Sashe 107
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ya yi shiru ya kasa ce wa komai. Haka ita ma. Yara ne kawai su ke ta wasa a tsakaninsu. Sai iskar fanka da take kadawa da karfi sosai. Amma hakan bai sa zufa ta daina yanko masa ba. Gaba daya ya shiga rudani mai yawa. Ya rasa inda Yabi ta gudu. Ga magaganun Babah masu tsauri. Wanda hakan yake alamta masa yana cikin fishinta.
A sanyaye ya sake bata hak'uri tare da matsar da jakar kayan yaran gabanta. Ya mik'e ya faki kallon yaran da suke wasan tsere a tsakaninsu. Ya ce "Zuwa gobe zan dawo".
Galala ta kalle shi ta ce "Dauki jaka da y'aya'nka. Ai ba zai yiwu ka kori uwarsu da baki cikinka ba. Sannan ka saka rai zan maka wahalarsu. Wato na zama shasha ma!
Ya koma ya zauna ya sassauta murya ya ce "Haba mana, dan Allah ki ji tausayi na. Gabadaya nutsuwa ta yi mini tutsu. Idan na barsu ma ba wai hutawa zan yi ba. Neman ta zan cigaba da yi. Gobe Kaduna zan tafi".
Cikin rashin nutsuwa ta ce "To ka tafi da su, ko ka fara kai su Toro wajen Nasibar sai ka wuce. Amma Wallahi ko gwaggonsu ka kai wa yaran nan, ni da kai ne".
Ya yi shiru, idon sa ya kad'a ainun, ya koma ya zauna. Murya babu amo ya ce "Ki yi hakuri dan Allah Babah."
Ta jijjiga kai ta ce "A kan Yabi Bilhillazi zan yi matukar saba maka. Zan fita a sha'anin ka gabad'aya."
Ya yi shiru. Amma ransa suya yake tamkar ya fad'o kasa.
Me ya yiwa Yabi da zata janyo masa irin wannan jidalin?
Ya dinga bata hak'uri. Da k'yar ta ce sai ya gano Yabi idan ta huce, sannan ita ma zata hakura." Ya mik'e da sauri yana fad'in "Na gode sosai. Bari na tafi neman ta da ikon Allah zan nemo ta".
Daidai lokacin Hamim ya fasa kuka yana nuna windo. Tare suka isa gare shi, suna fad'in mene ne?"
Shi dai Hanif yana tsaye, yayin da Hamim yake kuka tare da nuni da saitin windo. Nan da nan zuciyar Baba ta tsinke domin ta gano kayan Yabi yake nuna wa akan igiya. Ma'ana ya gane kayan uwarsu, a ba shi ya rik'e mata.
Nan da nan ta dauke kai, ta shiritar da Tijjani da ce wa "Tofa masa addu'a mana, watak'ila shaid'anu ke son bude masa ido. Allah ya tsaremu daga sharrin abin da bama kallonsu".
A gigice ya hau tofa masa falaki da nasi. Yaro kuwa sai zabura yake akan zai je ya dauko abin da yake ganin na uwarsa ne. Yayin da Babah take ta hirji tare da addu'ar kada Yabi ta kasa jure kukan Hamim da yake d'ada canyarwa tamkar gyare ta fito. Ita da kanta ta gane irin kukan da Yabin ta yi tana yarinya ya gado.
Ta ce "Dauke shi ku tafi. Idan ya ga kun shiga mota zai yi shiru."
A raunana ne ya ce "Yadda ya razana hakan zan tafi da shi? Ki yi hakuri na bar su a nan, gobe ko jibi da ikon Allah zan dawo na dauke su. Ko ban ganta ba.
Ta ce "A a ba fa zan rike su ba. Ai idan kasan zan rik'e maka yara ka dinga shagulatin bangaro da auren ka kenan. Ina ce lokacin da suke hannuna ka fi uwarsu nuna zalamar na baku su? Yanzu kuwa ba zan karbe su ba."
