Sashe 120
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ban kalle shi bare na ba shi amsa. Maimakon shi ma ya sawa bakinsa linzami tamkar yadda na yi sai ya zarce da ce wa "Baban kasuwa ne kawai mai mace daya, shi ma nasan a dole yake zaune bai k'ara ba. Shi Baban Marina din da yake tunzuri irin haka ai uku ne da shi, shine ni zai nemi hana ni jin yadda a ke ji?"
Na kalle shi da fishi sosai na ce "Ya isa haka! Ina rantse maka da Allah Tijjani zamu kwashi y'an kallo. Komai kake ji da shi na wulakanci ya tsaya iya kaina. Amma ka yi kad'an ka tabo alfarmar ubana. Ya wuce hakan Wallahi".
Bansan ya aka yi ba jikinsa ya mutu. Ya kasa ce wa uffan.
Na ja tsaki mai tsananin gaske na tashi na bar masa wajen.
Muka k'ulla gaba sosai. Domin ya kullaci zuwan Baban Marina da kalamansa, dazu har da shaguben laifinsa ya shafi twins a wajen Baban Marina bai kula su ba. Yana wankin kayansu yana mini azanci. Ya kuma zabe iya nasu ya bar mini nawa. Ko kallo bai ishe ni ba. Domin sosai nake jin zafinsa.
Ranar da aka tabbatar mini su Baban Tsakiya sun kai masa kudin aure gidan iyayen Nasiba kwana na yi ina kuka. Sassafe na yi Bulkachuwa. Ina zuwa na sake tarar da wani abin alajabin. Fad'a kawai Babah take mini wanda babu rarrashi ko nuna soyayya a ciki. Cikin sanyi ainun ta ce "Haba kina da k'warzaba Yabi. A kanki aka fara yin kishiya ne? Tun yaushe kike jidali?. To ni bazan iya hana shi aure ba. Ni nan da kike ganina kan kishiya aka kawo ni. Mahaifiyar ki ma kan kishiyar ta zo, sannan bayan ita ma ya sake yin wata. Ina dalilin wannan kai komon da kike yi na azina?"
Na kafe ta da ido na ce "Har cikin zuciyata nasan ba haka siddan kika mini hakan ba. Allah Ubangiji ya kawo karshen wannanan al'amarin." Na fada ina kuka sosai. Ina kula da yadda kukan nawa ya raunanta amma ta kasa ce wa komai.
Haka na dawo Bauchi da kaina. Tare da hak'urin dole. Amma ni kad'ai nasan me nake ji a zuciyata.
*Toro*
Tunda a kai kudin auren Tijjani gabadaya lafiya ta yiwa Baban Marina karanci. Ba komai ke nukurkisar sa ba illah yadda babu wani mutum d'aya a gidan Marina da ya fito ya nuna rashin dacewar al'amarin. Ya kasa samun Hauwa uwar Tijjani a waya. Kowa murna yake yi da auren.
Tun jinyar na sand'arsa a hankali har ta kai ya kwanta. Ba'a samu wanda ya fito ya soki al'amarin a cikin yan'uwansa ba, balle a farga da yadda bakinciki ke sakatarsa. A wannan karon dukkan juriyarsa ta k'are. Ya yi amannar yan'uwansa basa son sa da gaske. Ban da haka mene ne za'a fifita Nasiba akan Yabi da take yar gidan?
A cikin wannan yanayin Babah ta Bulkachuwa ta zo garin.
A dakinsa ta tarar da shi. Kallon sa kawai ta yi hawaye ya tsinke mata. Domin a cikin sati kacal tsufa ya keto masa na ban mamaki. Tausayi ya kamata, ta sani bakin cikin yadda al'amarin ya juye ne yake neman kassara shi. Mussaman yadda kowa ya koma bangaren uwar Nasiba da ta take komai ta runtse idonta. Babban abin da yake damunta bata san me yasa take jin tamkar idan ba a yi auren Nasiba da Tijjani ba zata dauma a cikin kaico. So take ta bude baki ta barranta kanta daga lamarin amma ta kasa.
