← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 100 OF 146

Sashe 100

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kwana biyu da komawa ta Muna ta barzar amarci. Yaran kuwa tamkar almara basa kuka. Da sun yi ka'dan suka sha nono sai su yi kwanciyarsu sai an idar da sallar asuba zasu farka.
Yana dawowa kuwa zai d'ora mana ruwan wanka. Da aka sa zai juyo, ya taya ni mu yi musu wanka.
Ni da kaina na tabbatar zai yi wahalar gaske a samu miji irin Bulkachuwa. Domin duk aiyukan gida ba zai zame masa komai ya yi ba.
Ina jin dadin Supplement din FASEELAT. Sun taimake ni wajen gyara mini ruwan nono da sake hade ni. .G H.T duniya ne na yarda *07039269802*.

Rainon yaran nan kuwa ba abin da ba ya yi. Kafin na yi musu hidima d'aya ya yi musu biyar. Ko pampars suka bata, ba ya jin komai zai cire ya wanke musu ya saka musu wani. Idan sun yi barci, sai kuma ya dawo yana tiritiri da ni.
Tun tafiyar tamu bata yi nisa ba na fara fa'din madallah da aurensa a zuciyata. Ban dai furta a fili ba ne.
Kwana duk da kuwa yana da na'kasu, sai dai alherinsa yafi tsiyatakum yawa.
Kwana biyar da komawa. Baba Lami ta zo daga kangire. Wacce matsayin kaka ce a wajena. Tunda k'anwar mahaifiyar Gwaggo ce uwa daya uba daya.
Ranar da ta zo, a ranar ya koma Bauchi.
Cikin sau'ki da rangwame nake rainon yan biyu. Basu da fitina. Sannan Baba lami mace ce mai kazar kazar ainun. Abin da nake yi ka'dan ne. Watana biyu da haihuwa na koma kan sana'a ta.
A hankali kuma Tijjani yana samun rufin asiri a zamansa a baucy. Tunda abinci dai baya yanke mana. Iyakar kokarin jarfinsa yana yi. Duk sati zai taho musu da Pampers. Ni kuwa kayan shayi duk sati ne. Idan na ce "Basu kare ba".
Ya dinga fa'da akan me bazan dinga shan shayi mai kauri ba, alhalin ina shayar da yara har biyu. Ga su nan su sun yi girma ni kuma na sake zuke wa.
Watarana Baba lami ta ce masa ba rashin cin abinci ba ne, wasu matan idan suna shayarwa hakan suke yi. Sai sun ya ye sannan su yi kumari.
Baba Lami bata tafi ba sai da muka kwashe watanni kusan biyar a tare. Lokacin su Hanif na da watanni shida.
Muka ha'da mata alheri sosai. Sannan suka tafi da Gwaggo da Yaya Ummi bikin da za'a yi a can Kangire. Na so zuwa, amma ya yi mirsisi ya hana.
Sannu a hankali muke rayuwa, bamu cika samun matsala ba, tunda kwanakin da yake yi a Bauchi sun fi wanda yake yi a Toro.
Kullum idan ya dawo sai ya ce "ki tsananta yimini addu'a little. Mahassada sun kewaye ni a kasuwar nan. Ga shi an rasa gane inda matsalar take kullum Alhajin da muke wajensa sai karayar arziki ya ke samu.
Ina jin tsoro k'warai da gaske.
Cikin tausayi na ke kwantar masa da hankali da kalamai masu taushi.
Wani zuwa da ya yi, ya ce "mu
shirya zai kai mu Bulkachuwa mu yi sati.
Na dinga murna domin rabona da zuwa tun kafin na haihu. Ga shi yazu watannin su tara har sun fara tsayawa. A yanzu kam na gasgata kama suke yi da Bulkachuwa. Domin suma haka suke dogaye, masu gaba manya. Ba wanda zai ce ni ce uwarsu. Domin manya ne sosai, sannan ni yar tsurut ce sosai. Kawai faratuna suka diba, da kuma yan k'ananun kamanni. Amma kammanin ubansu yafi yawa a tare da su. Tun yanzun kuma halayyarsu ta banbanta. Haneef mai sanyi da hakuri ne. Sai ya yini baka ji kukansa ba. Kafin ya nemi nono sau daya Hamim ya nema sau uku.
