Sashe 101
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Watanni bakwai a gaba*
Zuwa wannan lokacin mun koma Bauchi da zama. A satin nan kuma na yaye yara. Bulkachuwa aka kaiwa Babah su. Kwance nake ina fama da zazzabin da ciwon nono ya zuba mini. Ga kewar yara, abin sai ya hadu ya kwantar da ni. Nasan Hanif ba shi da matsala, amma Hamim kam sai Allah. Rashinsa ya fi takura ni.
Tijjani kuwa sai tsokana ta yake da fa'din Hanif ne kawai zai dawo, Hamim ya zama dan Bulkachuwa.
Bana ce wa komai amma na sani zolaya ta yake yi.
Sai da na sha allurai sannan na warware.
Sannu a hankali na shiga saboggina tunda anan Bauchi ma na fara sanuwa a wajen k'unshi da kitso, sai dai ba kaman Toro ba.
Matsakaicin gida ya kama, cikin madaidaiciyar unguwa.
Cikin nutsuwa da rufin asiri mukr rayuwarmu. Har yau din nan Bulkachuwa tattala ni yake yi. Baya kaunar abin da zai ha'damu rikici sai dole. Baya mini fishin da ya wuce na kwana d'aya. Ni ce dai nake jarumtar share shi na lokaci mai yawa.
Duk da ni din ma karfin hali nake yi.
Yanzu haka Tijjani yana da nasa teburin a cikin kasuwar ma'ana ba k'arkashin Alhaji yake ba. Watanni uku ya karbi ku'dina ya mallaki wajen flda zai ajiye teburinsa. Zobena daya muka siyar. Yanzu haka jiya ya kai ni na zabi wanda nake so ya siya mini a madadin nawa.
Na sani ba dan ya samu damar biyan ba ne, sai dan yana son ya biya ni ne.
Hakan kuma bai sa sun rabu da Alhaji Auta ba.
Ana cikin haka guda cikin kamfanin sadarwa ya nemi kafa turakan ayyuknasu cikin unguwar da filin Tijjani yake. Gaba'daya mutanan da suke da fili a wajen kowa fata yake a ce su karbi nasa, tunda haya zasu kar'ba.
Alhaji Auta har addu'a ya baza a yi masa ko ya samu ya d'an farfado.
Kamfani har yanzu zagaye yake tare da wakilinsu da suka san ilimin kimiyya suna ta auna inda zasu fi samun sabis.
Gaba'daya Tijjani bai sa hankalinsa a wajen ba. Gara ma jiya ya ce mini ku'din da mutum zai samu a shekara d'aya kacal ba k'ananu ba ne.
Ina bu'de baki na ce "Idan akwai alheri a cikin samun da za'a yi, Allah ya saukar a kan filinmu".
Ya ce "Kayya! Amma tunda Allah kika ce ai magana ta k'are. Ameen".
Muka bar magana a hakan.
A wannan tsukun auren su Yaya Ammar da na Yaya Rabiu da su Kaltume ya zo.
Muka shirya muka tafi tare. A can muka tarar da Babah da y'an yayenta. Hamim na ganina ya cakume ni, ya cukuikuiye hijabina wai bazan gudu na bar shi ba. Hanif kuwa kawai kwantar da kansa ya yi a jikina. Tijjani ya kalle shi ya ce "Kai ma ka bi bayan d'anuwan ka, baka ta tawa ko?" Ya kalle shi kawai. Ya yafice shi tare da ce wa "zo mana Babana".
Ya kuwa isa gare shi ya kwanta. Yayin da Hamim ya rikice sai ya sha nono. Da k'yar Tijjani ya yane shi suka fice.
Babah ta ce "Ai ban yi zaton darun d'anuwana ya kai haka ba sai yanzu".
Na ce "Ai ba shi da sau'ki Babah. Hanif ya fi sassauci". Ta ce "Babu hadi ma. Allah ya musu albarka ya tsare su. Ki yawaita yi musu addu'ar tsari da kuma kambun baka".
Cikin na ce "To".
Duk inda na shiga sai an kalle ni. Da na juya baya za a hau zancena. Haka Ikilima ta jiyo mini gulmar da sa'anina da muka taso tare su Saratu su Maijida. Suna fa'din ",Ai gaba'daya Bulkachuwa tsorona yake ji saboda ina da ku'di. Duk kafafar da nake yi da burgar kwalliya da yadikan yan gayu na Umm Nihla collection. Ni nake yiwa kaina ba shi ba ne. Su kuwa sun gode Allah mazajensu ne suke dawainiya da su yadda Allah ya hukunta. Barin Maijidda da a yanzu suke Kaduna. A dalilin Yaya J ya samu aiki a kwalejin kimiyya ta kaduna(Kad-poly).