Murya na rawa ta ce "Sannu Yaya!
Ya kalle ta da idanuwansa da suka kad'a. Murya babu amo ya ce "Hauwa Tijjani zai yi aure nan da kwanaki kad'an. Bana inkarin k'arin aurensa domin kuwa yana da sukunin da zai ajiye mace hudu ma. Amma ki sani Wallahi ba zai had'a mini y'aya'na guda biyu kishi ba. Idan har dukkan ku babu mai fitowa ya yi magana to ni na yi. Bazan yarda na mutu na bar Yabi a cikin wannan taskun ba. Domin na san kafatalin ahalin gidannan ba zata samu wanda zai mata adalci irin na uba ba. Ke nake da garantin zaki tsaya mata. To ga shi ke ma an juya miki tunani. Shin kina ganin ya dace na zuba ido ana jifanmu ni da ahalina da sihiri bayan na jure dukkan k'iyayya da warakin da na shafe lokaci mai yawa ana mini ni da zugata?"
Kamar a tsaorace ta ce "A a Yaya! Ni kaina ina tambayar kaina me yasa na kasa yin magana? Me yasa nake jin tsoron yin magana? Me yasa tashi d'aya na ji soyayyar al'amarin ta shige ni fiye da komai a yanzu?"
Ya jijjiga kai ya ce "Na barwa Allah ya kawo mini dauki. Abin da nake so da ke yanzu. Yau din nan ki shiga mota ki dauko mini Yabi. Saboda ke na bawa Tijjani ita. Kin sani a wanccan lokacin ba shi da rigar da za'a bashi aure, asalima hana shi ake yi gida da dawa. Ke na bawa amanarta, ke na damkawa ita a hannunki. A yau kuma ina son ki dawo mini da ita salin alin yadda na baki ita cikin girma da arziki".
Ta fara kuka mai tsananin gaske. Tana fad'in "kada ka yi hakan Yaya. Daure mu bi al'amarin a nutse. Tunda har ka gano sihiri ne, ka taimake ni mu lalubo bakin zaren mana!"
Ya yi shiru yana sauraren kukanta. Ya numfasa ya ce "Bayan sihiri ai kin san yadda ni da y'aya'na muka zama saniyar ware. Lokacin da Jabir yake hakilon zai had'a Yabi da Maijidda gabad'aya kowa tofin Allah tsine aka yiwa lamarin. Bansan adadin kashedin da Dada ta yi mini akan na jawa Yabi kunne ba. A gabana Badamasi yake fad'in Jabiru ba zai auri Yabi ba. Iliya kuwa shi ma ya sha fad'in "Daga ranar da aka ce Jabiru zai auri Yabi to a lokacin zai sako masa Maijidda. Amma kuma an zuba ido tare da bada goyon baya a kwace wa Yabi mijin da ba'a yarda aka bata shi ba, sai da aka tabbatar ba shi da mamora. Yanzu kuma da ya samu madogara sai aka ga yafi k'arfin ta. Tunda abin hakane sai ta fito ta basu waje. Adalcin Ubangiji ya ishi kowa.
Kuka kawai take yi tana jin yadda tsoro da sanyi yake d'ada girma a zuciyarta.
Murya babu amo ta ce "Dan Allah Yaya ka janye umarnin na dauko maka ita. Kasan dai yadda Ubangiji ya mutunta sha'anin aure. Ka yi hak'uri mana har muga karshen wannan waki'ar".
Ya yi shiru kamar ya yarda sai kawai ta ji ya ce "Wallahi ba zai had'a su ba. P bi mini kadina. Bare ina fatan na yi tsawon rai dan kawai ran Yabi kad'ai ".
Kukanta ya karu. Tana yi tana ce wa "Allah ka warware wannan dambarwar. Ubangiji ka taimaki zumuncin ka fahimtar da ni abin da yake boye. Allah na tuba astagafirillah. Ta mike ta tafi babu waiwaye. Ya bi ta da ido yana gasgata surkullen dabaibaye zuciyarta aka yi.
