← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 109 OF 146

Sashe 109

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya jima bai iya ce wa komai ba. Da alamu kokawa yake da zuciyarsa. Domin fishin da ya ke shimfide a fuskarsa ya kai intaha.
Tsawon lokaci mun yi shiru. Yaran kuwa duk sun yi barci.
Ya munfasa ya ce "Ki yi hakuri. Na baki hakuri. Tashi mu tafi, na yafe miki".
Na sake hade rai na ce "Ba na son ka yafe mini, domin ban maka komai ba. Ban zalunce ka ba. Kai ne ka ke shirin zalunta ta. Shi yasa na saukaka maka hanyar rabuwa da ni. Kawai ka sallame ni, ba zan iya zaman zullimi da fargaba ba. Tunda ka fara samun kudi ka ke canjawa. Nan gaba bansan yadda zamu kwashe ba. Gara tun wuri na barka tun baka gama barina ba ".
Murya babu amo ya ce "me nake yi miki Asiya?"
Baka yi mini komai. Son ka ne ba na yi! Ko dole ne?"
Ya mik'e tsaye ya ce "Babu dole, to ba ni yarana".
Na rungume Hamim da yake ta barci yana sakin ajiyar zuciya. Na ce "Ba zan bayar ba, dauki Hanif shi kenan an raba."
Nan da nan ya hau rantsuwar ba zai bar shi ba. Ba zai raba su ba. Na dage tamkar har cikin zuciyata da gaske nake yi. Sosai muke yin takaddama.
Sai da na gama famfa shi. Ya sakankan ce bazan iya yarda ya tafi da su ba.
Sai kawai na ce "Dauke su ku tafi, Allah ya shiga al-amarinsu."
Nan da nan ya yi turus. Jikinsa ya yi sanyi ainun. Ya zuba mini ido tsawon lokaci, ni kuma na yi kamar ban ga ni ba.
Ya koma ya zauna a maimakon mikewar da ya yi, yana kumfar bakin sai na ba shi y'aya'nsa.
Ya sassauta murya ya ce "Na baki hak'uri fa little. Ki mini uzziri mana".
Murya na rawa na ce "Sau nawa ka ke yi mini laifi ina share wa?"
Da sauri ya ce "Da yawa. Ina kuma gode miki. Na kuma dha fad'a miki kina da alfarmomi masu yawa a waje na. Yanzu ki mini hakuri dan Allah. Bazan sake yin hakan ba."
Na hirgiza kai tabbacin ban karbi ban bakinsa ba.
Ya marairaice ya ce "Haba mana my little angel. Ki huce, kin san fishin ki kassara ni yake yi".
Sai lokacin na ji kuka ya zo mini. Na dinga yinsa bilhakki. Tsawon lokaci sannan na daina. Ya saki gauron numfashi ya ce "very sorry little. Nasan kin huce, tashi mu tafi dan Allah".
Na girgiza kai na ce "Ni kam bazan koma ba fa. Ai tunda har waya ka ke yi da ita, nasan akwai abin da zai biyo baya. Dan haka ka je na bar mata kawai."
Ya diririce ainun. Ya fara musun basa waya.
Na zuba masa ido na ce "Waye ya ce mini Nasiba ta ce da Dada za'a zo ganin gida?"
Ya ce "Ni ne".
"Me yasa ni bata fada mini a wayar ba? Me yasa kullum sai ta kira ka? Me yasa sai kai Tijjani? Tunda bata kirana, bata kiran Yaya Salisu da ragowar. Na tsani rashin kame wa".
Ya kasa magana tsawon lokaci. A sanyaye ya ce "Ba ni da bakin magana , am speechless. Abin da zan iya ce wa biyu ne. Ki mini uzziri, ki yi hakuri."
Na yi shiru. Cikin rarrashin ya ce "Wallahi duk hasashen da kuke yi ni ban tab'a d'arsa shi a raina ba. Amma na gamsu kin fini gaskiya. Idan kika yarda muka tafi yanzu kuma. Na miki alkawarin har kasa ta rufe idona babu magana mai tsayi a tsakanina da ita bare soyayya ko aure, In sha Allah ".
Na yi k'asa da kaina, ban ce komai ba, amma kuma k'ullin zuciyata ya hau warware wa".
Ganin rarrashin ya fara tasiri. Ya sake tausasa harshe ya ce "Ai ni na dauka babu abin da zan yi miki, ki yi mini yaji. Tunda baki kai hakan ba ma, na miki babban laifi, kika rufa mini asiri kika yafe mini. Amma yanzu kuma a kan zato da zargi kika tozarta ni. Me yasa zaki munana zato a kaina? Me yasa kika zabi ki janyo mini fishin Babah?"
Yana rufe baki na ce "saboda ka fahimci ban dauki alamarin da wasa ba, ka kuma gane yanzu hankali ya fara ratsa ni. Ba komai zan lamunta ba".
"A karo na ba adadi ina sake baki hakuri. Allah ya huci zuciyar ki. Dan Allah mu rufe wannan matsalar. Wallahi bazan sake yi miki hakan ba, babu ruwana da ita, ko kallon inda take bazan sake yi ba. Ko na ganta a wajen Dada idan ta gaishe ni, zan amsa ne ba tare da na kalle ta ba, bare na gane me take ciki".
