← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 146

Sashe 25

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

*Dukkan littafan Saliha Abubakar Abdullah Zaria akwai su in soft copies a hannuna.*

Takaicinsa ya shake Yaya J. Ya nuna shi da yatsa ya ce "Bana son irin haka Bulkachuwa".
Ya make kafa'da alamun ko oho ya wuce yana sake fa'din "Ato ai gaskiyar magana kenan, ku barta ta ji da bacin ran da take ciki mana, ai kowa yasan tana sonka, akan idonta da na iyayenta aka dauki wata aka baka, ka karba da sunan biyayya, amma ka kasa gwada kwanjin ayi maka alfarmar ka ha'de su biyun ka yi wuf da su.
Sai kuma ka dinga tare ta kana tayar mata da hankali a wofi. Ita ma k'uruciya ce ya sanya take zubar da hawaye akan ka.
Ni yanzu da na fahimci inda aka ajiye ni, na sake yiwa Nasiba kallon soyayya ne? Duk nacin ta bana sauraron ta".
Daga haka ya fice gaba'daya.
Yayin da Ba'kin ciki mai tsananin gaske ya dabaibaye Yaya J.
Ya ce "Ban da ma idon ka babu kunya Bulkachuwa har ka iya tsayawa ka ce zaka fa'da wa wani dai-dai?
Ina ka santa, ai kanka zaka fara yiwa bitar gaskiyar kafin wani, wanda tsoron Allah baya iya hana shi aikata kaba'ira, shine zai yi kishin ana bata wa wata lokaci, kai kuma *BAK'AR TA'ADAR* lalata y'ay'an jama'ar da kake yi fa?
Ko an ce maka daga sama suka fad'o babu mai kishinsu?"

*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*

✍️
*BAKAR TA'ADA*
*NA*
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*
*(MRS M.I.NASHE)*

*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•

*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAYAN G.H.T.* *DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA*. *HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*07039269802*

*Follow me @Arewa books*
https://arewabooks.com/chapter?id=6504c04660ef31f52af5ad6c

*VIP 1k*
*Regular 500 via*
*2384876855*
*Surayya Ibrahim*
*Zenith Bank.*
*08032773332*.
*Free pages na daf da tsinke wa*
*Ku zo ku shiga tafiyar Yabi. Sa'adan Mk da Guduyon Gudale tuni suna cikin paid group*.

15&16.
Bulkachuwa ya juyo ya ce "Tir da masu gori, Albarkar Annabi ba zaka samu Asiya Toro ba, tunda kallon kitse nake yiwa rogo, marar mutunci kawai".
Ya juya ya yi tafiyarsa a tunzure.
Ya juyo da nufin yi mini magana sai kawai na d'aga masa hannu na ce "Kada ka ce mini komai Yaya J.
Wannan maganar fa, gaskiya ce tsagwaro.
Na roki arzikin ka bar ni na ji da damuwata".
Na juya na tafi.
Na bar shi yana fa'din "Kaicon Bulkachuwa, ko har yaushe yasan mutuncin gaskiyar da har yake wannan zugar?"
Ina shiga d'akin Gwaggo na zube na fashe da kukan da ya ja hankalinta k'warai da gaske.
Ta jani jikinta ta ce "To mene ne kuma?
Kin yi k'ok'ari, kin yi ha'kuri, sake daure wa mana, komai zai wuce fa".
Na saka hannuna na rike ta sosai, baki na rawa na ce "Yi mini addu'a Gwaggo, ki yafe mini bacin ran da na yi ta sanya ki.
Ina jin mutuwa zan yi."
"Ba zaki mutu ba Yabi.
In sha Allah! Ubangiji ba zai bar ki hakan ba, ai yasan an zalunce ki, amma daure ki cigaba da nuna jarumta, ki cigaba da sha'aninki tamkar baki da wata damuwa."
Na ce "Abin ne yake neman fin k'arfina".
Na fa'da, kuka na sake kwace mini.
Ta dinga bubbuga bayana tana fa'din "yadda aka yi din ne akwai tozarci a ciki, amma ni dama bana son wannan ha'din domin tsananin da zaki fuskanta mai girma ne. Allah ya sa haka ne mafi alheri.
Share hawayenki ki d'oro alwallah ki yi ta nafila tunda hantsi ne yanzu."
Na kuwa mike ina share idon nawa, na fita da zummar yin alwallah.
Na dawo na tarar da ita, tana ganin kayan da suke cikin ledar.
Leshi mai kyau, da mayafin da ya dace da shi, da doguwar riga abaya, da takalmi da jakarsa, sai tarkacen sark'a da abin hannu ga kayan kwalliya da turaruka.
Da envelope mai dauke da wasika da kudin dinki.
Gwaggo ta ce "Wannan kaya masu daraja haka? Ajiye wa za'a yi sai Babanku ya ga ni".
Na tayar da sallah ban ce komai ba.
Chapter 25 · 0% Book details