Sashe 129
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Kotun ta cika makil domin sharioi za'a yi masu daukar hankali.
A kuma wannan ranar za'a yanke wa Tijjani hukunci.
Da wuri muka iso. Da ni, da Yaya Salisu da Baban Marina da kuma Yaya Salamatu.
Sai ko Yaya Ammar da yake Bauchi.
Karfe shadaya aka fara shari'arsa. Babu wata hujja da zata wanke Tijjani. Domin lambar da ya ce an k'ira shi da ita kwata kwata bata shiga. Sannan an tambaye shi me yasa da aka ba shi kaya bai bude ya duba ba? Tunda ya dauki delivery a matsayin sana'a. Me yasa ba ya nazarin kauce wa dukkan wata matsala da zata taso. Wajibi ne idan zaka karbi sako, ka duba ka ga mene ne a ciki tunda idan aka kama ka ai kai ne a ciki.
Sannan me yasa bai binciki ainihin inda mutumin yake ba?"
Lauyan da k'aninsa Aliyu ya daukar masa, ya kasa inkarin hujjojin lauyoyin gwamnati tunda tabbas Tijjani bai yi bincike ba ya karbi kaya. Bai kuma bude ya duba ba. An ba shi abu a d'aure cikin buhu kawai ya danna a mota. Sannan bai san mutum ba. Kawai ance idan ya je Kano za'a karba a biya shi.
Sannan lauyan gwamnati ya k'ara kafa hujja da ce wa "saboda Tijjani yasan ba shi da gaskiya ya dauko wiwi da koken mai nauyin tam goma shi yasa ya ki tsayawa da jami'an tsaro suka tsayar da shi wanda hakan rashin da'a ne da raina jami'an tsaron da k'asa ta wakilta su duba shige da ficen al'umma."
Na zuba wa Tijjani ido da yana tsaye jikin kantar da ake tsayar da wadanda ake tuhuma. Ya zube aiun, ya sake yin duhu.
Zuciyata ta karaya, na hangi rashin sassauci a shari'ar. Ta zo fiye da yadda muka tsammace ta.
Domin maganarsa d'aya ce ba shi kayan aka yi, bai san kuma san mutanan ba. Lambar wayar da ya gabatar a matsayin wacce aka kira shi da ita bata yi.
Jikin kowa ya yi sanyi. Bayan dogon rubutu da alkalin ya yi.
Ya yi gyaran murya ya ce "Duba da hujjojin da lauyan gwamnati da kuna jami'an tsaro suka gabatar kotu ta yanke wa Tijjani hukuncin shekaru biyar a gidan yari babu tara. Bisa kama shi da safarar kwaya wanda hakan ya saba kashi na goma sha takwas b cikin baka. Bayan haka kotu ta sake d'aure shi shekara d'aya bisa cin zarafim jami'an tsaro da ya yi ta hanyar yi musu gaddama. Har ila yau kotu ta daure Tijjani na watanni uku ko tarar dubu ashirin saboda rashin kiyaye kaidojin kasuwanci. Ba zai yiwu mutum yana hulda da jama'a ba amma babu taka tsantsan da sanin me mutum ya dauko ko mai zai kai. Yana cikin dab'iun d'an kasa na gari ya zama yana duba komai yana kuma kiyaye dukkan doka."
Ya rattaba hannu akan takardun tare da buga stamfi.
Gabadaya ahalinmu hankaliinmu ya yi mummunan tashi. Ni kam kuka na ke yi mai gunza. An daure shi shekaru bakwai babu tara?
Wacce irin bak'ar kaddara ce wannan?
A harabar kotun muka tsaya da shi tunda Yaya Ammar na cikin ma'aikatam gidan yarin. Na kalle shi sai kawai na fashe da kuka a dalilin raunin da na ga ni ya bayyana masa a dukkan jikinsa da zuciyarsa.
Muka zubawa juna ido ba tare da mun tuna daruruwan mutanen da suke wajen ba .
A sanyaye ya ce "Asiya shekaru bakwai da yawa. Tashin hankalina bai wuce ke ba. Ba zaki iya ba. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun "
Sai kawai hawaye ya ya k'wace masa shabe shabe".
Na rik'e hannunsa na ce "Ko shekaru sha bakwai ne zan jira ka Baban 2. Idan har rayuwarmu ta kai zaka fito ka tarar da ni a dakin ka. Zan kiyaye maka amana, zan yi aiki tuk'uru na kular maka da y'aya'n ka. Jarumtar nan da ka ke fad'in na dinga yi, zan nin ka ta daga yau".
