Sashe 18
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko kuma kina sha'awar yin register da su. Ki tuntubi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn mai kore dukkan kwadayi*.
*07036662633*.
Gwaggo ta ce "Dutse a tsakaninmu da duk masu wannan al'amarin, muna neman tsarin Allah da su, muna kuma nema musu shiriyarsa."
Ta ce "ASMA'U Wallahi kin siffatu da agwagwa, ace wai baki isa ki sarrafa y'ar cikinki ba, ta gallabi kowa a gidan amma ba k'ya yi mata fa'da, saboda tana samun ku'di shiyasa ta gagareku?
Sai ayi ta fankamar ku'din kitso da na lalle ne, alhalin munsan samarin da suke mata layi ne suke bata. Wallahi idan ba sa'a kika yi ba sai Yabi ta hana ki shan ruwa kamar yadda ta fitine mu".
Na fito na ce "Umma ya isa haka nan, ba zai yiwu fa kizo k'ofarmu ki zagi Gwaggo ba".
Ta mini dakuwa ta ce gidanku tabbataciyar yarinya marar albarka".
Tana rufe baki na ce "yarinya tana bayan uwarta Wallahi, albarka kuwa da ikon Ubangiji sai na yi ta".
Gwaggo ta yo kaina na ki guduwa tasan kuma matu'kar ta kawo mini duka ban gudu ba, na riga na shiga yanayin da nake bu'katar a kashe ni kawai na huta.
Inna ta yi maza ta karbe itacen hannun Gwaggo tana fa'din "Wannan ai sai ki sabauta ta".
Yayin da Umma Abu ta juya tana fa'din "Zaman babban gida ko masifa, ba dama a ganka da haske sai an tisa ka a gaba da ba'kin ciki da hassada tamkar dai kai ofne ka tare wa mutum nasa arzikin".
Tana fita Gwaggo ta kalli inda nake a tsaye kik'am tana fa'din "Kin ji da'di ai da wannan wula'kancin da kika janyo mana".
Ban ce komai ba, sannan kuma ban ji a raina cewar zan koyi ha'kurin dole idan an ta'ba ni ba.
Wannan rikicin yana cikin al'amura masu tsananin gaske da ya faru.
Domin da daddare babu kunya bare kawaici Baban kasuwa ya gurfanar da mahaifina a gaban Dada yana ta sababin ya gaji da yadda na takura wa ya'yansa amma ubana ya kasa tsawatarwa.
Da yake Dada bata iya tsallake umarninsa sai kuwa tabi bayansa.
Ta dinga fa'din ai tsoron zuciyata yake yi.
Cikin rishin kuka Baban kasuwa ya ce "Ki gafarce ni Dada! Wani satin zan koma gidana dana kammala gina wa tun bara, amma na kasa tashi saboda ke, to yanzu kam zan tashi na gaji da wannan masifar Wallahi".
Dada ta ce "Wallahi ko ubanta ba zai tashe ka ba tunda matsayinku guda a cikin gidan bare kuma ita.
Share hawayenka ita ce zata bar mini gidan".
Na sake kasa kunne domin tunda aka aiko cewar Babanmu ya zo in ji Dada nasan karata za'a kai sai na bi bayansa ba tare da yasan ina binsa ba.
Na makale a soron Dada ina addu'ar kada Allah ya kawo Bulkachuwa tunda dakinsa a cikin soron yake.
Ta ce "ka fa'dawa Yabi ta tsayar da miji da dukkan yaran ma.
Na umarce ku, ku aurar da su nan da watanni biyu".
Baban kasuwa ya ce "Shi kenan"
Ya fice ya barta da Babanmu."
Ganin zai fito ya gan ni sai na yi maza na fice daga soron na tsaya a bakin k'ofar shashinmu.
Ya zo wuce wa ya dallaro mini ido da sabuwar tocilayit dinsa da alamu suka nuna yau ya zuba mata sabbin batira saboda tsananin hasken ta.
Na dauke kai tare da saka hannunwana na rufe fuskata dan rage wa kaina kaifin hasken da ya dauke mini ido.