Gaskiya ne duk ta fimu d'aukar ido. Amma kuma ba wai ta fi kowa kwanciyar hankali ba ne. Ko wacce ita tasan yadda take zaune a gidanta.
Nasiba tuni ta sake dawowa gidanmu gaban Dada. A yanzu da bata da aure ma tafi walwala da kwanciyar hankali. Tunda yayanta Ammar na kula da ita daidai gwagwado. Sannan iyayen mijinta suna ri'ke da Muhsin cikin kulawa, Maryam din da take shan nono ma sukan yi mata aike lokaci zuwa lokaci. Gaba'daya ta murmure ta dawo da jikinta da ta rasa a baya. Sai daga baya aka gane komai na d'akinta ashe ya siyar tunda mashayi ne kuma dan caca. Da ace wata a k'ofarmu hakan ta same ta da anyi yamididin halin d atake ciki. Amma wannan shiru ake ji.
Tallafin da take samu ya sanya take figa take yin y'an sitturu da kayan kwalliya dan haka fes take bata da makusa.
Na yi tsuka na ce "Basu da abin yi ne, koma a ya ya na ke rayuwa ai babu ruwansu, tagayyara da ake mana fata kuwa ba zamu shige ta ba in sha Allah."
Amma a tunzure nake kwarai da Maijidda. Na kuma ku'dire indai ta sake ta mini maganganun banza yadda ta saba yi mini, idan mun hadu a taro, to a wannan karon zamu sake gwada yar kwanji dan na tuna mata baya.
Ta fitine ni da yawa. Nazira da take gefe ta ce "Sanin kina da daraja ne a wajen mijinta ya sanya ta washe ki, ban da haka kina matar wani, ta shafa miki lafiya mana, tunda tasan a musulunci mace bata auren miji biyu. Da a ce Nasiba ce ke, ai da tuni Maijidda ta kusa zama gawa, domin ba abin da zai hana mijinta fitowa neman auren ki, tunda har gobe yana son ki".
Da hanzari na ce "Allah suturi bukui. Ai sai yanzu na fahimci tun asali ba wani sonsa na yi ba, shak'uwa ce da soyayyar k'uruciya. Yanzu da na saba mua'amalantar barden namiji irin Baban 2, mai zan yi da dan karamin sauron mijinta? Su je can su k'arata har abada ba zai sake burge ni ba."
Dadi ya kama Adda Nazira ta fashe da dariya ta ce "Ina komawa zan fa'dawa Baban su Abid tun yanzu Yabi ta fara fa'din madallah da auren Yaya Bulkachuwa".
Kunya ta dan rufar mini na ce "eh ki fa'da masa".
Haka aka yi bikin aka gama lafiya. Baba Maryo da kanta wani gani gani take yi mini da ban san dalilinsa ba. Ba dama ta ga Babah ta yi mini wani abu sai ta ce "Ba hakan aka barki ba, da aka tashi kame mata Tijjani har da uwarsa aka ha'da ban da hakan irin wannan gudun zuciyrta da kike yi har ina? Yara na son zuwa wajen uwarsu kin kanekane kin rikesu kina fa'din ta je ta yi hidimar jama'a. Ke kuma kin zama mai raino'.
A lokacin da take fa'din haka ina tsaye, wata irin fargaba ta kama ni, domin na hango kishina ke cinta ba ka'dan ba. Na laluba ko na yi mata laifi ne, amma ban ga na yi mata komai ba. Wata'kila zamana lafiya a gidan aurena ne yake mintsinarsu. Tunda da safen nan ma sai da Baban Tsakiya da na kasuwa suka tambaye ni, wai na fa'di irin zaman da nake yi, idan babu dama sai a ha'kura ramar da nake yi ta yi yawa.
A dakin Dada a gaban kuma Babah.
Na kalle su ina mamakin manufarsu. Domin ni dai jefi jefi Tijjani na matsa mini na kira na gaishe su, ina kuma yi tunda tisa ni yake yi a gaba. Amma su kam tunda na yi aure ba wanda ya ta'ba kirana ya ji lafiyata, ko ya ji ya ya na ke? Baban Marina ne kawai yake mini hakan a cikinsu.
Amma abin mamaki sune da fa'din wai na rame tsabar sun saka mini ido suna kuma adawar sun jimu k'alau ni da Tijjani.
