Kansa na kan wayarsa dai, ya ce "Ai da yake tana mutunta mijinta ne. Baban Marina aikin ya kama, da yake ita mace ta gari ce, sai ta fanshi mijinta".
Na zabura na ce "Wallahi ba shi ya kama ba. Ina ce ga Baban Tsakiya nan, ga kuma dan k'wai Baban kasuwa, dukkansu suna da matan auren kuma".
A fusace ya ce "To basu yi ba, ita Gwaggo ita ce ta yi domin tafi dacewa ta yi aikin".
Na harzuka na ce "Ban gane ba Tijjani. Wato ita ce kaskantacciya kake nufi ko me? Ai ba ita ce babba ba, ga Mama nan".
Ya dago ido cikin ido ya ce "Asiya na ce miki da ita aikin yafi dacewa shiyasa ta yi d'in".
Na mike na ce "Wallahi aikin bai dace da ita ba kai ma ka sani. Y'ay'an cikinta ne a hak'ku. Baba Maryo fa?" Ga mamakina sai na kasa ambato Baba ta Bulkachuwa.
Shima ya mike ya ce "jikinki na yi miki k'aik'ayi Asiya Toro. Bilhiillazi kika yi gigin zaginsu a gabana sai jikinki ya fa'da miki. Bazan dauki wananan mugun halin ba. Ke abu ba zai wuce a wajen ki ba? D'azu dukkansu sai da suka tambaye ki, amma ke kin k'wafesu a cikin zuciyarki".
Na ja tsaki na ce "Kana yi mini dukan da jikina ya fa'da mini. Ka tabbatar kai ma sai naka jikin ya fa'da maka. Domin kuwa dai ka daki aurenka tunda shine lasisinka na dukan jikin nawa".
Ya kasa ce wa komai. Amma na lura ba k'aramin b'acin rai ya shiga ba.
Ya kewaye ni ya fice. Bai dawo gidan ba. Sai wajen goma. Ni kuma tuni na sake fusata. Dan haka da ya dawo ya shigo d'akina ban ko kalle shi ba, bare nasan me yake ciki.
Ga mamakina shima bai kalle ni ba, ya koma k'arshen gado ya kwanta.
Washagari ma da asuba ya fice, k'ofar d'akin ya buga da k'arfi. Wanda na gane tashina ya yi dan na yi sallar asuba.
Ya dawo ya ajiye burodi. Ya ha'da nasa shayin ya karya ya fice.
Na yi abinci na ajiye masa na rana, amma bai dawo ba.
Da yake lahadi ne. Mutum biyu sun zo lalle, haka kitso ma mutum uku na yiwa. Kafin la'asar babu kowa.
Duk da zuciyata babu da'di a dalilin yadda na lura Tijjani ya tsananta fishin da yake yi.
Wayata na dauka na shiga manhajar WhatsApp. Sai ganin Umm Nihla ta yi posting hadaddun materials daga Malaysia. Ina matu'kar son irin yadukan. Ba don komai ba, sai dan basu da nauyi, sannan gasu da taushi, ga kuma sau'kin ku'di ainun. Abin burgewa kuma basa kodou sai da ka gaji da su ka bayar.
Wani yellow da blue suka tafi da ni. Kai tsaye na ce mata ina sonsu. Ga mamakina duk ku'din basu yi tsanani ba.
Ta tambayi a wanne garin nake? Na bata amsa da Toro. Ta ce to sai a saka miki a motar Jos kenan?. Tunda kunfi kusa akan Bauchi.
Na ce "A a akwai sister ta Aisha Lame jakadiyar oriflame. Ita zaki aikawa zasu same ni.
Ta yi mamakin cewar nasan Aisha Lame.
Na ce "To ai yar garinmu ce. Sannan muna da alaka ta wajen kakata da ta haifi Babana.
Umm Nihla ta turo emojin mamaki ta ce "Ai kuwa Aisha na da kirki, kafin na bar Nigeria a wajenta nake siyayyar kayan kwalliya da spices. Farashin kayanta mai sau'ki ne ainun".
Cikin alfahari na ce "Ai ko anan haka ahalinsu suke, mutane ne masu kirki kwarai da gaske. Nima da aurena ta bani kyautar fame wash. Yanzu kuwa na tura mata ku'din wani zan siya saboda na gane muhimmancinsa".
Daga haka ta turo mini asusunta da zan tura ku'din.
Sai mamakin yadda duniya ta samu cigaba nake yi. Ina Toro amma na sayi kaya a hannun wacce take zaune a Malaysia. Har na tura ku'din, ta tabbatar mini ta ga ni. Nima kuma ina da tabbacin zuwa gobe zan ji Aisha Lame ta karba mini. Na saki gauron numfashi.
Na fara lissafin ku'dina domin so nake na yi k'undubalar fara shafa man oriflame. Idan nafi haka sheki da d'aukar ido zan fi daukar hankalin Tijjani fiye da yanzu.
Haka na lalubo lambar Aisha Lame cikin sa'a tana online, ita da kanta ta za'ba mini Wanda yafi dacewa da farare. Itama take na tura mata ku'dinta. Na fa'da kuma za'a kawo mata material d'ina ta ha'do ta aiko aiko mini. Muka yi sallama.