Hawaye mai ciwo ya dinga gangarowa ta kwarmin idonsa.
Gwaggo ta shiga ta tarar da shi a hakan. Ta zauna ta ce "Alhaji ba zaka karanta wa kanka damuwa ba? Ina jin tsoron kada ka hadu da ciwon nan mai shanye barin jiki".
Murya a karye ya ce "Ban da darajar sallah da salati Asama'u ai da tuni zuciyata ta buga ma gabad'aya. A ce haka zan kare cikin bak'inciki da tashin hankalin cikin yan'uwana? Yanzu na rasa mutum daya da zai yuwa Yabi kara da alkunya duk cikin dangina? Tausayin yarana gabad'aya ne yake neman kassara ni. Idan na mutu haka zasu yi ta tashi fad'i babu mai tsaya musu, yanzu shi ke nan bani da wanda zai kula mini da alamarinsu ko wanda zan damk'asu a hannunsa?"
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
Idonta ya ciko sosai amma ta sanya jarumta ta hadiye. Ta ce "To Alhaji ban da abin ka, duk wanda ka damkasu gare shi ai shima zai mace wata rana. Kawai yi dabarar damkasu a hannun Ubangiji domin shi ne rayayye wanzazze. Ina kuma son ka yiwa Hauwa adalci. Al'amarin ne yafi k'arfinta. Shi kansa Tijjani ai ba'a hayyacinsa yake ba. Idan muka daure muka yi hakuri. Muka taushi Yabi ta yi hak'uri komai zai wuce. Duk abin da aka gina shi da son zuciya baya k'arko".
Ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa. Ya ce "Kina nufin na sake tirsasa Yabi ta zauna da Tijjani ko da bata son hakan?"
Da sauri ta ce "Eh. Domin babu abin da hak'uri ba zai bayar ba idan aka nutsu."
Ido cikin ido ya ce "To a yau kam bazan d'auki shawarar ki ba. Sassauci d'aya zan yi, idan ta ga zata zauna shi ke nan sai na bita da addu'a. Idan kuwa ta ga ba zata zauna ba, to kuwa ko menene zai faru sai dai ya faru amma zan fanshi y'ata."
Ta kasa ce wa komai domin ta san da dukkan zuciyarsa yake magana.
Na kalle shi da fishi sosai na ce "Ya isa haka! Ina rantse maka da Allah Tijjani zamu kwashi y'an kallo. Komai kake ji da shi na wulakanci ya tsaya iya kaina. Amma ka yi kad'an ka tabo alfarmar ubana. Ya wuce hakan Wallahi".
Bansan ya aka yi ba jikinsa ya mutu. Ya kasa ce wa uffan.
Na ja tsaki mai tsananin gaske na tashi na bar masa wajen.
Muka k'ulla gaba sosai. Domin ya kullaci zuwan Baban Marina da kalamansa, dazu har da shaguben laifinsa ya shafi twins a wajen Baban Marina bai kula su ba. Yana wankin kayansu yana mini azanci. Ya kuma zabe iya nasu ya bar mini nawa. Ko kallo bai ishe ni ba. Domin sosai nake jin zafinsa.
Ranar da aka tabbatar mini su Baban Tsakiya sun kai masa kudin aure gidan iyayen Nasiba kwana na yi ina kuka. Sassafe na yi Bulkachuwa. Ina zuwa na sake tarar da wani abin alajabin. Fad'a kawai Babah take mini wanda babu rarrashi ko nuna soyayya a ciki. Cikin sanyi ainun ta ce "Haba kina da k'warzaba Yabi. A kanki aka fara yin kishiya ne? Tun yaushe kike jidali?. To ni bazan iya hana shi aure ba. Ni nan da kike ganina kan kishiya aka kawo ni. Mahaifiyar ki ma kan kishiyar ta zo, sannan bayan ita ma ya sake yin wata. Ina dalilin wannan kai komon da kike yi na azina?"
