← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 146

Sashe 22

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*

13&14.
Da azama na shige cikin gidan na bar shi domin na samu sau'kin halin da nake ciki.
Kuka na dinga yi tamkar zuciyata zata fa'do k'asa, bansan son Yaya J ya tumbatsa a zuciyata irin hakan ba sai yau, domin sai na tsinci kaina da addu'ar na zama gawa kafin igiyar aure ta d'auresu da Maijidda.
A wannan daren barci rabi rabi na yi shi.
Washagari da hantsi sai ga shi ya dawo, kallo d'aya na yi masa na gane yana cikin zullumi mai yawa domin gaba'daya ya zube ya sake fige wa.
Yaya Salisu da ba shi da matsala da kansa ya masa iso har cikin falon gidan da yake dakuna uku ne a jere falle falle.
Na fito a sanyaye sanye da hijabi idanuwana a kumbure a dalilin kuka da rashin barci.
Na zauna a kujerar da ta yi nesa da wacce yake zaune.
Tsawon lokaci muna zaune jigum jigum, tamkar masu makoki, daga karshe dai ya k'osa cikin murya marar amo ya ce " Yabi babu gaisuwa ne?"
Kaina a kasa na ce akwai gaisuwar da tafi nema maka amincin da na yi?
Shin ka raina sallamar ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Hakkun Yabi. Kin fini kusa da daidai, kin yi barci kuwa?".
Kaina a k'asa na ce "Me zai hana Yabin Marina barci a wannan duniyar? Sai mutuwa, ko ciwo".
A matu'kar sanyaye ya ce "Idan kuwa hakane ki shirya kwanan zaune domin kullu nafsin za'ikatul maut. A kowanne lokaci muna iya rasa mutane mafiya daraja a rayuwarmu, ko kuma a jarrabemu da ciwo mai hana runtsawa. Fata dai Allah ya bamu ikon cinye dukkan jarabawowin da suke dunfaromu.
Ban da dai dan-adam an jarrabe shi da tsoron mutuwa, mene ne abu mai da'di a cikin wannan duniyar da a kullum tsanani da bacin rai suke sake yiwa mumini k'awanya?"
Ban tanka masa ba, domin kuwa gaba'daya zuciyata babu sukuni, kuma cike take da ba'kin ciki mai nauyi.
Cikin alhini ya ce "Yabi ban yi zaton munin dambarwar da take faruwa ta kai lalacewar da ta yi ba!
Na gamsu, na ha'kura da aurenki a yanzu, dan na tsaremu daga fa'dawa halaka.
Amma na rantse miki babu wata macen da zan sota irin son da nake yi miki, zan kuma dauwama a cikinsa.
Tsoron hakkkm iyaye ne kawai zai sanya na yarda na yi aure kuma na mua'amalaci matar cikin adalci. Amma ban ha'kura da ke ba, zan cigaba da kokarina har sai Ubangiji ya mini taimakon tabbatar da aurenmu.
Hawaye ya balle masa tamkar ba namiji ba.
Da rawar murya ya ce "Akwai bukatar mu tsananta addu'a a cikin zumuncin Gidanmu Yabi. Daga jiya zuwa yau na fahimci BAK'AR TA'ADAR wariyar launin fata, ta yi kane kane a cikin gidan".
Na dago idona jage jage da hawaye na ce "Komai zai dai-daita idan arzikin Baban Marina ya dawo, ko idan ya'yansa suka kawo k'arfi."
A kasalance ya ce "Ba wannan ce matsalar ba kawai.
Shin menene ribar hana ni auren ki?"
Na dago na ce "Saboda ana ganin zan samu cigaba, ana ganin ban cancanci na samu irin wannan darajar ba, bai kuma kyautu ayi wa Baban Marina irin wannan zumuncin ba tunda ba za'a amfana da shi ba, an kuma rufe ido an mance irin amfanar sa da aka yi a shekarun baya".
Ya yi shiru ya ce "ban gamsu ba, idan kuma wannan ne hujjar da gaske?
Menene dalilin da zai sa ba za'a bawa Bulkachuwa auren Nasiba ba?
Ai duk lalacewarsa jininmu ne. Idan za'a hana shi mace a cikin danginsa to ina za'a bashi? kawai halin da ya jefa kansa ne ya sanya baya iya tanadi. Amma idan aka bashi mace na tabbatar indai yana samun nutsuwa da ita, zai nutsu ya zama mutum na sosai, sannan zai daina zalama da tsilla tsillar da yake yi tunda yana da tasa ta halal a dakinsa ."
Duk da matsananciyar damuwar da nake ciki sai da maganganunsa suka jefa ni cikin kunya da takura.
Na kasa magana.
Ya sake cewa "To saboda Allah idan ba'a taimake shi a cikin danginsa an rufa masa asiri, an tsaya kai da fata wajen ganin al'amarinsa ya kintsu ba, me za'a yi masa? A wajene ake son ayi masa irin wannan sadaukarwar da kishin kai?
