Sashe 108
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Suna shiga ta janyo k'ofar ta zauna akan kujera, ta tsare gida ainun.
Ya rasa ta yadda zai fara yi mata magana.
Tsawon lokaci kafin ya tausasa harshe. Ya ce "Ina sake baki hakuri. Tunda wannan ne karon farko da ta kawo miki karata a zamanmu da ita. To ki yi mini uzziri a wannan karon . Ni kuma na miki alkawarin ba zata sake kawo miki karata akan wannan matsalar ba. Ki yi hakuri dan Allah".
Jikinta ya yi sanyi. Mussaman da ta zuba masa ido ta ga ya fada ya kuma birkice gabadaya.
Ya dinga magiya. Da ban baki tamkar zai rushe da kuka tsabar tsananta rokon da ya yi.
Rauni irin ma uwa ya shige ta. Ta furzar da iskar takaici. Ta ce "Ba dan ta yi hankalin tahowa nan ba. Da an yi ta yamididi da murnar ka yi kudi ka fara wulakanta ta. Da wanne idon zamu Kalli iyayenta da suka yi alkunya da kawaicin baka auren ta? Ta dinga yi masa fada da togaciya tamkar zata bige shi. Yayin da shi kuma yake fad'in "Ki yi hakuri zan Kiya ye da ikon Allah".
Ta tashi ta nufi daki. Ya yi maza ya mik'e ya bi bayan ta a d'arare tare da fargabar kada ta dakatar da shi.
Tana tsakiyar gadon. Yayin da Hamim yake kwance kan cinyarta. Hanif kuwa sarkin hakuri filo kawai ya yi da cinyar jikinsa na kan gadon. Daga ita har yaran kowa ya yi shiru tabbacin suna cikin alhini.
Baba ta sassauta murya ta ce "Yabi ga shi nan ku sasanta. Idan kin ga zaki yi hakuri ki bisu to, idan kuwa kin ga ba zaki bisu ba. Ba zan matsa miki ba. Ban san me kike hadiye wa ba".
Ya rasa inda zai tsoma ransa. Murya babu amo ya ce "Amma na baki hakuri fa".
"Dan ka bani hakuri sai na tirsasa ta?"
Ta jijjiga kai tabbacin ba zata mini dole ba.
Ya sassauta murya ya kalle ni ya ce "Asiya ki yi hakuri da abin ya faru. Na yi kuskure duk da dai fahimta ta ne baki yi ba".
Yana rufe baki na ce "Ba zan fahimta ba."
Babah ta yi shiru tana kallonmu. Watak'ila kuma mamakina ta yi na yadda na kame kamar ban gan shi ba tamkar ba yanzu na gama yin tijarar na huce ba ".
Ya munfasa ya ce "shi kenan ki yi hakuri." Ya furta a hankali.
Babah ta zame ta fice.
Yana ganin hakan ya matso kusa da ni ya zauna. Ya rage murya ainun ya ce "Saboda Allah little ya kamata ki bar dakin ki babu iznina?"
Na galla masa harara na dauke kai ban ce komai ba.
Ya sake tausasa harshe ya ce "Tashi mu tafi, idan mun je gida sai ki yi mini ko wanne irin darun ni kuma zan yi ta rarrashin ki, da kalolin soyayya masu tsayawa a rai."
Na ja tsaki tare da fad'in "Na bi soyayya da gudu. Ni yanzu bana son ka, kai ko ganin ka bana kaunar na bude ido na yi".
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Tom shi kenan, ki dawo dakinki dan yaran ki, ko ban ci arzikin komai ba ki dawo dan y'aya'n ki".
Na dauke kai na ce "Idan na mutu zasu fasa rayuwa ne?".
Ya rik'e kafata da tafi kusa da shi. Na goce da sauri. A tunzure na ce "Kada ka kuma tab'a ni. Ka je ka cigaba da damukar wadanda suke da daraja a wajen ka".
A zafafe ya ce "Na cigaba Asiya?".
Na dauke kai na ce "Eh".
Murya na rawa ya ce "Kin ga na damuk'e ta ne? Me yasa kike son jifa na da wannan mummunar maganar ne?"
Ba ja in ja na kalle shi na ce "Saboda ina da hujjoji na gaskiya. Sannan idan ba hakan ba, me yasa zaka kawo mini wannan suntumemiyar cikin gida? Har kuma kana kumfar bakin ba zaka ce ta tafi ba, saboda ta yi maka alkhairai. Fada mini alherorin da ta yi maka dan kuwa ban sansu ba".
Ya kafe ni da ido. Cikin matsanancin bacin rai ya ce "saboda kin fahimce ni a baibai shi yasa kika taho babu izinina, sannan kike kallon idona kike jifana da alamarin da kika san na tsani a jingina mini. Me yasa kike son ki dinga tayar mini da hankali ne Asiya?"
A tunzure na ce "Saboda ba ni da alheri a wajen ka sai sharri. Yanzu ba sai ka sakawa Nasiba da kalar naka alherin ba. Ni kuma ka bini da irin nawa sharrin ba".