Na kafe ta da ido na ce "Har cikin zuciyata nasan ba haka siddan kika mini hakan ba. Allah Ubangiji ya kawo karshen wannanan al'amarin." Na fada ina kuka sosai. Ina kula da yadda kukan nawa ya raunanta amma ta kasa ce wa komai.
Haka na dawo Bauchi da kaina. Tare da hak'urin dole. Amma ni kad'ai nasan me nake ji a zuciyata.
*Toro*
Tunda a kai kudin auren Tijjani gabadaya lafiya ta yiwa Baban Marina karanci. Ba komai ke nukurkisar sa ba illah yadda babu wani mutum d'aya a gidan Marina da ya fito ya nuna rashin dacewar al'amarin. Ya kasa samun Hauwa uwar Tijjani a waya. Kowa murna yake yi da auren.
Tun jinyar na sand'arsa a hankali har ta kai ya kwanta. Ba'a samu wanda ya fito ya soki al'amarin a cikin yan'uwansa ba, balle a farga da yadda bakinciki ke sakatarsa. A wannan karon dukkan juriyarsa ta k'are. Ya yi amannar yan'uwansa basa son sa da gaske. Ban da haka mene ne za'a fifita Nasiba akan Yabi da take yar gidan?
A cikin wannan yanayin Babah ta Bulkachuwa ta zo garin.
A dakinsa ta tarar da shi. Kallon sa kawai ta yi hawaye ya tsinke mata. Domin a cikin sati kacal tsufa ya keto masa na ban mamaki. Tausayi ya kamata, ta sani bakin cikin yadda al'amarin ya juye ne yake neman kassara shi. Mussaman yadda kowa ya koma bangaren uwar Nasiba da ta take komai ta runtse idonta. Babban abin da yake damunta bata san me yasa take jin tamkar idan ba a yi auren Nasiba da Tijjani ba zata dauma a cikin kaico. So take ta bude baki ta barranta kanta daga lamarin amma ta kasa.
Murya na rawa ta ce "Sannu Yaya!
Ya kalle ta da idanuwansa da suka kad'a. Murya babu amo ya ce "Hauwa Tijjani zai yi aure nan da kwanaki kad'an. Bana inkarin k'arin aurensa domin kuwa yana da sukunin da zai ajiye mace hudu ma. Amma ki sani Wallahi ba zai had'a mini y'aya'na guda biyu kishi ba. Idan har dukkan ku babu mai fitowa ya yi magana to ni na yi. Bazan yarda na mutu na bar Yabi a cikin wannan taskun ba. Domin na san kafatalin ahalin gidannan ba zata samu wanda zai mata adalci irin na uba ba. Ke nake da garantin zaki tsaya mata. To ga shi ke ma an juya miki tunani. Shin kina ganin ya dace na zuba ido ana jifanmu ni da ahalina da sihiri bayan na jure dukkan k'iyayya da warakin da na shafe lokaci mai yawa ana mini ni da zugata?"
Kamar a tsaorace ta ce "A a Yaya! Ni kaina ina tambayar kaina me yasa na kasa yin magana? Me yasa nake jin tsoron yin magana? Me yasa tashi d'aya na ji soyayyar al'amarin ta shige ni fiye da komai a yanzu?"
Ya jijjiga kai ya ce "Na barwa Allah ya kawo mini dauki. Abin da nake so da ke yanzu. Yau din nan ki shiga mota ki dauko mini Yabi. Saboda ke na bawa Tijjani ita. Kin sani a wanccan lokacin ba shi da rigar da za'a bashi aure, asalima hana shi ake yi gida da dawa. Ke na bawa amanarta, ke na damkawa ita a hannunki. A yau kuma ina son ki dawo mini da ita salin alin yadda na baki ita cikin girma da arziki".
Ta fara kuka mai tsananin gaske. Tana fad'in "kada ka yi hakan Yaya. Daure mu bi al'amarin a nutse. Tunda har ka gano sihiri ne, ka taimake ni mu lalubo bakin zaren mana!"
