Sashe 106
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Na kwanta lamo. Ina kallon silin. Babah ta shigo yanayin da ta ganni a ciki sai ta yi turus. Ta iso ta zauna a gefen k'afafuwana. Ta sassauta murya ta ce "Nasan zaki so yaranki a tare da ke. Amma ki daure ba jimawa zaki yi ba. So nake ya rikice gaba'daya, ta yadda da kansa zai zo da bakinsa ya fa'da mini ba kya tare da su.
Har da ce mini wai kina gida zazzabi kike yi".
A hankali na ce "Idon Hamim ya yi ja?"
Ta galla mini harara ta mik'e ta na ce wa "Ban sani ba. Idan kuwa haka zaki mini, ki kuntata kanki sai ki zo ki bi bayansu kawai".
Ta fice tana ta sababin masifar son y'ay'a da iyayen yau suka mak'alawa zukatansu.
Da gaske dai mace tana saurin yin afuwa ga namiji a dalilin yaranta. Domin tun yanzu na fara kewarsu. So nake na bu'de ido na ga suna wasan hawa da sauka a jikina.
Na fesar da iskar damuwa. Na sani daga shi har yaran suna cikin kewata mai yawa. Barin ma sarkin kuka da k'ulafaci Hamim.
Haka na zauna, ina jin wani irin abu na bina.
**
Bulkachuwa kuwa da k'yar ya isa Bauchi domin ya shiga rudun inda zai ga Yabi. Ya kira wayarta yafi sau goma ana fa'da masa a kashe take. Amma ya kasa dainawa.
Suna isa gida, dakinta ya dire. Yaran da suka waiwaya basu ganta ba, suka dinga kuka a tare. Shi kansa ji yake tamkar ya bare baki ya tayasu. Gaba'daya azanjinsa ya k'are. Da k'yar ya shawo kansu suka yi shiru. Kwanaki biyu yana tiritiri da su. Sa'ar da ya yi ma ya riga ya saba da hidimarsu. Jiya a Toro suka yini, yana bulayin yiwa gidajen mutane dirar mikiya ko zai ga Yabi. Amma shiru tamkar Malam ya ci shirwa.
Komai ya tsaya masa cak. Kan dole ya sake komawa Bulkachuwa da su.
Ya rasa ta yadda zai fa'dawa Babah Yabi ta gudu ta barsu.
Ya gama kame kamensa ya fa'da mata gaskiya sun samu sabanin fahimta da Yabi ta yi yaji, ya kuma neme ta ya rasa tsawon kwanaki uku kenan.
Ta dauki salati mai tsananin gaske. Ta dake ta ce "Yarinyar da ubanta ya damka mini amanarta a hannuna ka yiwa sanadin da ta gudu ta fantsama duniya?"
Ya yi tsumu ya rasa me zai ce. Ta ce "Sai ka fa'da mini abin da ka shuka mata har ta kasa ha'diye wa ta bar maka wadannan yaran da suka shiga ranta. Ta tafa hannu tana skae kambaba girman lamarin. Fadi take yi "Duk uwar da tafi ta bar k'ananun y'ay'anta ai ba'kin cikin da take ha'diye wa ba ka'dan ba ne. Tura ce ta kai bango".
Ya kasa ce wa komai. Illah zufa da take yanko masa tamkar mai hadiyar kunama.
Cikin bacin rai ta ce "Ya ya ina magana ka mini shiru sai zare ido ka ke yi irin na rashin gaskiya".
Murya babu amo ya ce "Wallahi ba komai na yi mata ba. Nasiba ce ta zo shike nan ta kwarzabi kanta."
"Ta kwarzabi kanta kamar ya ya?"
Ta tambaya cikin wani irin yanayi na bacin rai mai yawa.
Ya numfasa ya ce "Ce wa ta yi sai na kore ta. Ni kuma na ce bazan kore ta ba. Shi kenan na dawo na tarar ta bar gidan".
Ta rausayar da kai ta ce "To ai Yabi
ta yi adalci. Sai da ta fa'da maka bata son zamanta. Kai kuma ka nuna kana da bu'katar ta zauna a gidan tunda naka ne. To mene ne kuma dan ta fita ta bar muku gidan ku tabbata a ciki?".
