← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 124 OF 146

Sashe 124

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da daddare muna kwance a dakinsa yara suna dakinsu da yake cikin falona sun yi barci.
Dukkanmu kowa tunanin zuci yake yi.
Ba abin da nake so irin na fice na bar gidan Tijjani. Tufka da warwara kawai nake yi. Maganganun Gwaggo sun yi matukar karya lagona. Domin a da na kudire wa raina daga ranar da ya shiga dakin Nasiba ya kwana da ita. Tabbas washegari zan bar shi, bari na har abada tunda nasan Baban Marina zai bani masauki tare da kyakkwar mu'amala a tsakaninmu.
Amma yanzu Gwaggo ta mini tilas din cigaba da zama ta hanyar rarrashi da dabara.
Na nisa na saki ajiyar zuciya.
Daidai lokacin ya ce "Sannu Asiya!
Ban kula shi ba, ya ruko ni, na yi bakam tamkar mai barci.
A sanyaye ya ce "Zullimi ne yake kama ni from no where! Samar mini da nutsuwa pls. Dan Allah bude baki ki fad'a mini wata kalma da zan samu sassauci a zuciyata. Ina daf da tarwatse wa Asiya".
Na ja tsaki mai tsananin gaske tare da ce wa "Tsuntsun da ya ja ruwa".
Ya sake rik'e ni ainun. Ya kasa ce wa kanzil. Ajiyar zuciya kawai yake yi. Murya babu amo ya ce "Idan na mutu Asiya dan Allah kada laifina ya shafi twins. Ni kaina bana gane kaina a wasu lokuta, kin ga da hantsi ko yamma sai na ji tamkar ana hura mini huta a kirjina.
Da zarar wani aka jima kuma sai na ji duk yadda aka azalzale ni na je Toro sai kuma na ji ke nake son na dawo ma ga ni. Ko dai na haukace ne Asiya?"
Da k'arfi sosai na ce "Tunda har kana banbance wasu alamuran da hamkalinka sarai. Kuma ina nan akan bakana, ba zan zauna da kai ba Bulkachuwa. Ana kawo maka Nasiba ka tabbatar na hak'ura da kai".
Jikinsa ya dauki rawa. Ya ce "Bazan iya rabuwa da ke ba. Haka kuma idan ban aure ta ba, bazan tab'a samun nutsuwa ba. Ki taimake ni mana".
Na ce "zaka ga taimako ganin idon ka. Na rantse maka duk wani sababin duniya ka shiryawa ganinsa. Hala dai ka manta Yabin marina ne Tijjani?".
Ga mamakina bai iya taso mini da masifar sa ba. Gabadaya jikinsa ya sake sosai.
Washagari na tashi da bala'i ko kallon inda yake ban yi ba. Na yarda da zancen Gwoggo. Amma bazan iya samar masa da nutsuwar da ake so ba.
Ya je can ya k'arata da dibar albarkar sa, shi da masu goya masa baya.
A wannan safiyar ya mini magana yafi sau goma ban kula shi ba. Na ki yin girki. Shi kuma ba shi da kuzarin da zai yi. Gabadaya ya koma Tijjanin farkon aurenmu. Ba na yanzu da yake masife ni a dalilin ina adawa da k'arin aurensa.
Ya kai ya kawo a tsakanin dakinsa da nawa. Ya kasa fita bare na samu na d'an sarara. Tunda gabadaya haushinnsa nake ji mai kama da tsana.
Sallah kawai yake fita. Da k'yar ya lallaba ya tafi dauko su Hanif.
Da gudu suka shigo. Na yi maza na hadiye damuwar da nake ciki na shiga yi musu oyoyo tare da murmushin yak'e.
Na dora musu indomie, bayan na juye musu ruwan wanka. Na kammala yi musu wanka, suka yi sallah.
Sannan na juyo mana indomie muka fara ci da su.
Hanif ya ce "Baban 2 sauko mu ci".
Hamim ya ce "Ba shi da lafiya ai marar lafiya ba ya cin abinci"
Takaici ya shake Bulkachuwa.
Ya daidai ta zamansa ya ce "Hamim baka tausayina ko kad'an?. Zaka ga tsiya, daga yau Hanif zan dinga siyo wa abina tunda kai uwarka kake so kawai".
Da yake mai kwadayi ne sai ya marairaice ya ce "Na daina Baban 2 sauko mu ci to."
Bai sauko ba, ya koma ya zauna. Ba tare da ya sake ce wa komai ba.
Muka kammala da kansa ya saka musu yunifom din islmamiya ya rakasu waje ya dawo.
Ya zauna daf da ni ya ce "Asiya Tsakanin ki da mai rumfa me ya hana ki daukar ciki?"
Na hassalo na ce "Saboda na gama haihuwar da kai, sai da wani".
Ai kuwa ina rufe baki ya cakume ni yana kokarin murde mini baki.
Na dinga zille wa, ina ture shi. Maimakon ya bar ni tunda ya ga kuka nake yi sosai, duk da bai mini komai ba, kuka nake na takaicinsa da na aurensa.
Amma bawan Allah bai yarda ya kyale ni ba. Ya sure ni ya yi dakina da ni. Sai da ya yi abin da yake so. Ya tara mini gajiya ya ce "Ya kika ji? Kin hana ni abinci, amma kin dafa muku ke da y'aya'n ki, kun ci. Sai kuma na zarta ki k'arfi da kuzari."
Na ja tsaki na juya masa baya, bayan na ja mayafi na lullube jikina.
