Sashe 2
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*SHIMFI'DA*. Sunana Asiya Sani Toro. Amma mafi yawa da Yabi ake kira na a dalilin mahaifiyata ta yi aikin Hajj da ni a cikinta. Mama ce kawai bata kira na da hakan sai Asiya saboda tana adawa da Yabi tunda ana nufin nima Hajiya ce. Gidanmu babban gida ne a garin na Toro domin ko yaro k'arami ka tambayi gidan Marina zai nuna maka. A dalilin asalin kakanmu da ya zo daga Kano ya fara kafa wannan sana'ar a garin. Fiye da shekaru saba'in kenan, amma har yau ba'a juya wa sana'ar baya ba, duk da dai an zamanantar da ita, ba kuma cikin gidan ake yin ta ba saboda warinta. Gidanmu babban gida ne k'warai da gaske. Idan na ce babban gida ina nufin mai d'auke da ahali daban daban masu yawa. Ko a k'ofar mahaifinmu Alh Sani (Baban Marina) da shi ne babba mata uku ne. Hajiya Habiba ita ce uwargidan mahaifinmu, mace mai k'ifadi da kutunguila. Duk wani rikicin da yake k'ofarmu, dama cikin gidan tana da sa hannu, ta tsani ta ga ko wanne irin cigaban d'an wata sai nata yaran kawai. Sannan komai cikin dabara da girma ta ke yinsa, ba kowa ne ya fahimci irin makircin da take k'ullawa ba. Sai mu da mu ke rayuwa da ita kullu yaumin. Ta kanka ne komai, ta yadda komai ta shimfi'da akan haka za'a tafi, sai dai ranar da ta samu bacin rana Baba ya bijire mata. Ya'yanta biyar. Yaya Musa, Yaya Hadiza, Yaya Salamatu, Yaya Indo sai autarta da ta haifa bayan ta shafe shekaru masu yawa Nazira, wacce ita ce sa'a ta ta girme ni da wata uku. Sai Mahaifiyata Hajiya Àsma'u wacce muke kira da Goggo. Ba dan tana mahaifiyata ba, amma mace ce mai sanyin hali da matsanancin ha'kuri. Idan na ce ha'kuri, ina nufin ha'kuri gangariya, irin ha'kurin nan da mai yinsa kan saka a alummar da suke kewaye da shi su halaka saboda hakkinsa da za suyi ta d'auka. Yaranta takwas cif. Yaya Salisu, Yaya Rabi'u, Yaya Ummi, Yaya Adnan, Yaya Ali, sai ni Yabi, duk dai bani nake bin Yaya Ali ba, akwai wani ya rasu ne, sai Anas da kuma autarmu Ikilima. Wannan yawan yara da mahaifiyata ta tara a d'akinta, kuma maza, ya sanya Mama ta tisa ta a gaba da masifa da tuggu, kusan kowa a gidan ya tsani mahaifiyarmu, ba kowa ne yake mua'amala da ita ba. Duk gidan bakinsu daya ne a kanta. Duk kuma Mama ce ta b'ata ta, take adawa da duk wanda zata ga ya mu'amalan ce ta Shi yasa hatta mu yaranta bamu da wani kwarjini har a wajen Dada kakarmu da ita ma tana cikin gidan bangarenta daban. Sai Hajiya Sahura muna k'iranta da Innah. Yaranta biyar Na farkon ma mun dan girme masa ka'dan Ubaid, Ubaida sai Abida, Hajara, Ismail da autarmu gaba'daya Saliha. Duk yadda Mama ta so wajen raba zumunta a tsakaninmu bai yi tasiri a tsanina da Nazira ba. Duk yadda bata kula ni, bata sakar mini fuska hakan bai hana ni yin dabdala a dakinta ba a dalilin Nazira. Bare ita kuma da dakin Goggonmu take kwana.. Sau dubu gara Inna akan Mama. Domin dai ba yadda za'a yi Inna ta ha'da wa Goggo sharri, ko ta tsokane ta da gangan, amma bata wani girmama ta a dalilin Mama ta dabarbarce ta, ta hana ta yin mu'amala da Goggo ta hanyar