Na yi shiru. Ban tanka ba. Ya ce "Haba mana Little"!
Na cuna baki na ce "To kuma wayar da kuke yi fa?"
Da hanzari ya miko mini wayar yana fad'in duba ki ga ni. Na share lambarta. Na kuma jefe lambar a black list ta yadda ita ma ba zata same ni ba".
Na yi shiru ya ce "please mana Little ki ce kin huce, ki ce komai ya wuce".
Na dauke kai na ce "To kuma iyakar da ka nuna mini fa? Da ka ce gidan ka ne ba nawa ba?"
Da rawar murya ya ce "Kinsan An nadamu ala ma fata? To hakan maganar ta ke. To ni me ma zan yi da gidan da babu ke a cikinsa? Idan wannan maganar ne ta sake b'ata miki rai to ki huce. Na baki gidan ma gabadaya. Ki yi yadda ki ke so a cikinsa. Shi kenan?"
Na ce shi kenan, amma bazan koma yau ba".
Da hanzari ya ce "A a kada mu yi hakan, yanzu zamu tafi idan ba so kike hankalina yafi hakan tashi ba."
A hankali na ce "To kawai sai Babah ta ga zamu tafi? Ka bari idan na fada mata jibi sai ka dawo mu tafi".
Da azama ya ce "Wallahi bazan iya ba, kada ki zalunce ni, kin sani bazan iya ba. Tunda mun shirya ina ruwanta da mu?"
Ya mik'e yana ce wa "bari na je na fada mata zamu tafi".
Na bi bayan sa da kallo. Ina jin fishin da na yi da shi yana warware wa.
Na zuba wa yaran ido. Ina rasa ga ne wa nafi so a cikinsu. Dukkansu Abu guda nake ji a kansu. Amma na fi jin tausayin Hamim haka siddan duk da shine fitinanne kuma marar hak'uri.
A fili na furta "Allah ka rayamu tare da yaranmu, ka tsare mana su, ka yiwa rayuwarsu albarka".
Ina kallon Hanif da yake barcinsa akan gado illah kansa da yake jikina. Ina ayyana mutane masu karamci da sadaukarwa tun suna kananu ake fahimtarsu. Yana wahalar gaske ya ture d'an-uwansa a jikina. Ko abu ya dauka da Hamim ya fara kuka zai ba shi. Haka nan baya damuwa idan na goyi Hamim shi na rik'e hannunsa.
A raina sai nake ganin shine yafi dace wa ya amsa sunan Baban Marina. Ko da yake bansan ko Baban Bulkachuwan shi ma haka yake mai hak'urin gaske ne.
Na shafa kansa ina ce wa "Allah yasa ka zarce da hak'uri da yakanar ka. Allah ya saukaka muku rayuwarku gabadaya".
Na yi shiru ina jin wani irin abu na tsirga mini da bansan ko mene ne ba.
A hakan Babah ta shigo, Tijjani na biye da ita a baya.
Ta kalle ni ta ce "Wai har kin hakura kin ce zaki bi shi Yabi?"
Yadda ta yi maganar sai na kasa amsawa.
Nan da nan ya ce "Ta hakura mana Babah. Dan Allah kada ki sauya mata shawara. Na bata hak'uri, ke ma ina sake baki hak'uri."
Ta ce "Idan ta ce zata koma ai shike nan. Amma idan ta ni ne ko zata koma sai na kira maza sun taya ni kafa maka hujja".
Ya marairaice ya ce "Harshe da hakori ma ana samun sab'ani. Mun fahimci juna yanzu. Na yi alkawarin bazan kuma yi mata hakan ba. Mu rufe wannan matsalar a tsakaninmu dan Allah".
Ta kalle ni ta ce "Zaki koma, ko sai mun zauna da iyayensa na nan na fada musu BAK'AR TA'ADAR da yake neman tsiro da ita, kada nan gaba su ce na kashe masa aure".
Na kasa magana. Shi kuma fadi yake "Babah mun fa shirya ta fahimce ni, na bata hak'uri."
Ta ce "Kasan Allah sai na ji da kunnena sannan zan bari ku tafi. Ai kai yanzu maganar ka ba abin dubawa ce ba".
Ya rasa inda zai sa ransa. A kidime ya ce "Asiya taimake ni ki fada mata, kin huce, daure ki ce komai ya wuce. Kalli yadda yaran nan suke barcin nutsuwa a jikin ki. Ko baki hakura dan ni ba, huce saboda su".
Dakin ya dauki shiru. Kallon Tijjani kawai za'a yi a gane yana cikin zullimi sosai.
Ta sassauta ta ce "me kika ce, zaki koma, ko kuwa?"
Na yi k'asa da kaina na ce "Tunda ya gane kurensa, ya janye kalamansa, ya kuma bada hakuri, to ba sai an tara masa jama'a ba. Ai mun ba shi assignment ".
Ya yi maza ya ce "Wallahi exam ma kuka ba ni."

*Anti Rabi how far?*

✍️
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633
Chapter 109 · 0% Book details