Baban Marina ya dauke idonsa amma bai iya tsayar da hawayensa ba. Tijjani ya matsa kusa da shi ya ce "Wallahi ban aikata laifin da aka jingina mini ba, rami aka haka mini na fad'a. Ka taimake ni, ba zullimin hukuncin ne ya zautar da ni ba. Fargabar yadda zan iya rasa Asiya ne. Shekaru hudu ne gejin da shari'a ta dibawa mace akan dakon mijinta. Ni kuwa shekaru bakwai aka zarge ni".
Hawaye ya cigaba da tsere babu kakkautawa.
Baba ya kasa ce wa komai. Su Yaya Salisu kowa hawaye. Cikin k'arfin zuciya na ce "Idan ni ce matsalar ka, to ka kaddara baka da damuwa. Zan jira ka. Ba ka ce ko ka mutu na zama jaruma dan na tallafi y'aya'n ka ba? Zan kiyaye mutuncin ka, zan kuma maye wa y'aya'n ka gurbin ka har zuwa lokacin da zaka dawo ka cigaba da kulawa da mu gabadaya. Ka sa a ranka ban yi kokwanto akan ka ba Tijjani. Na gasgata ka, na yarda da kai."
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Allah ya k'ara lafiya Baba. A sanya ni cikin addu'a. Ni kuma ya mini murmushi kad'an ya ce "Na gode".
Daga haka suka tafi da shi.
Fir na k'i yarda na koma Toro. Domin idan ina gida tashin hankalina yafi yawa a dalilin ina ganin tamkar Tijjani ya rasu ko mun rabu. Bayan haka karatun yara ya dakata.
Baban Marina bai matsa mini ba, jikinsa ya yi laushi ya kamu da mugun tausayinmu.
Yaya Indo ta zauna da ni na kwanaki biyu. Komai ita take yi, ta ji da hidimar yara ta kuma yi girki da kwantar mini da hankali. Tun sanadin auren Nasiba muka hade da su. Gabadaya yan k'ofarmu muka dinke, muka dunkule, duk wani tsegmi ya yi s'auki tunda dama manyan namu ne karkatattu.
Sai da Babah ta Bulkachuwa ta zo sannan ta tafi. Dada ce ta zartar da umarnin Babah ta zo ta zauna da ni. Cikin alhinin rashin Tijjani da kuma tausayi da kyautatawa muke zaune. Nasirun ta wanda shi Ihisan take bi a kai a kai yake zuwa mana domin dalibi ne a jami'ar Abubakar Tafawa Balewa da take cikjn Bauchi.
A kuma wannan ranar za'a yanke wa Tijjani hukunci.
Da wuri muka iso. Da ni, da Yaya Salisu da Baban Marina da kuma Yaya Salamatu.
Sai ko Yaya Ammar da yake Bauchi.
Karfe shadaya aka fara shari'arsa. Babu wata hujja da zata wanke Tijjani. Domin lambar da ya ce an k'ira shi da ita kwata kwata bata shiga. Sannan an tambaye shi me yasa da aka ba shi kaya bai bude ya duba ba? Tunda ya dauki delivery a matsayin sana'a. Me yasa ba ya nazarin kauce wa dukkan wata matsala da zata taso. Wajibi ne idan zaka karbi sako, ka duba ka ga mene ne a ciki tunda idan aka kama ka ai kai ne a ciki.
Sannan me yasa bai binciki ainihin inda mutumin yake ba?"
Lauyan da k'aninsa Aliyu ya daukar masa, ya kasa inkarin hujjojin lauyoyin gwamnati tunda tabbas Tijjani bai yi bincike ba ya karbi kaya. Bai kuma bude ya duba ba. An ba shi abu a d'aure cikin buhu kawai ya danna a mota. Sannan bai san mutum ba. Kawai ance idan ya je Kano za'a karba a biya shi.
Sannan lauyan gwamnati ya k'ara kafa hujja da ce wa "saboda Tijjani yasan ba shi da gaskiya ya dauko wiwi da koken mai nauyin tam goma shi yasa ya ki tsayawa da jami'an tsaro suka tsayar da shi wanda hakan rashin da'a ne da raina jami'an tsaron da k'asa ta wakilta su duba shige da ficen al'umma."
Na zuba wa Tijjani ido da yana tsaye jikin kantar da ake tsayar da wadanda ake tuhuma. Ya zube aiun, ya sake yin duhu.
Zuciyata ta karaya, na hangi rashin sassauci a shari'ar. Ta zo fiye da yadda muka tsammace ta.
Domin maganarsa d'aya ce ba shi kayan aka yi, bai san kuma san mutanan ba. Lambar wayar da ya gabatar a matsayin wacce aka kira shi da ita bata yi.
Jikin kowa ya yi sanyi. Bayan dogon rubutu da alkalin ya yi.