Da daddare ya fita ya siyo tsire mai yawa. Ya dafa shayi ya kawo falo.
Ya juye naman a plate ya ce mu sauko mu ci.
Shi da yaran suka ci. Ni kuwa ko sha'awar ci ban ji ba, duk da yadda k'amshin ya cika wajen gabad'aya.
Washagari har wajen tara yana gida kamar ba zai fita ba. Kamar zan masa magana a dalilin yadda ya bani tausayi, amma da zarar na tuna ba janye wa zai yi ya fasa auren Nasiba ba, sai na ji tsanarsa na sake darsuwa mini.
Yana zaune sai waya ake yi masa babu kakkautawa. Kan dole ya yi shirin fita. Murya babu amo ya ce "Zan fita Asiya sai na dawo".
Ko motsi ban yi ba bare na masa shi. Ya sa kai ya fice. Sai kuma ya dawo, ya gama kame kame ya fita.
Mintina kusan talatin ya sake dawo wa.
Ya tarar da ni a zaune. Ya ce "Gabad'aya jikina bana jin dad'i. Ga shi fitar ta zame mini dole. Kano zan je na kai kaya. Amma yau zan dawo komin dare in sha Allah ".
Na dauke kai na kasa ce wa A dawo lafiya.
Ya fita. Na ja tsaki tare da ce wa "Ka gama shige da ficen ka ba kula ka zan yi ba.
Azahar ta tayar da ni. Na yi sallah na d'ora abinci saboda yara.
A daddafw na yi shara na gyara dakin.
Na fito wanka su Hamim suka dawo.
Da yake alhamis ne babu islamiya.
Dan haka sai suka debe mini kewa, ban fada nazarin yadda zamana da Nasiba zai kasance ba. Tunda a duniya bani da matsalar da ta wuce hakan.
Ban ankara da rashin dawowarsa ba sai wajen goma na dare. Yana wahalar gaske ya yi dare. Idan kuwa hakan ta kasance sai ya bugo mini waya, ko da ni ban masa wayar ba.
Na fara tsorata da shadaya ta gota. Zuciyata na bugawa na d'auki waya na k'ira shi.
Abin mamaki wayar ta ki shiga, na dage da kira babu kakkautawa.
A karshe a ka ce a kashe take gabad'aya.
Na shiga zullimi sosai. Mussaman da ya tabbatar mini zai dawo komin dare.
Na rasa yadda zan yi. Na Kalli yara na barci. Hamim ya dora kafarsa jikin Hanif.
Hawaye ya tsinke mini domin yadda nake jin jiki da zuciyata suna bari, nasan akwai abin da zai biyo baya marar dad'i.
Duk yadda na so na tashi na yi sallah kasawa na yi. Daren ya mini tsayi ainun. Domin tunda muka dawo Bauchi bai tab'a tafiyar kwana ya barmu ba.
Na dinga kuka ina fad'in "Allah ka taimake ni ka dawo da shi lafiya."
Da asuba na cigaba da kiran wayarsa nan ma shiru.
Ina idar da sallaj na bugawa kaninsa Aliyu waya na sanar masa Tijjani bai dawo ba, kuma wayarsa a kashe. Ya yi yunkurin kwantar mini da hankali. Na katse wayata na kira Yaya Salisu na shaida masa.
Har karfe daya na rana babu labarin sa. Hankali dangi ya fara tashi. Da la'asar sai ga Babah ta Bulkachuwa tare da Aliyu.
Kuka kawai muke yi ni da ita. Aka rasa mai bawa wani hak'uri a tsakaninmu.
Yayin da Yaya Salisu da Yaya Aliyu suka nufi Kano tun hantsi.
Tashin hankalinmu ya sake tsananta da la'asar ta yi babu wani tartibin labari akan Tijjani ko motarsa.
Hatta Toro hankakula ya tashi ainun domin tabbas abu marar dad'i ya same shi, mutuwa ko mummunar hadarin da aka kasa gane shi.
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai muke ta ambata ni da Babah.
Babu abin da yake sake tayar mini da hankali irin idan na kalli twins.. gabadaya sun kasa sukuni. Duk fitinar Hamim ya zauna a gefe ya nutsu tamkar marar lafiya. Maganganunsa da ya dinga yi mini a baya akan mutuwa suka dinga dawo mini. Na fara kuka sosai ina ce wa "Sai da na sakankance ba mutuwa zaka yi ba shine zaka tafi ka bar omu, me yasa zaka tafi yanzu alhalin zukatanmu cike suke da gilli da bacin rai mai tsananin gaske?.".
Babah ta kasa ce wa komai illa hawaye da ita ma yake k'waranya daga fuskarta.
Ina cikin haka sai ga Yaya Ummi da Mama. Baban Marina ya turo su, su zauna da ni. A dalilin bai san Babah tana tare da ni ba. Ganinsu ya sake rikitini ina sake gasgata abu marar dad'i ya same ni. Ina kuka ina fad'in "Ni Yabi yaushe zan tsallake damuwowi ne a rayuwa ta?"
Gabadaya na rikice, sai tausa ta suke yi, duk da Yaya Ummi ma kukan take yi sosai.
Sai dare Aliyu ya k'ira Babah. Murya babu sukuni. Ya ce "Al'amarin dai sai hak'uri."
Abin da na ji ke nan na yanke jiki na fad'i ban sake gane komai ba.

*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
Chapter 124 · 0% Book details