Ransa ya baci ainun. Ita ma bata fahimce shi ba. Su duk haka mata su ke da kishi ne?. Basa fahimtar komai matu'kar akan kishi ne.
A hankali ya ce "Yanzu dan Nasiba ta zo shi kenan sai ya zama masifa? Ta ce sai ta bar gidan? Duk zamanmu da ita bata gasgata ni ba ke nan? Ni ba kula ta nake yi ba, bare ta ce ta fahimci wani abu a tsakaninmu. Wallahi saboda sababin Yabi ko kallon inda ta ke bana yi. Amma hakan bai yi mata. Shin Nasiba ba zata zo gidana ba, ba yar'uwa ta ba ce?".
Babah ta girgiza kai ta ce "K'warai yar'uwar ka ce ta gaske tunda har ka zabi fishin matarka akan ta. Madallah da Yabi bata za'bi zaman muzanci ba. Ta daga hannuwanta sama ta ce "Allah kasa yarinyar nan tana hannu na gari. Allah kasa tana Kangire ko kaduna gidan Jabir".
Nan da nan ya muzanta. Ya kasa yin shiru ya ce "Kaduna! Ya fa'da cikin takaici mai yawa.
Ya kasa yin shiru da rawar murya ya ce "Na rantse idan aka same ta a Kaduna duk masifarta sai ta ga ne bata iya komai ba".
Ta galla masa harara ta ce "To me zaka yi ne? K'arshe dai ka sake ta. Ni kuwa Wallahi tana gama idda zan bada aurenta ga saurayi ma, don bazan yarda ta fita daga ahalina ba."
Idonsa ya kad'a ya yi jawur. Da rawar murya ya ce "Babah a gabana kike nuna zaki bawa k'anina auren matata?"
Ta bu'de murya ta ce "Na fa'da na ji ruruf!".
A matu'kar ki'dime ya ce "Allah ya huci zuciyarki. Allah ya tsare ni aikata irin wannan BAK'AR TA'ADA din".
Ya bata tausayi ainun. Amma ta cije ta ce "Akan idona uwar Nasiba ba abin da bata fa'da akan ka ba. Ita ta hana a baka aurenta saboda suna ganin ka baka da mamora. Amma Yaya Sani ya juyawa dukkan nak'asunka ya tursasawa Yabi auren ka sai kuma dan ka fara samun dama, ka fara shiga sahun mutane sai a yi maka shunen ta har cikin gidan Yabi! Ta yi shiru. Saboda yadda zuciyarta take jin tsananin zafin yadda aka tado mata tsumin bacin rai na tsawon lokaci.
Ta zuba masa ido wanda rabon da ta yi masa haka ya manta.
A kaurare ta ce "Nasiba ba matarka ba ce, ko bayan raina ba zata zama matarka ba. Shari'a ta halasta ka aure ta babu aibu a cikin hakan. Amma kuma shariar da kanta ta ce "ku girmama ra'ayin iyayenku sama da naku. Matu'kar ina da hak'ki akan ka Wallahi na haramta maka ita. Soko marar tunani. Har ka manta tozarcin da uwarta ta yi mini akan maganarku?"
Hankalinsa a matu'kar tashe ya ce ", Wallahi Tallahi ba ni da manufar komai akan ta. Dan Allah ku fahimce ni mana"
"An k'i a fahimce kan. Ban da sakarci me ya kai ka taho da ita tunda ga Toro har Bauchi ku ka'dai ka kawo ta gidan ka. Ai sai a rasa gane wace ce matar gidan tunda sai ta goyi Yabi da zani tsab. A kan wanne dalilin da ta ce ba zata zauna mata a gida ba, ka kafe sai ta zauna d'in? Ban da munafunci irin na ku na maza. Na gode wa Yabi da ta fahimci bata da daraja a wajen ka. Ta fice ta bar maka gidan".