fa'da mata Goggo ce da gida, duk yaranta maza ne, idan Alhaji ya mutu duk su din y'an kallo ne. Da na fara mallakar hankalina sai nake tambayar kaina wai mene ne mahaifinmu ya mallaka da har ake fatan ya mutu? A da kam ya yi arziki k'warai da gaske, domin duk girman Gidanmu shi ya zaga ye ya gine shi, sannan mafi yawa na cikin zuri'arsu shine ya biya musu suka sauke farali. Amma tun shekarar da aka haife ni ya ha'du da y'an damfara suka yi masa sanadin karayar arziki, har yanzu da muke da shekaru goma sha biyar bai farfad'o ba. Yan'uwansa kuma kowa ya zuba masa ido ya zama abin tausayi. Amma a hakan Mama take fa'din Goggonmu ce zata ja komai. Wannan kenan. Sai k'ofar Alh Badamasi(Baban Tsakiya). Matansa biyu da yara sha biyu. Na uwargidan Hajiya guda bakwai . Babban d'anta Yaya Jabir, Zakiya, Jamila, Hauwa, Firdausi, Aisha sai k'aramarsu , Basira. Nan Firdausi ce warinmu. Sai amaryar Momi tana da yara biyar, Nasiru, Naziru, Sararu, Rumanatu da Kubrah. Anan ma Saratu ce sa'armu. Sai kofar k'arshe ta Alh Iliya (Baban kasuwa). Matarsa daya da yaransu shida. Amina, Aminu, Maijidda, Kaltume Abba andda Aliya. Maijidda ce sa'armu Sai wajen kakarmu Hajiya Binta! wadda Yaya Umminmu sunanta ta ci. Kowa Dada yake ce mata, wata irin tsohuwa mai wahalar sha'anin gaske. Tana daga zaune rikicin da take yi ba dan ka'dan bane, haka nan bata damu da ha'din kai a tsakanin ahalin gidan ba. Domin bayan su Babanmu akwai yan'uwansu mata biyu. Bangaren Dada ma hawa biyu ne, domin akwai wata k'ofar a can ciki bayan ka wuce k'ofarta ta farko, sannan ana iya fita waje ma ta wannan wajen Sai dai kofar a rufe take. Amma ba kowa ciki sai kayan ajiye ajiye da dangin kayan noma da tarkace. Babar Bulkachuwa(Hauwa) ita ta biyo Baban Tsakiya, tana aure a Bulkachuwa, mijinta Alh Yusufu babban d'an kasuwa ne a kasuwar kayan miya ta Muda lawal a Bauchi. Ita ce amarya amma sai a kanta ya samu haihuwa ta tsaya masa, uwargidan wabi take yi, ma'ana idan ta haihu sai su koma. Tijjani ne babba sai Aliyu, sai Nasir. Sai bayan haihuwar Nasir ne uwargidan ta haifi Maryam da kuma Hafsa. Daga nan sai Babah ta sake haifar Ihisan. Kenan yaranta hudu na uwargidan kuma biyu. Tijjani ya taso cikin wani irin gata a wajen mahaifinsa a dalilin tsawon lokacin da ya shafe babu haihuwa. Sai dai kash gatan ya zame masa d'an zani domin gaba'daya sai ya kangare, tun yana karaminsa ya ko yi fitina iri iri, shine kame kaji da awakin jama'a yana siyar wa, gaba'daya ya ki kar'bar tarbiyar da ake ba shi a sanadin duk abokansa lalattu ne. Duk yadda Baba ta Bulkachuwa da mahaifinsa suke son fige masa wannan dabi'ar abin ya ci tura. Akan dole suka raba shi da garin, suka dawo da shi wajen Mahaifinmu da Baban Tsakiya, tunda su din zafi ne da su ainun. A lokacin bai fi shekaru sha biyar ba. Sa'an Yaya Salisu ne, amma shiriritarsa ta mayar da shi cikin kannensa su Anwar, duk dai su din ma sun raina shi, sun ware shi ba wanda yake son a ganshi da Bulkachuwa saboda munanan TA'ADODIN sa. Yayin da mu muke k'ananu sosai Sai Baba Maryo ita ce autar Dada. A