Kamar zai rushe da kuka ya ce "Gobe Kaduna zan je Baba."
A gajar ce ta ce "Tafi da su ka kai wa Ihisan. Idan ka dawo ka je ka dauke su".
A kan dole ya sunkuya ya dauki Hamim. Ya rike hannun Hanif. Bayan ya saba jakar kayansu. Yadda ya d'ebi yaran da jakarsu sai tausayinsu duka ya kama ta.
Suka fita, sai da suka jima da fita. Sannan ta bude dakin da Yabi ta ke. Ta tarar da ita zaune akan gado tana faman goge idonta tabbaccin kuka take yi.
Ta k'arisa kusa da ita. Ta ce "Yabi kuka kike dan ina kokarin ya fahimci muhimmancin ki a rayuwar sa da ta y'aya'nsa?"
Da wata irin tab'ara da kuka na ce "Ai da sai ki karbe su. Kukan Hamim kad'ai abin dubawa ne".
Ta yi galala ta zuba mini ido ta kasa ce wa uffan.
Na kuwa matse na ce "To ni dai na huce tunda haka ne. Ai ya yi ta zuwa, na kuma san yana cikin tasku, sai ki zaunar da mu, a mayar da zan ce, ki yi masa fada, mu tafi."
Ta jijjiga kai tare da ce wa "Ban yi hakan ba Yabi. Ba kuma zan yi ba".
Na kuwa juya na kwanta ina kunkunin bazan sake yin yaji na zo nan ba, tunda ba sulhu zata yi ba".
Ta dinga salati tana tafa hannu. Tare da ce wa "Ban ga laifinki ba. Amma zaki ga karshen iyashege. Dauko hijabin ki, ki bisu. Na bata rai tare da daure fuska ainun. Ta sassauta ta ce "Ba fishi na yi ba. Tunda laifin kaina zai juye to kawai ki bisu. Duk tsamin ran da nake taya ki, baki yaba ba, bare ki bani hadin kai mu yi maganinsa da kyau".
Murya na rawa na ce "To ai da sai ki karbi yaran Babah".
Ta bude murya ta ce "Na ki karbar tasu. Ina ce ke kika barsu a gidansu? Kuma ba a hannun ubansu suke ba tabbatacciyar marar ta ido!"
Na yi shiru amma dai fuskata a daure.
Kafin ta yi magana sai kukan Hamim muka jiyo tabbacin sun dawo. Kafin Baba ta fita har sun shigo falo.
Da azama ta fita tana mini kashedin kada na fito da hannu.
**
Turus ta yi ganin Hamim na rike da riga da hijabin Yabi a hannunsa, ya kuma sassauta kukan da yake yi. Sai ajiyar zuciya yake faman saki.
Kafin ta ce komai Hanif ya ruga ya dauko takalman Yabi da suke gefen falon. Shi ma ya rik'e.
Tijjani ya samu nutsuwa domin ya tabbatar tana gidan.
Yayin da Babah ta kasa ce wa komai.
Cikin nutsuwa Tijjani ya ce "Ashe ba shaid'anu ya ke nuna mana ba. Kayan ta ya ga ni. Har mun fita ya tsananta kuka, ya kuma k'i yarda ya shiga motar. Sai hannuna yake ja. Na yarda na biyo shi muka dawo, sai kawai ya kai ni baya wajen kayan. Anan na fahimci kayan Yabi ya ga ni. Dan Allah Babah ki yi hakuri, ki ji tausayinsu ki basu uwarsu."
Ta yi kicin kicin ta ce "Idan ka ganta ba sai ka daukar musu ita ba. Ai tunda har zaka wulakanta Yabi irin haka, tabbas nima zaka wulakanta ni. Dan haka ba zan zuba ido ka fara mata cin kashi bayan ta gama shanye wahalar ka ba".