Zai yi wahalar gaske ya damuki d'anuwansa yasa shi kuka. Amma Hamim kullum cikin nukurkusrsa yake.
Ga shi da shegiyar kiwa. Ko wajen Babansu sai ya akan dole yake zuwa. Ko idan ya ga ya dauki Hanif zasu fita.
Shi dai kullum yana jikina. Ko k'unshi zan yi, sai dai na ha'da masa kayan wasa a kusa da ni.
Ko ya ce ",sai na goye shi.
Sabanin Hanif da ba ya yin kiwa. Kowa ya mika masa hannu zuwa yake yi.
Shiyasa ma na fi kai shi gidan Yaya Ummi ya yini tunda yanzu ba ni da nisa da ita.
Kullum Bulkachuwa sai ya ce halina ya kwaso. Domin mafad'aci ne na gaske, ga kuka. Idan ina mita akan halinsa Gwaggo ma ce wa take yi hakan na yi mata. Haka ta sha fama a goyona. Bana yarda a dauke ni. Ko band'aki zata shiga sai an yi artabu da ni.
Da yammaci muka isa Bulkachuwa. Babah sai ina ka saka take yi da ni da yara. Komai ta mika hannu a kai sai ta dauko ta ajiye a gabana. Yara kuwa kayan wasa sabbi sun fi kala uku tamkar dama a wajenta suke. Na kasa ha'kuri na ce "Babah wadanda kayan wasan fa?". Domin ihisan ba a garin take ba. A cikin Bauchi take bari na yi zaton na yaranta ne.
Da walwala ta ce "Tunda ya ce zaku zo na siya musu, tunda na ga mai sunan yayan nawa rigimamme ne. Shi dai bai kwaso halin mai sunansa ba. Hanif ne ya kwaso halin mai sunansa."
Nasir da yake gefe ya ce "Su Babah ana yabon sunan masoyi".
Ya bani dariya na rufe fuskata na dinga yinta. Ta mike sabe da Hanif tana fa'din ja'iran yara bari na baku waje.
Shi dai Tijjani bai ce komai ba. Asalima matse wa ya yi ko dariyar bai yi ba.
Kwana biyu ya yi, ya barmu ya wuce Bauchi.
Bayan dakina da na Gwaggo ba inda nake samun natsuwa irin a dakin Babah. Domin wata irin mua'amala take yi da ni mai dadi da tattali. Bata taba nuna surukunta a tsakaninmu ba. Sai ni ce ma nake jin kunyar yin wasu abubuwan a gabanta. Ita kuwa da taga hakan zata balbale ni da fa'da tana fa'din bata son rashin kunya. Har yaushe na zama matar tasa da zan ture ta a uwa na mata kallon suruka. Na sake na yi komai yadda nake so kamar yadda nake yi tuntuni.
Da kanta ta dafa mini kazar da na tabbatar ta mata ce. Kunya ta kama ni. Ita kuwa fadi take ci ki sha romon. Tun lokacin haihuwar na siya na dauka zaku zo yawon arba'in. Tunda baku zo ba. Na ajiye nasan a can ma za'a gyara ki."
Na rasa yadda zan yi, ita kuwa ko a jikinta.
Ranar da Bulkachuwa ya dawo. Da daddare an hadu a falonta ana ta hira cikin walwala ya kutso da maganar yana son mu koma Bauchi gaba'daya.
Ta ce "ka dai kafe. Yanzu kam tunda yaranta sun yi k'wari ba zan hana ba. Allah ya bada sa'a.
Dama har da tunanin yadda sana'ar ta zata durk'ushe ne. Amma In sha Allah a can din ma sannu a hankali za'a santa."
Ni kuma sai kawo masa abinci abubuwa nake yi. Gaba'daya na kasa sukuni. Babah da kanta ta gane yanzu kam sonsa nake yi da dukkan zuciyata.