Na bu'de baki cikin nutsuwa na ce "Satin jiya na yaye yara, na yi fama da zazzabi a dalilin haka. Sannan ni ba ni da matsalar komai ina cikin rufin asiri mai yawa. Allah ya saka muku da alheri bisa bawa Tijjani aurena da kuka yi. Bana fatan sauyi ko a aljannah ne".
Baban Kasuwa ya ce "To ya isa zabiya! Mun ji, mun ga ne ba sai kin zarce da rashin kunyar da kika saba ba."
Baban Tsakiya kuwa ya ce "Na tashi na basu waje sun sallame ni, dama sun nuna kulawa ne dan sun gane muna zaginsu a bayan idonsu akan basa kula da sha'anin yan k'ofarmu. Amma zan fara yi musu rashin kunya da iyashege."
Na fito zan shige Babah da take bawa tagwaye koko da kosai.
Suka fashe da kuka wannan karon kukan har da Hanif.
Murya babu amo ta ce "Zo ki zauna, yunwa suke ji".
Na dawo na zauna shi ke nan kuma suka yi shiru. Suka ci gaba da cin abincinsu.
Muna haka Tijjani ya shigo dan haka na sid'ad'a na fice tunda suna ganinsa.
Washagari muka koma, daga ni har Tijjani so muke mu tafi da yaranmu. Tunda sun yi sati biyu. Amma kowa ya kasa fa'dawa Babah da ta daure fuska bayan ta fahimci take takenmu.
Sai da zamu tafi ta biyo ni har zaure tana fa'din "Zan dawo muku da su, amma sai kin warware kin murje. Kina ganin dai yadda ramar ta ki ta janyo cece kuce. Ki kwantar da hankalinki, nan da wata ma zasu dawo."
Kunya ta kama ni, na shagwabe fuska na cuna baki na ce "Ni fa Babah ban damu da su ba, su zauna ma gaba'daya a wajen ki, ba ni da matsalar komai".
Ina rufe baki Tijjani ya yi maza ya ce "Bilhiillazi karya take yi miki Babah."
Ta gwale shi da ce wa "ko k'arya take yi, ai ta saya, kai da baka da kunya ai ka bu'de ka nuna na baku yaranku".
Nan da nan ya yi shiru, ni kuma na yi dariya tare da yi masa gwalo.
Da hakan muka rabu, ta koma cikin gida, mu kuma muka tafi.
✍️.
Zuwa wannan lokacin mun koma Bauchi da zama. A satin nan kuma na yaye yara. Bulkachuwa aka kaiwa Babah su. Kwance nake ina fama da zazzabin da ciwon nono ya zuba mini. Ga kewar yara, abin sai ya hadu ya kwantar da ni. Nasan Hanif ba shi da matsala, amma Hamim kam sai Allah. Rashinsa ya fi takura ni.
Tijjani kuwa sai tsokana ta yake da fa'din Hanif ne kawai zai dawo, Hamim ya zama dan Bulkachuwa.
Bana ce wa komai amma na sani zolaya ta yake yi.
Sai da na sha allurai sannan na warware.
Sannu a hankali na shiga saboggina tunda anan Bauchi ma na fara sanuwa a wajen k'unshi da kitso, sai dai ba kaman Toro ba.
Matsakaicin gida ya kama, cikin madaidaiciyar unguwa.
Cikin nutsuwa da rufin asiri mukr rayuwarmu. Har yau din nan Bulkachuwa tattala ni yake yi. Baya kaunar abin da zai ha'damu rikici sai dole. Baya mini fishin da ya wuce na kwana d'aya. Ni ce dai nake jarumtar share shi na lokaci mai yawa.
Duk da ni din ma karfin hali nake yi.
Yanzu haka Tijjani yana da nasa teburin a cikin kasuwar ma'ana ba k'arkashin Alhaji yake ba. Watanni uku ya karbi ku'dina ya mallaki wajen flda zai ajiye teburinsa. Zobena daya muka siyar. Yanzu haka jiya ya kai ni na zabi wanda nake so ya siya mini a madadin nawa.
Na sani ba dan ya samu damar biyan ba ne, sai dan yana son ya biya ni ne.
Hakan kuma bai sa sun rabu da Alhaji Auta ba.
Ana cikin haka guda cikin kamfanin sadarwa ya nemi kafa turakan ayyuknasu cikin unguwar da filin Tijjani yake. Gaba'daya mutanan da suke da fili a wajen kowa fata yake a ce su karbi nasa, tunda haya zasu kar'ba.
Alhaji Auta har addu'a ya baza a yi masa ko ya samu ya d'an farfado.