Ta rik'e hannun yaran ta tura su cikin dakin. Domin sun bata tausayin yadda suka rik'e kayanta gamgam. Kayan da shafa'a ne ya sanya aka barsu har yaran suka ankarar da ubansu.
A sanyaye ya sake bata hak'uri tare da matsar da jakar kayan yaran gabanta. Ya mik'e ya faki kallon yaran da suke wasan tsere a tsakaninsu. Ya ce "Zuwa gobe zan dawo".
Galala ta kalle shi ta ce "Dauki jaka da y'aya'nka. Ai ba zai yiwu ka kori uwarsu da baki cikinka ba. Sannan ka saka rai zan maka wahalarsu. Wato na zama shasha ma!
Ya koma ya zauna ya sassauta murya ya ce "Haba mana, dan Allah ki ji tausayi na. Gabadaya nutsuwa ta yi mini tutsu. Idan na barsu ma ba wai hutawa zan yi ba. Neman ta zan cigaba da yi. Gobe Kaduna zan tafi".
Cikin rashin nutsuwa ta ce "To ka tafi da su, ko ka fara kai su Toro wajen Nasibar sai ka wuce. Amma Wallahi ko gwaggonsu ka kai wa yaran nan, ni da kai ne".
Ya yi shiru, idon sa ya kad'a ainun, ya koma ya zauna. Murya babu amo ya ce "Ki yi hakuri dan Allah Babah."
Ta jijjiga kai ta ce "A kan Yabi Bilhillazi zan yi matukar saba maka. Zan fita a sha'anin ka gabad'aya."
Ya yi shiru. Amma ransa suya yake tamkar ya fad'o kasa.
Me ya yiwa Yabi da zata janyo masa irin wannan jidalin?
Ya dinga bata hak'uri. Da k'yar ta ce sai ya gano Yabi idan ta huce, sannan ita ma zata hakura." Ya mik'e da sauri yana fad'in "Na gode sosai. Bari na tafi neman ta da ikon Allah zan nemo ta".
Daidai lokacin Hamim ya fasa kuka yana nuna windo. Tare suka isa gare shi, suna fad'in mene ne?"
Shi dai Hanif yana tsaye, yayin da Hamim yake kuka tare da nuni da saitin windo. Nan da nan zuciyar Baba ta tsinke domin ta gano kayan Yabi yake nuna wa akan igiya. Ma'ana ya gane kayan uwarsu, a ba shi ya rik'e mata.
Nan da nan ta dauke kai, ta shiritar da Tijjani da ce wa "Tofa masa addu'a mana, watak'ila shaid'anu ke son bude masa ido. Allah ya tsaremu daga sharrin abin da bama kallonsu".
A gigice ya hau tofa masa falaki da nasi. Yaro kuwa sai zabura yake akan zai je ya dauko abin da yake ganin na uwarsa ne. Yayin da Babah take ta hirji tare da addu'ar kada Yabi ta kasa jure kukan Hamim da yake d'ada canyarwa tamkar gyare ta fito. Ita da kanta ta gane irin kukan da Yabin ta yi tana yarinya ya gado.
Ta ce "Dauke shi ku tafi. Idan ya ga kun shiga mota zai yi shiru."
A raunana ne ya ce "Yadda ya razana hakan zan tafi da shi? Ki yi hakuri na bar su a nan, gobe ko jibi da ikon Allah zan dawo na dauke su. Ko ban ganta ba.
Ta ce "A a ba fa zan rike su ba. Ai idan kasan zan rik'e maka yara ka dinga shagulatin bangaro da auren ka kenan. Ina ce lokacin da suke hannuna ka fi uwarsu nuna zalamar na baku su? Yanzu kuwa ba zan karbe su ba."
Kamar zai rushe da kuka ya ce "Gobe Kaduna zan je Baba."
A gajar ce ta ce "Tafi da su ka kai wa Ihisan. Idan ka dawo ka je ka dauke su".