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
Ya rasa ta yadda zai fara yi mata magana.
Tsawon lokaci kafin ya tausasa harshe. Ya ce "Ina sake baki hakuri. Tunda wannan ne karon farko da ta kawo miki karata a zamanmu da ita. To ki yi mini uzziri a wannan karon . Ni kuma na miki alkawarin ba zata sake kawo miki karata akan wannan matsalar ba. Ki yi hakuri dan Allah".
Jikinta ya yi sanyi. Mussaman da ta zuba masa ido ta ga ya fada ya kuma birkice gabadaya.
Ya dinga magiya. Da ban baki tamkar zai rushe da kuka tsabar tsananta rokon da ya yi.
Rauni irin ma uwa ya shige ta. Ta furzar da iskar takaici. Ta ce "Ba dan ta yi hankalin tahowa nan ba. Da an yi ta yamididi da murnar ka yi kudi ka fara wulakanta ta. Da wanne idon zamu Kalli iyayenta da suka yi alkunya da kawaicin baka auren ta? Ta dinga yi masa fada da togaciya tamkar zata bige shi. Yayin da shi kuma yake fad'in "Ki yi hakuri zan Kiya ye da ikon Allah".
Ta tashi ta nufi daki. Ya yi maza ya mik'e ya bi bayan ta a d'arare tare da fargabar kada ta dakatar da shi.
Tana tsakiyar gadon. Yayin da Hamim yake kwance kan cinyarta. Hanif kuwa sarkin hakuri filo kawai ya yi da cinyar jikinsa na kan gadon. Daga ita har yaran kowa ya yi shiru tabbacin suna cikin alhini.
Baba ta sassauta murya ta ce "Yabi ga shi nan ku sasanta. Idan kin ga zaki yi hakuri ki bisu to, idan kuwa kin ga ba zaki bisu ba. Ba zan matsa miki ba. Ban san me kike hadiye wa ba".
Ya rasa inda zai tsoma ransa. Murya babu amo ya ce "Amma na baki hakuri fa".
"Dan ka bani hakuri sai na tirsasa ta?"
Ta jijjiga kai tabbacin ba zata mini dole ba.
Ya sassauta murya ya kalle ni ya ce "Asiya ki yi hakuri da abin ya faru. Na yi kuskure duk da dai fahimta ta ne baki yi ba".
Yana rufe baki na ce "Ba zan fahimta ba."
Babah ta yi shiru tana kallonmu. Watak'ila kuma mamakina ta yi na yadda na kame kamar ban gan shi ba tamkar ba yanzu na gama yin tijarar na huce ba ".
Ya munfasa ya ce "shi kenan ki yi hakuri." Ya furta a hankali.
Babah ta zame ta fice.
Yana ganin hakan ya matso kusa da ni ya zauna. Ya rage murya ainun ya ce "Saboda Allah little ya kamata ki bar dakin ki babu iznina?"
Na galla masa harara na dauke kai ban ce komai ba.
Ya sake tausasa harshe ya ce "Tashi mu tafi, idan mun je gida sai ki yi mini ko wanne irin darun ni kuma zan yi ta rarrashin ki, da kalolin soyayya masu tsayawa a rai."
Na ja tsaki tare da fad'in "Na bi soyayya da gudu. Ni yanzu bana son ka, kai ko ganin ka bana kaunar na bude ido na yi".
Ya saki ajiyar zuciya ya ce "Tom shi kenan, ki dawo dakinki dan yaran ki, ko ban ci arzikin komai ba ki dawo dan y'aya'n ki".
Na dauke kai na ce "Idan na mutu zasu fasa rayuwa ne?".
Ya rik'e kafata da tafi kusa da shi. Na goce da sauri. A tunzure na ce "Kada ka kuma tab'a ni. Ka je ka cigaba da damukar wadanda suke da daraja a wajen ka".
A zafafe ya ce "Na cigaba Asiya?".
Na dauke kai na ce "Eh".
Murya na rawa ya ce "Kin ga na damuk'e ta ne? Me yasa kike son jifa na da wannan mummunar maganar ne?"
Ba ja in ja na kalle shi na ce "Saboda ina da hujjoji na gaskiya. Sannan idan ba hakan ba, me yasa zaka kawo mini wannan suntumemiyar cikin gida? Har kuma kana kumfar bakin ba zaka ce ta tafi ba, saboda ta yi maka alkhairai. Fada mini alherorin da ta yi maka dan kuwa ban sansu ba".
Ya kafe ni da ido. Cikin matsanancin bacin rai ya ce "saboda kin fahimce ni a baibai shi yasa kika taho babu izinina, sannan kike kallon idona kike jifana da alamarin da kika san na tsani a jingina mini. Me yasa kike son ki dinga tayar mini da hankali ne Asiya?"
A tunzure na ce "Saboda ba ni da alheri a wajen ka sai sharri. Yanzu ba sai ka sakawa Nasiba da kalar naka alherin ba. Ni kuma ka bini da irin nawa sharrin ba".
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*