Ya yi shiru yana sauraren kukanta. Ya numfasa ya ce "Bayan sihiri ai kin san yadda ni da y'aya'na muka zama saniyar ware. Lokacin da Jabir yake hakilon zai had'a Yabi da Maijidda gabad'aya kowa tofin Allah tsine aka yiwa lamarin. Bansan adadin kashedin da Dada ta yi mini akan na jawa Yabi kunne ba. A gabana Badamasi yake fad'in Jabiru ba zai auri Yabi ba. Iliya kuwa shi ma ya sha fad'in "Daga ranar da aka ce Jabiru zai auri Yabi to a lokacin zai sako masa Maijidda. Amma kuma an zuba ido tare da bada goyon baya a kwace wa Yabi mijin da ba'a yarda aka bata shi ba, sai da aka tabbatar ba shi da mamora. Yanzu kuma da ya samu madogara sai aka ga yafi k'arfin ta. Tunda abin hakane sai ta fito ta basu waje. Adalcin Ubangiji ya ishi kowa.
Kuka kawai take yi tana jin yadda tsoro da sanyi yake d'ada girma a zuciyarta.
Murya babu amo ta ce "Dan Allah Yaya ka janye umarnin na dauko maka ita. Kasan dai yadda Ubangiji ya mutunta sha'anin aure. Ka yi hak'uri mana har muga karshen wannan waki'ar".
Ya yi shiru kamar ya yarda sai kawai ta ji ya ce "Wallahi ba zai had'a su ba. P bi mini kadina. Bare ina fatan na yi tsawon rai dan kawai ran Yabi kad'ai ".
Kukanta ya karu. Tana yi tana ce wa "Allah ka warware wannan dambarwar. Ubangiji ka taimaki zumuncin ka fahimtar da ni abin da yake boye. Allah na tuba astagafirillah. Ta mike ta tafi babu waiwaye. Ya bi ta da ido yana gasgata surkullen dabaibaye zuciyarta aka yi.
Hawaye mai ciwo ya dinga gangarowa ta kwarmin idonsa.
Gwaggo ta shiga ta tarar da shi a hakan. Ta zauna ta ce "Alhaji ba zaka karanta wa kanka damuwa ba? Ina jin tsoron kada ka hadu da ciwon nan mai shanye barin jiki".
Murya a karye ya ce "Ban da darajar sallah da salati Asama'u ai da tuni zuciyata ta buga ma gabad'aya. A ce haka zan kare cikin bak'inciki da tashin hankalin cikin yan'uwana? Yanzu na rasa mutum daya da zai yuwa Yabi kara da alkunya duk cikin dangina? Tausayin yarana gabad'aya ne yake neman kassara ni. Idan na mutu haka zasu yi ta tashi fad'i babu mai tsaya musu, yanzu shi ke nan bani da wanda zai kula mini da alamarinsu ko wanda zan damk'asu a hannunsa?"
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
Idonta ya ciko sosai amma ta sanya jarumta ta hadiye. Ta ce "To Alhaji ban da abin ka, duk wanda ka damkasu gare shi ai shima zai mace wata rana. Kawai yi dabarar damkasu a hannun Ubangiji domin shi ne rayayye wanzazze. Ina kuma son ka yiwa Hauwa adalci. Al'amarin ne yafi k'arfinta. Shi kansa Tijjani ai ba'a hayyacinsa yake ba. Idan muka daure muka yi hakuri. Muka taushi Yabi ta yi hak'uri komai zai wuce. Duk abin da aka gina shi da son zuciya baya k'arko".
Ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa. Ya ce "Kina nufin na sake tirsasa Yabi ta zauna da Tijjani ko da bata son hakan?"
Da sauri ta ce "Eh. Domin babu abin da hak'uri ba zai bayar ba idan aka nutsu."
Ido cikin ido ya ce "To a yau kam bazan d'auki shawarar ki ba. Sassauci d'aya zan yi, idan ta ga zata zauna shi ke nan sai na bita da addu'a. Idan kuwa ta ga ba zata zauna ba, to kuwa ko menene zai faru sai dai ya faru amma zan fanshi y'ata."
Ta kasa ce wa komai domin ta san da dukkan zuciyarsa yake magana.