A kan dole ya sunkuya ya dauki Hamim. Ya rike hannun Hanif. Bayan ya saba jakar kayansu. Yadda ya d'ebi yaran da jakarsu sai tausayinsu duka ya kama ta.
Suka fita, sai da suka jima da fita. Sannan ta bude dakin da Yabi ta ke. Ta tarar da ita zaune akan gado tana faman goge idonta tabbaccin kuka take yi.
Ta k'arisa kusa da ita. Ta ce "Yabi kuka kike dan ina kokarin ya fahimci muhimmancin ki a rayuwar sa da ta y'aya'nsa?"
Da wata irin tab'ara da kuka na ce "Ai da sai ki karbe su. Kukan Hamim kad'ai abin dubawa ne".
Ta yi galala ta zuba mini ido ta kasa ce wa uffan.
Na kuwa matse na ce "To ni dai na huce tunda haka ne. Ai ya yi ta zuwa, na kuma san yana cikin tasku, sai ki zaunar da mu, a mayar da zan ce, ki yi masa fada, mu tafi."
Ta jijjiga kai tare da ce wa "Ban yi hakan ba Yabi. Ba kuma zan yi ba".
Na kuwa juya na kwanta ina kunkunin bazan sake yin yaji na zo nan ba, tunda ba sulhu zata yi ba".
Ta dinga salati tana tafa hannu. Tare da ce wa "Ban ga laifinki ba. Amma zaki ga karshen iyashege. Dauko hijabin ki, ki bisu. Na bata rai tare da daure fuska ainun. Ta sassauta ta ce "Ba fishi na yi ba. Tunda laifin kaina zai juye to kawai ki bisu. Duk tsamin ran da nake taya ki, baki yaba ba, bare ki bani hadin kai mu yi maganinsa da kyau".
Murya na rawa na ce "To ai da sai ki karbi yaran Babah".
Ta bude murya ta ce "Na ki karbar tasu. Ina ce ke kika barsu a gidansu? Kuma ba a hannun ubansu suke ba tabbatacciyar marar ta ido!"
Na yi shiru amma dai fuskata a daure.
Kafin ta yi magana sai kukan Hamim muka jiyo tabbacin sun dawo. Kafin Baba ta fita har sun shigo falo.
Da azama ta fita tana mini kashedin kada na fito da hannu.
**
Turus ta yi ganin Hamim na rike da riga da hijabin Yabi a hannunsa, ya kuma sassauta kukan da yake yi. Sai ajiyar zuciya yake faman saki.
Kafin ta ce komai Hanif ya ruga ya dauko takalman Yabi da suke gefen falon. Shi ma ya rik'e.
Tijjani ya samu nutsuwa domin ya tabbatar tana gidan.
Yayin da Babah ta kasa ce wa komai.
Cikin nutsuwa Tijjani ya ce "Ashe ba shaid'anu ya ke nuna mana ba. Kayan ta ya ga ni. Har mun fita ya tsananta kuka, ya kuma k'i yarda ya shiga motar. Sai hannuna yake ja. Na yarda na biyo shi muka dawo, sai kawai ya kai ni baya wajen kayan. Anan na fahimci kayan Yabi ya ga ni. Dan Allah Babah ki yi hakuri, ki ji tausayinsu ki basu uwarsu."
Ta yi kicin kicin ta ce "Idan ka ganta ba sai ka daukar musu ita ba. Ai tunda har zaka wulakanta Yabi irin haka, tabbas nima zaka wulakanta ni. Dan haka ba zan zuba ido ka fara mata cin kashi bayan ta gama shanye wahalar ka ba".
Ta rik'e hannun yaran ta tura su cikin dakin. Domin sun bata tausayin yadda suka rik'e kayanta gamgam. Kayan da shafa'a ne ya sanya aka barsu har yaran suka ankarar da ubansu.