Ya yi gyaran murya ya ce "Duba da hujjojin da lauyan gwamnati da kuna jami'an tsaro suka gabatar kotu ta yanke wa Tijjani hukuncin shekaru biyar a gidan yari babu tara. Bisa kama shi da safarar kwaya wanda hakan ya saba kashi na goma sha takwas b cikin baka. Bayan haka kotu ta sake d'aure shi shekara d'aya bisa cin zarafim jami'an tsaro da ya yi ta hanyar yi musu gaddama. Har ila yau kotu ta daure Tijjani na watanni uku ko tarar dubu ashirin saboda rashin kiyaye kaidojin kasuwanci. Ba zai yiwu mutum yana hulda da jama'a ba amma babu taka tsantsan da sanin me mutum ya dauko ko mai zai kai. Yana cikin dab'iun d'an kasa na gari ya zama yana duba komai yana kuma kiyaye dukkan doka."
Ya rattaba hannu akan takardun tare da buga stamfi.
Gabadaya ahalinmu hankaliinmu ya yi mummunan tashi. Ni kam kuka na ke yi mai gunza. An daure shi shekaru bakwai babu tara?
Wacce irin bak'ar kaddara ce wannan?
A harabar kotun muka tsaya da shi tunda Yaya Ammar na cikin ma'aikatam gidan yarin. Na kalle shi sai kawai na fashe da kuka a dalilin raunin da na ga ni ya bayyana masa a dukkan jikinsa da zuciyarsa.
Muka zubawa juna ido ba tare da mun tuna daruruwan mutanen da suke wajen ba .
A sanyaye ya ce "Asiya shekaru bakwai da yawa. Tashin hankalina bai wuce ke ba. Ba zaki iya ba. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun "
Sai kawai hawaye ya ya k'wace masa shabe shabe".
Na rik'e hannunsa na ce "Ko shekaru sha bakwai ne zan jira ka Baban 2. Idan har rayuwarmu ta kai zaka fito ka tarar da ni a dakin ka. Zan kiyaye maka amana, zan yi aiki tuk'uru na kular maka da y'aya'n ka. Jarumtar nan da ka ke fad'in na dinga yi, zan nin ka ta daga yau".
Baban Marina ya dauke idonsa amma bai iya tsayar da hawayensa ba. Tijjani ya matsa kusa da shi ya ce "Wallahi ban aikata laifin da aka jingina mini ba, rami aka haka mini na fad'a. Ka taimake ni, ba zullimin hukuncin ne ya zautar da ni ba. Fargabar yadda zan iya rasa Asiya ne. Shekaru hudu ne gejin da shari'a ta dibawa mace akan dakon mijinta. Ni kuwa shekaru bakwai aka zarge ni".
Hawaye ya cigaba da tsere babu kakkautawa.
Baba ya kasa ce wa komai. Su Yaya Salisu kowa hawaye. Cikin k'arfin zuciya na ce "Idan ni ce matsalar ka, to ka kaddara baka da damuwa. Zan jira ka. Ba ka ce ko ka mutu na zama jaruma dan na tallafi y'aya'n ka ba? Zan kiyaye mutuncin ka, zan kuma maye wa y'aya'n ka gurbin ka har zuwa lokacin da zaka dawo ka cigaba da kulawa da mu gabadaya. Ka sa a ranka ban yi kokwanto akan ka ba Tijjani. Na gasgata ka, na yarda da kai."
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Allah ya k'ara lafiya Baba. A sanya ni cikin addu'a. Ni kuma ya mini murmushi kad'an ya ce "Na gode".
Daga haka suka tafi da shi.
Fir na k'i yarda na koma Toro. Domin idan ina gida tashin hankalina yafi yawa a dalilin ina ganin tamkar Tijjani ya rasu ko mun rabu. Bayan haka karatun yara ya dakata.
Baban Marina bai matsa mini ba, jikinsa ya yi laushi ya kamu da mugun tausayinmu.
Yaya Indo ta zauna da ni na kwanaki biyu. Komai ita take yi, ta ji da hidimar yara ta kuma yi girki da kwantar mini da hankali. Tun sanadin auren Nasiba muka hade da su. Gabadaya yan k'ofarmu muka dinke, muka dunkule, duk wani tsegmi ya yi s'auki tunda dama manyan namu ne karkatattu.
Sai da Babah ta Bulkachuwa ta zo sannan ta tafi. Dada ce ta zartar da umarnin Babah ta zo ta zauna da ni. Cikin alhinin rashin Tijjani da kuma tausayi da kyautatawa muke zaune. Nasirun ta wanda shi Ihisan take bi a kai a kai yake zuwa mana domin dalibi ne a jami'ar Abubakar Tafawa Balewa da take cikjn Bauchi.