Kamfani har yanzu zagaye yake tare da wakilinsu da suka san ilimin kimiyya suna ta auna inda zasu fi samun sabis.
Gaba'daya Tijjani bai sa hankalinsa a wajen ba. Gara ma jiya ya ce mini ku'din da mutum zai samu a shekara d'aya kacal ba k'ananu ba ne.
Ina bu'de baki na ce "Idan akwai alheri a cikin samun da za'a yi, Allah ya saukar a kan filinmu".
Ya ce "Kayya! Amma tunda Allah kika ce ai magana ta k'are. Ameen".
Muka bar magana a hakan.
A wannan tsukun auren su Yaya Ammar da na Yaya Rabiu da su Kaltume ya zo.
Muka shirya muka tafi tare. A can muka tarar da Babah da y'an yayenta. Hamim na ganina ya cakume ni, ya cukuikuiye hijabina wai bazan gudu na bar shi ba. Hanif kuwa kawai kwantar da kansa ya yi a jikina. Tijjani ya kalle shi ya ce "Kai ma ka bi bayan d'anuwan ka, baka ta tawa ko?" Ya kalle shi kawai. Ya yafice shi tare da ce wa "zo mana Babana".
Ya kuwa isa gare shi ya kwanta. Yayin da Hamim ya rikice sai ya sha nono. Da k'yar Tijjani ya yane shi suka fice.
Babah ta ce "Ai ban yi zaton darun d'anuwana ya kai haka ba sai yanzu".
Na ce "Ai ba shi da sau'ki Babah. Hanif ya fi sassauci". Ta ce "Babu hadi ma. Allah ya musu albarka ya tsare su. Ki yawaita yi musu addu'ar tsari da kuma kambun baka".
Cikin na ce "To".
Duk inda na shiga sai an kalle ni. Da na juya baya za a hau zancena. Haka Ikilima ta jiyo mini gulmar da sa'anina da muka taso tare su Saratu su Maijida. Suna fa'din ",Ai gaba'daya Bulkachuwa tsorona yake ji saboda ina da ku'di. Duk kafafar da nake yi da burgar kwalliya da yadikan yan gayu na Umm Nihla collection. Ni nake yiwa kaina ba shi ba ne. Su kuwa sun gode Allah mazajensu ne suke dawainiya da su yadda Allah ya hukunta. Barin Maijidda da a yanzu suke Kaduna. A dalilin Yaya J ya samu aiki a kwalejin kimiyya ta kaduna(Kad-poly).
Gaskiya ne duk ta fimu d'aukar ido. Amma kuma ba wai ta fi kowa kwanciyar hankali ba ne. Ko wacce ita tasan yadda take zaune a gidanta.
Nasiba tuni ta sake dawowa gidanmu gaban Dada. A yanzu da bata da aure ma tafi walwala da kwanciyar hankali. Tunda yayanta Ammar na kula da ita daidai gwagwado. Sannan iyayen mijinta suna ri'ke da Muhsin cikin kulawa, Maryam din da take shan nono ma sukan yi mata aike lokaci zuwa lokaci. Gaba'daya ta murmure ta dawo da jikinta da ta rasa a baya. Sai daga baya aka gane komai na d'akinta ashe ya siyar tunda mashayi ne kuma dan caca. Da ace wata a k'ofarmu hakan ta same ta da anyi yamididin halin d atake ciki. Amma wannan shiru ake ji.
Tallafin da take samu ya sanya take figa take yin y'an sitturu da kayan kwalliya dan haka fes take bata da makusa.
Na yi tsuka na ce "Basu da abin yi ne, koma a ya ya na ke rayuwa ai babu ruwansu, tagayyara da ake mana fata kuwa ba zamu shige ta ba in sha Allah."
Amma a tunzure nake kwarai da Maijidda. Na kuma ku'dire indai ta sake ta mini maganganun banza yadda ta saba yi mini, idan mun hadu a taro, to a wannan karon zamu sake gwada yar kwanji dan na tuna mata baya.
Ta fitine ni da yawa. Nazira da take gefe ta ce "Sanin kina da daraja ne a wajen mijinta ya sanya ta washe ki, ban da haka kina matar wani, ta shafa miki lafiya mana, tunda tasan a musulunci mace bata auren miji biyu. Da a ce Nasiba ce ke, ai da tuni Maijidda ta kusa zama gawa, domin ba abin da zai hana mijinta fitowa neman auren ki, tunda har gobe yana son ki".