Washagari ana zaune bayan mun karya. Sai kawai ya kalle ni ya ce "A irin wannan ranar ta shekaru uku baya kika zo har nan kika ce ba kya sona Asiya".
Nan da nan na ji tamkar k'asa ta tsage na shige. Kunya ta rufar mini. Na rasa yadda zan yi. Sai kawai na fara kuka ina ce wa "Idan juninka tashin tashina ne, da son sai ka kunyata ni, to ni ba damuwa zan yi ba, kai ne zaka ji kunya Wallahi".
Nasiru ma cikin dariya ya ce "Ai kuwa nima na tuna yawun da kika kwalbana masa a fuskarsa. Yau kuwa sai faman girmama lamarinsa kike yi".
Na sake rushe wa da kuka ina ce wa "Ai kai dama baka fa'din gaskiya".
Babah ta ce "Yo ni ke kika fi ba ni haushi, to kukan na mene ne? Ware wa zaki yi ai ku yaga, suma ki nutsu ki fadi irin nasu al'amarin da baza su so a taso musu shi ba."
"Nasiru ya ce "Ni dai babu abin da zata fa'da a kaina, sai dai ko akan mijinta".
Tijjani dai tunda ya kunyata ni bai sake ce wa ba.
Jimawa ka'dan Babah ta mike ta shiga cikin gida.
Nasiru ma ya mike yana ce wa "Hajiya Yabi bari na fece tun Babah bata zo ta fa'da miki wani abu a kaina ba."
Ko kula shi ban yi ba.
Yana fita na kalli Tijjani na ce "Na gode sosai Baban 2"
Ya yi murmushi ya ce "wannan godiyar fa! Ta mece ce?"
Na matso hawaye na ce ",Na gode da kunyata ni da ka yi, na gode da wannan sakayyar".
Ya dara ka'dan ya ce ",Kin san na fa'da miki lokaci zai zo da zaki ji kunyar abin da kika yi".
A hassale na ce ",To mene ne zaka tayar a gabanta? Gaskiya kada ka sake yi mini irin haka. Idan kuwa ba hakan ba kasan kai ma ka mini laifin da ban ta'ba bude wa an ji ba".
Nan da nan ya shiga nutsuwarsa ya ce "Ai ni ba da bacin rai na fa'di hakan ba. Amma ba zan sake ba, mu rufe maganar haka nan.
Na girgiza kai na juyar da fuskata gefe. Ya shiga kiran sunana a hankali, na ki juyowa. Ya diririce. Ya ce "Asiya wasa fa nake yi miki. Me zai sa
mu yi fa'da a gaban Babah".
Na ce "Ai so kake ka bakanta ni a wajen ta, shi yasa ka dauko wannan maganar".
Ya marairaice ya ce "Billahillazi ba hakan ba ne. Gaba'daya ya rikice jin na lauya magana zan tado da tashin hankali.
Ya dinga lallaba ni da son sai na dawo da walwala ta.
Ni kuma ina sane na yi masa hakan.
Bamu bar garin Bulkachuwa ba sai da muka shafe sati biyu.
Da zamu tafi, tamkar wanda muka je fatauci saboda kayan da muka samu.
Lafiya k'alau muka isa Toro. Kwana biyu a tsakani ya koma Bauchi.
Kwatsam aka tashi da mutuwar mijin Nasiba. Wannan mutuwa ta bigemu, domin babu jinya sai mutuwa. Ashe kasurgumin dan shaye shaye ne. Can wajen sharholiyarsu rikici ya kaure tsakaninsa da abokinsa ai kuwa ya daba masa kwalbar a kahon zuci ya mutu a wajen nan take.
Gaba'daya maganar ta cika Toro da kewaye.
Na tausayawa Nasiba kwarai da gaske, duk da dama ba zaman dadi take yi da shi ba. Duk cikinmu ita ce bata samu sukuni a gidan aurenta ba. Yaranta biyu Muhsin, da kuma Maryam da bata fi watanni shida da haihuwa ba.
Chapter 100 · 0% Book details