Babban tashin hankalin ita Nasiban sonsa take yi kamar ta kai kanta dakinsa. Da ace bata sonsa na zan ga laifin kowa ba.
Shin wanne irin zamani muke ciki ne mai cike da son zuciya?"
Nan ma na kasa cewa uffan domin tunanina ya riga ya tsuke, ban sani ba ko dan har yanzu ban gama fahimtar al'amuran da shi ya fahimta a tsakanin yammacin jiya zuwa yau ba.
Ko dan ya fini shekaru, ya kuma fini ilimi da hangen nesa ne oho.
Gaba'daya a rikice yake, k'warai kwamacalar da take cikin gidanmu ta gigita shi.
Nasan bai san haka abin ya tsananta ba, tunda ba kasafai yake zaman garin ba.
Ya jima kafin ya sake cewa komai.
Ya mike ya zura hannunsa a aljihunsa.
Ya ce "Bansan me zan ce miki ba, amma nasan zan rayu da son ki a raina muddin rai.
Zan kuma rayu tamkar wanda ya rasa bangare guda a jikinsa. Ina fatan Ubangijinmu Allahu ya sanya mu cikin masu soyayya dan Allah. Har kuma yanzu da nake miki wannan jawabin ban cire alkalamina a cikin tawada ba. Ban cire rai cewar kaddara tana iya bani damar mallakar ki a matsayin matata ba.
Ina neman alfarma, komin kankantar damar da zamu samu ta cikar burinmu kada laifin da bani na yi ba, ya shafi hakan Yabi.
Ina da burin idan mun yi aure na mayar da ke makaranta ki zurfafa a ilimummuka daban daban.
Amma ko yanzu ma ban fitar da rai ba, lokaci zai zo da zaki tsaya ki yi karatu tuk'uru, ki cire shiriritar da kike yi.
Mu tsananta addu'a, mu barwa Allah ya yi mana zabin da ba zamu koka ba. Kin fini gaskiya duk al'amarin da babu saka albarkar iyaye to tsinannen al'amari ne.
Fatan alheri gareki Yabin J".
Ya fice da sauri.
Jikina ya yi matu'kar sanyi, domin na tabbatar akwai abin da Yaya J ya ga ni a cikin zumuncin Gidanmu da ya warware masa duk wani confidence dinsa.
Na kagu na samu labarin irin wainar da ake toyawa a gidan Marina.
Na rasa yadda zan yi, domin Yaya Salisu ba mai zama ya tattauna magana da mutane ba ne.
Na matsu kwarai na ga Nazira domin a bakinta zan ji komai kuma babu k'arya ko karin gishiri a cikin kalamunta.
Kwanaki suka yi ta shudewa, ban samu ganin Nazira ba, ban kuma ji labarin komai ba.
Abin da yake damuna daya ne takunkunmin hana ni zuwa gida da aka sanya mini.
A hakan har na shafe kwanaki ashirin da biyar a gidan Yaya Salisu.
Na riga na kai k'ololuwar gajiya da son jin makoma ta.
Gashi ba wanda ya zo daga gidanmu.
Dan ma ina samun y'an kitso da k'unshi, suna biyo ni, haka na unguwar ma suke yi mini layi.
Rannan da na gaji, sai kawai na zari jiki na doshi gida a sayyadata duk da tazarar gidan Yaya Salisu zuwa Gidanmu tafiya ce mai tsayi ainun.
Tunda na kusa k'arisa wa na fara jin jikina na kakkarwa, ga kuma luguden da zuciyata take yi tamkar ta faso ta fito.
Bakina na ambaton sunan Allah, duk da idan ance na fa'di me nake fa'di ba zan iya tantance wa ba.
Na fa'da zauren na yi kicibus da Baban Tsakiya, zai fita, da alamun rashin sukuni a tare da shi.
A farko kamar ba zan gaishe shi ba.
Bansan ya aka yi ba, cikin rawar murya na ce "Baban Tsakiya ina yini?"
Ina daga tsaye ban rusuna ba.
Ya mini dak'uwar da ta zame masa dabi'a ya ce "Baban farko ba na Tsakiya ba. Wato ke tabbataciyar yarinya ko? Sai kin ha'da da inkiya saboda ba kya mini kallon arziki.l?
Zan ga mai daura miki aure, sai dai Ubanki ya waklice ki da kansa.
Kuma indai ina numfashi duk wanda ya zo neman auren ki sai na fa'da masa rashin d'aarki da hatsabibanci irin na ki, domin fadar gaskiya a neman aure jihadi ne kabiran".
Na yi k'asa da kaina ba tare da na ce komai ba.
Ya juya ya tafi yana ta yi mini sababi da kwashe albarka da fatan tsiya iri iri.
Na jingine a jinkin garun ina tambayar kaina "Wai haka kowa yake fuskantar bacin rai da danginsa ko kuwa iya ni ce?

*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH*.
Chapter 22 · 0% Book details