← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 110 OF 146

Sashe 110

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Ya juya ga Babah ya ce "To ga shi nan ta fada miki ta hak'ura".
Ta fita tana fad'in "Y'aya'nta dai sun raunana ta. Ni kam ban so hakan ba."
Gabadaya ya yi sanyi da kalamanta. Yana ganin zasu sa na sake botsare wa. Da sanyin murya ya ce "Mu tafi yanzu ko sai anjima little?"
Na dauke kai ban amsa ba. Ya diririce. Ya ce "Mun gama magana fa Asiya".
"Sai na shirya kayana". Na fada ba tare da na juyo ba. Ya ce "To bari idan an yi azahar sai mu tafi ko?"
Ya fada da sigar da tambaya. Ni kuma na yi bakam.
Ya yi shiru yana kallona. Ya saki gauron numfashi ya ce "Ina kayan na ki suke na hada miki?"
Ban juyo ba na ce "Suna cikin wadirof din".
Ya bude ya fito da jakar kayan nawa. Ya gyara su. Ya ninke wanda Hamim ya dauko a igiya ya saka, sannan ya zuge.
Ya zauna yana ta yin mini maganganu da nufin mu yi hira. Ni kuwa sai basarwa na ke yi. Amma bai daina ba.
Ya dawo daga masallaci ya tarar yara sun tashi muna falo duka muna cin abinci.
Ya zauna shi ma ya zuba nasa.
Babah ta sake yi masa fada sosai. Sannan ta hadamu gabadaya ta ja kunnenmu akan mu kara hak'uri da junanmu. Sannan ta gode mini da har yau ban canja mata matsayin da na bata ba.
Ta rufe da ce wa "Dama idan kin ga kin gaji to wajena ne mafarki matukar ina raye".
Na amsa mata da ce wa "In sha Allah Babah".
Ya kasa hak'uri ya ce "Kin bata lasisin ta yiwa zaman aure tustu kawai Babah".
Ta girgiza kai ta ce "Matukar za'a tozarta ba. Amma idan akan son zuciya zata yi, ai ba yarda zan yi ba. Kai ba abin kunya ba ne ace anji kanki?"
Ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa. Ya ce *Tsautsayi ne. Zan kuma kiyaye.
Muka gama sannan muka yi haramar tafiya.
Har kofar gida ta rako mu tana sake ba ni hakuri.
A hanya kuwa shi da su Hanif suke ta hirarsu, yana ta amsa musu gwarmcin maganarsu.
Muka isa gidan. Kaca-kaca yake tabbacin bai samu nutsuwar da yake gyara shi ba.
Ya tafi masallaci sallar laasar. Ina idarwa na hau aikin gyara gidan. Ya dawo ya shiga taya ni. Cikin lokaci k'ank'ani muka kammala.
Na yi wanka, na shiga kicin na fara hidimar had'a abincin dare.
Ya fito sanye da jallabiya sai kamshi yake yi tabbacin shi ma wankan ya yi . Sannan ya yiwa yaran.
Ya shigo kicin din ya ja turmi ya zauna.
Ya zuba mini ido. Ya ce "Little ba ki huce ba ne?
Ban kalle shi ba. Na ce "Me ka ga ni?"
Murya babu amo ya ce "Ba ki dawo da walwalar ki ".
Na yi k'asa da kaina tare da ce wa "Na huce mana. Kawai zuciyata ce take ta yin wasiwasi mai yawa".
Ya mik'e da azama ya rungume ni ta bayana.

*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.
Chapter 110 · 0% Book details