nan Toro take aure, yaranta biyar amma biyun farko na wajen Dada da ta haifa da mijinta na farko. Anwar da Nasiba. Yaya Jabir, Yaya Rabi'u, Yaya Abba da Yaya Anwar duk sa'annin juna ne tare suka taso, fikon junansu mafi girma watanni biyar ne. Kazalika muma y'anmatan tare muka taso. Duk da babu ha'din kai ko ka'dan a tsakanin iyayenmu mata, hakanan ni da Nazira an fi mayar da mu banza da wofi a dalilin mahaifinmu ba shi da shi, ga shi dai shine babba amma ya zama fanko, ya zama wofi dai dai da shawara ba a yi da shi. Duk yadda ba wani shakuwa a tsakaninmu irin na zumunci, in dai fita ne, to tare ake tafiya zuwa makarantar boko ko Islamiya. Haka za'a ganmu zaratan y'anmatan reras da mu. Kusan ba'a ta'ba yin y'anmata da muke sa'anni da yawa a gidanmu irin akan mu ba. Domin mun doshi bakwai Ni Yabi, Nazira, Basira, Firdausi, Maijidda, saratu, Nasiba. Dukkanmu kowa turbarakallah babu makusa, tunda asalin Kakarmu Dada Bafulatanar Lame ce asalin fulanin Mali. To kusan dukkanmu mun samu tsayi da gashinta. Duk da ni din bani da tsayi, yar shafal ce, matsakaicin kyau ne da ni amma fara ce sol, sannan kuguna a dan bude yake ka'dan, sai dai kirjina kam ko na kai shekarun budurci sosai baza su yi wani girma ba. Kowanne irin sutura na saka sai ta yi mini kyau. Duk da kayan nawa mafi yawansu masu sau'kin farashi ne a dalilin mahaifinmu baya samun sukunin yi mana sutura. Abinci ma da wahalar gaske muke cinsa, duk da ga yan'uwansa nan suna cin duk abin da suke so. Amma ba'a yi mana kara ni da Nazira idan zasu yiwa y'ay'ensu sutura su ha'da da mu. Ko da yake Nazira ta fini sutura a dalilin Mama tana sanya yayyenmu na d'aki suna yi mata. Yaya Salamatu tana d'an yin kara tana bada kuncen har da ni, da yake babu laifi mijinta yana da rufin asiri, amma Mama bata bari a bani, sai dai da Yayar ta fahimci hakan sai take bani a b'oye tana fa'din ba sai na fa'da ba. Ni kuma bana iya yin shiru sai na nuna wa mahaifiyarrmu, ita kuma sai tasan yadda ta yi ta yi mata godiya tana kuma jan hankalina na kula da ita. Sosai nake ganin kirkin Yaya Salamatu duk da dai sai ta zab'e mafi kyau ta bawa Nazira ni kuma ta bani saffa saffa, amma dai ta k'ok'arta a yadda mutanan yau suka dauki y'an uban ci. Yayata da muke d'aki d'aya ita ma tana cikin matsanancin babu, domin duk talaucin gidanmu a hakan Goggo take tara mata k'anzo dan ta ci ita da yaranta. Wani irin bahagon miji take aure, bai san hakkin komai ba sai hakkin auratayya tunda kusan duk shekara biyu suke haihuwa ita da uwargidanta tamkar masu gasa. Dan ma yanzu uwargidan ta daina yi. Hatsin da za'a yi tuwon dare kawai zai bayar, dai-dai da cefanen miya mace ce zata yi, da safe a yi dumame a ci yadda ya samu, ba dan an koshi ko dan da'di ba. Da rana kuwa ko wacce ita zata ciyar da kanta da y'ay'anta. Ba maganar sabulun wanki bare a je ga na wanka. Yaya Ummi kyakkawar mace amma wahalar da miji ya sakar mata da muguntar kishiya ta saka duk ta fita a hayyacinta. Domin ita ce mai k'ananun yara, ita d'ayar al'amura sun fara saisaita mata, tunda manyan ya'yanta