Da hanzari na ce "Allah suturi bukui. Ai sai yanzu na fahimci tun asali ba wani sonsa na yi ba, shak'uwa ce da soyayyar k'uruciya. Yanzu da na saba mua'amalantar barden namiji irin Baban 2, mai zan yi da dan karamin sauron mijinta? Su je can su k'arata har abada ba zai sake burge ni ba."
Dadi ya kama Adda Nazira ta fashe da dariya ta ce "Ina komawa zan fa'dawa Baban su Abid tun yanzu Yabi ta fara fa'din madallah da auren Yaya Bulkachuwa".
Kunya ta dan rufar mini na ce "eh ki fa'da masa".
Haka aka yi bikin aka gama lafiya. Baba Maryo da kanta wani gani gani take yi mini da ban san dalilinsa ba. Ba dama ta ga Babah ta yi mini wani abu sai ta ce "Ba hakan aka barki ba, da aka tashi kame mata Tijjani har da uwarsa aka ha'da ban da hakan irin wannan gudun zuciyrta da kike yi har ina? Yara na son zuwa wajen uwarsu kin kanekane kin rikesu kina fa'din ta je ta yi hidimar jama'a. Ke kuma kin zama mai raino'.
A lokacin da take fa'din haka ina tsaye, wata irin fargaba ta kama ni, domin na hango kishina ke cinta ba ka'dan ba. Na laluba ko na yi mata laifi ne, amma ban ga na yi mata komai ba. Wata'kila zamana lafiya a gidan aurena ne yake mintsinarsu. Tunda da safen nan ma sai da Baban Tsakiya da na kasuwa suka tambaye ni, wai na fa'di irin zaman da nake yi, idan babu dama sai a ha'kura ramar da nake yi ta yi yawa.
A dakin Dada a gaban kuma Babah.
Na kalle su ina mamakin manufarsu. Domin ni dai jefi jefi Tijjani na matsa mini na kira na gaishe su, ina kuma yi tunda tisa ni yake yi a gaba. Amma su kam tunda na yi aure ba wanda ya ta'ba kirana ya ji lafiyata, ko ya ji ya ya na ke? Baban Marina ne kawai yake mini hakan a cikinsu.
Amma abin mamaki sune da fa'din wai na rame tsabar sun saka mini ido suna kuma adawar sun jimu k'alau ni da Tijjani.
Na bu'de baki cikin nutsuwa na ce "Satin jiya na yaye yara, na yi fama da zazzabi a dalilin haka. Sannan ni ba ni da matsalar komai ina cikin rufin asiri mai yawa. Allah ya saka muku da alheri bisa bawa Tijjani aurena da kuka yi. Bana fatan sauyi ko a aljannah ne".
Baban Kasuwa ya ce "To ya isa zabiya! Mun ji, mun ga ne ba sai kin zarce da rashin kunyar da kika saba ba."
Baban Tsakiya kuwa ya ce "Na tashi na basu waje sun sallame ni, dama sun nuna kulawa ne dan sun gane muna zaginsu a bayan idonsu akan basa kula da sha'anin yan k'ofarmu. Amma zan fara yi musu rashin kunya da iyashege."
Na fito zan shige Babah da take bawa tagwaye koko da kosai.
Suka fashe da kuka wannan karon kukan har da Hanif.
Murya babu amo ta ce "Zo ki zauna, yunwa suke ji".
Na dawo na zauna shi ke nan kuma suka yi shiru. Suka ci gaba da cin abincinsu.
Muna haka Tijjani ya shigo dan haka na sid'ad'a na fice tunda suna ganinsa.
Washagari muka koma, daga ni har Tijjani so muke mu tafi da yaranmu. Tunda sun yi sati biyu. Amma kowa ya kasa fa'dawa Babah da ta daure fuska bayan ta fahimci take takenmu.
Sai da zamu tafi ta biyo ni har zaure tana fa'din "Zan dawo muku da su, amma sai kin warware kin murje. Kina ganin dai yadda ramar ta ki ta janyo cece kuce. Ki kwantar da hankalinki, nan da wata ma zasu dawo."
Kunya ta kama ni, na shagwabe fuska na cuna baki na ce "Ni fa Babah ban damu da su ba, su zauna ma gaba'daya a wajen ki, ba ni da matsalar komai".
Ina rufe baki Tijjani ya yi maza ya ce "Bilhiillazi karya take yi miki Babah."
Ta gwale shi da ce wa "ko k'arya take yi, ai ta saya, kai da baka da kunya ai ka bu'de ka nuna na baku yaranku".
Nan da nan ya yi shiru, ni kuma na yi dariya tare da yi masa gwalo.
Da hakan muka rabu, ta koma cikin gida, mu kuma muka tafi.
✍️.