Da rawar murya ya ce "Allah ya huci zuciyar ki. Na yi kuskure a yafe ni dan Allah. Tun ranar kuma Nasiba ta tafi, da kaina na ce tafi din"
Ta ja tsaki mai tsananin gaske tare da fad'in "Ta baya ta rago".
Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
✍️
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUN KI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES.*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.
Har da ce mini wai kina gida zazzabi kike yi".
A hankali na ce "Idon Hamim ya yi ja?"
Ta galla mini harara ta mik'e ta na ce wa "Ban sani ba. Idan kuwa haka zaki mini, ki kuntata kanki sai ki zo ki bi bayansu kawai".
Ta fice tana ta sababin masifar son y'ay'a da iyayen yau suka mak'alawa zukatansu.
Da gaske dai mace tana saurin yin afuwa ga namiji a dalilin yaranta. Domin tun yanzu na fara kewarsu. So nake na bu'de ido na ga suna wasan hawa da sauka a jikina.
Na fesar da iskar damuwa. Na sani daga shi har yaran suna cikin kewata mai yawa. Barin ma sarkin kuka da k'ulafaci Hamim.
Haka na zauna, ina jin wani irin abu na bina.
**
Bulkachuwa kuwa da k'yar ya isa Bauchi domin ya shiga rudun inda zai ga Yabi. Ya kira wayarta yafi sau goma ana fa'da masa a kashe take. Amma ya kasa dainawa.
Suna isa gida, dakinta ya dire. Yaran da suka waiwaya basu ganta ba, suka dinga kuka a tare. Shi kansa ji yake tamkar ya bare baki ya tayasu. Gaba'daya azanjinsa ya k'are. Da k'yar ya shawo kansu suka yi shiru. Kwanaki biyu yana tiritiri da su. Sa'ar da ya yi ma ya riga ya saba da hidimarsu. Jiya a Toro suka yini, yana bulayin yiwa gidajen mutane dirar mikiya ko zai ga Yabi. Amma shiru tamkar Malam ya ci shirwa.
Komai ya tsaya masa cak. Kan dole ya sake komawa Bulkachuwa da su.
Ya rasa ta yadda zai fa'dawa Babah Yabi ta gudu ta barsu.
Ya gama kame kamensa ya fa'da mata gaskiya sun samu sabanin fahimta da Yabi ta yi yaji, ya kuma neme ta ya rasa tsawon kwanaki uku kenan.
Ta dauki salati mai tsananin gaske. Ta dake ta ce "Yarinyar da ubanta ya damka mini amanarta a hannuna ka yiwa sanadin da ta gudu ta fantsama duniya?"
Ya yi tsumu ya rasa me zai ce. Ta ce "Sai ka fa'da mini abin da ka shuka mata har ta kasa ha'diye wa ta bar maka wadannan yaran da suka shiga ranta. Ta tafa hannu tana skae kambaba girman lamarin. Fadi take yi "Duk uwar da tafi ta bar k'ananun y'ay'anta ai ba'kin cikin da take ha'diye wa ba ka'dan ba ne. Tura ce ta kai bango".
Ya kasa ce wa komai. Illah zufa da take yanko masa tamkar mai hadiyar kunama.
Cikin bacin rai ta ce "Ya ya ina magana ka mini shiru sai zare ido ka ke yi irin na rashin gaskiya".
Murya babu amo ya ce "Wallahi ba komai na yi mata ba. Nasiba ce ta zo shike nan ta kwarzabi kanta."
"Ta kwarzabi kanta kamar ya ya?"
Ta tambaya cikin wani irin yanayi na bacin rai mai yawa.
Ya numfasa ya ce "Ce wa ta yi sai na kore ta. Ni kuma na ce bazan kore ta ba. Shi kenan na dawo na tarar ta bar gidan".
Ta rausayar da kai ta ce "To ai Yabi
ta yi adalci. Sai da ta fa'da maka bata son zamanta. Kai kuma ka nuna kana da bu'katar ta zauna a gidan tunda naka ne. To mene ne kuma dan ta fita ta bar muku gidan ku tabbata a ciki?".
Ransa ya baci ainun. Ita ma bata fahimce shi ba. Su duk haka mata su ke da kishi ne?. Basa fahimtar komai matu'kar akan kishi ne.
A hankali ya ce "Yanzu dan Nasiba ta zo shi kenan sai ya zama masifa? Ta ce sai ta bar gidan? Duk zamanmu da ita bata gasgata ni ba ke nan? Ni ba kula ta nake yi ba, bare ta ce ta fahimci wani abu a tsakaninmu. Wallahi saboda sababin Yabi ko kallon inda ta ke bana yi. Amma hakan bai yi mata. Shin Nasiba ba zata zo gidana ba, ba yar'uwa ta ba ce?".
Babah ta girgiza kai ta ce "K'warai yar'uwar ka ce ta gaske tunda har ka zabi fishin matarka akan ta. Madallah da Yabi bata za'bi zaman muzanci ba. Ta daga hannuwanta sama ta ce "Allah kasa yarinyar nan tana hannu na gari. Allah kasa tana Kangire ko kaduna gidan Jabir".
Nan da nan ya muzanta. Ya kasa yin shiru ya ce "Kaduna! Ya fa'da cikin takaici mai yawa.
Ya kasa yin shiru da rawar murya ya ce "Na rantse idan aka same ta a Kaduna duk masifarta sai ta ga ne bata iya komai ba".
Ta galla masa harara ta ce "To me zaka yi ne? K'arshe dai ka sake ta. Ni kuwa Wallahi tana gama idda zan bada aurenta ga saurayi ma, don bazan yarda ta fita daga ahalina ba."
Idonsa ya kad'a ya yi jawur. Da rawar murya ya ce "Babah a gabana kike nuna zaki bawa k'anina auren matata?"
Ta bu'de murya ta ce "Na fa'da na ji ruruf!".
A matu'kar ki'dime ya ce "Allah ya huci zuciyarki. Allah ya tsare ni aikata irin wannan BAK'AR TA'ADA din".
Ya bata tausayi ainun. Amma ta cije ta ce "Akan idona uwar Nasiba ba abin da bata fa'da akan ka ba. Ita ta hana a baka aurenta saboda suna ganin ka baka da mamora. Amma Yaya Sani ya juyawa dukkan nak'asunka ya tursasawa Yabi auren ka sai kuma dan ka fara samun dama, ka fara shiga sahun mutane sai a yi maka shunen ta har cikin gidan Yabi! Ta yi shiru. Saboda yadda zuciyarta take jin tsananin zafin yadda aka tado mata tsumin bacin rai na tsawon lokaci.
Ta zuba masa ido wanda rabon da ta yi masa haka ya manta.
A kaurare ta ce "Nasiba ba matarka ba ce, ko bayan raina ba zata zama matarka ba. Shari'a ta halasta ka aure ta babu aibu a cikin hakan. Amma kuma shariar da kanta ta ce "ku girmama ra'ayin iyayenku sama da naku. Matu'kar ina da hak'ki akan ka Wallahi na haramta maka ita. Soko marar tunani. Har ka manta tozarcin da uwarta ta yi mini akan maganarku?"
Hankalinsa a matu'kar tashe ya ce ", Wallahi Tallahi ba ni da manufar komai akan ta. Dan Allah ku fahimce ni mana"
"An k'i a fahimce kan. Ban da sakarci me ya kai ka taho da ita tunda ga Toro har Bauchi ku ka'dai ka kawo ta gidan ka. Ai sai a rasa gane wace ce matar gidan tunda sai ta goyi Yabi da zani tsab. A kan wanne dalilin da ta ce ba zata zauna mata a gida ba, ka kafe sai ta zauna d'in? Ban da munafunci irin na ku na maza. Na gode wa Yabi da ta fahimci bata da daraja a wajen ka. Ta fice ta bar maka gidan".
Da rawar murya ya ce "Allah ya huci zuciyar ki. Na yi kuskure a yafe ni dan Allah. Tun ranar kuma Nasiba ta tafi, da kaina na ce tafi din"
Ta ja tsaki mai tsananin gaske tare da fad'in "Ta baya ta rago".
Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
✍️
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUN KI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES.*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.