Takaicin rashin gaishe shi ya sanya ya ce "Asiya ce?"
Na dauke kai a shak'e na ce "Yabi ce?"
Ya kuwa bu'de murya ya ce "Ja'irar yarinya mai mugun y'anci dama nasan ke ce zaki gan ni ki mini irin wannan iyashegen. Na ce ba, zaki yiwa ubanki Sani hakan?"
Na dauke kai ina kunkunin fa'din "Ai kai ma ba zaka yiwa su Maijidda irin hakan ba".
"Me kika ce? Bude Baki sosai ki fa'di abin da kike ce wa shedaniya."
Ganin Baban Tsakiya dawo ya nufo mu dan ya shiga wajensa ya sanya Baban kasuwa ya d'auki k'arfaffan salati.
Ganinmu hakan ya sanya Baban Tsakiya ya dakata ya ce "ya ya ne Iliya?"
Ai kuwa ya hau rattab'a masa bayanin da aka yi masa na karya akan fad'anmu da Maijidda.
Wani abin mamaki a gabana ya lauya zance yana fa'din a gabansa ma, na zage shi yanzu nan. Da kunnensa ya ji ina zaginsa.
Baban Tsakiya yana bu'de baki sai ce wa ya yi "Tuni fa na d'iga alamar tambaya akan yarinyar nan domin wacce ta saba cudanya da maza ne take irin wannan dibar albarka."
Gabana ya yanke ya fa'di wacce irin magana ce mai muni ta fito a bakin kanin mahaifina kuma uban wanda nake burin aure?"
Na yunkura da nufin mayar masa da zazzafar magana sai kuma na tuna girman aika aikar da zan janyo wa kaina da uwata.
Na sani mahaifina ba zai d'auki al'amarin da sauki ba, domin kuwa zai ce tunda na iya zagin dan-uwansa shima zan zage shi, hukuncin da zai biyo baya kuwa na tabbatar zai zama mai tsananin gaske.
Na ha'diye maganar na juya na tafi na barsu dan kada na yi subutul kalam.
Sai na sake juyo muryar Baban kasuwa yana sake cewa "Na kagu a samu mai tsautsayin daukar kara da kiyashi ya zo ya kwashe ta, ko zamu sarara da musibarta domin ta riga ta zame mana tamkar annoba" .
Baban Tsakiya ya ce "Lallai kuwa kara da kiyashi daukar marar sani, na tausaya wa ahalin gidan Sarkin gida q tunda ina ganin d'ansu a wajenta"
"To namu d'an fa? In ji Baban kasuwa.
Baban Tsakiya ya yi wata irin dariya ya ce "Ta yaro ai kyau take yi bata k'arko, yaushe kana ganin kashi a jikin mutum, za kuma ka yi kuskuren bari naka ya dauki abin nan?"
Kai-tsaye dakin Gwaggo na fa'da na zauna akan tabarmar da take shinfide, yayin da take zaune gefe daya, yanayinta ya nuna a takure take ma'ana tana cikin zullumin kiran da aka yiwa Babanmu me zai haifar mata.
Na sassauta murya na ce "Gwaggo ki yi ha'kuri dan Allah"
Ta muskuta ta ce "Idan ban yi ha'kuri ba ya ya zan yi ne Yabi?
Ai a gabanki aka tabbatar mini ni agwagwa ce akan ki.
Kinsan me hakan yake nufi kuwa?"
Manufa kina gaba ina bin ki a baya, saboda gudun zuciyarki da nake yi.
Ace yanzu kullum a cikin d'aukar wa kanki baki kike, sai ka ce ke kad'ai ce a gidan?
Ga yar'uwarki nan ban ta'ba jin an kawo togaciyar Nazira ba.
Amma ke idan ba'a kawo k'ararki ba, sai idan baki fita ba, ko kuma kin ha'du da masu alkunya, anya Yabi kina ganin kin hau turba mai b'ille wa?
Jikina ya yi sanyi sosai na ce "Duk fa'dan da nake yi kowanne takala ta ake yi, ba wanda nake yin sa na rashin gaskiya, amma ki yi ha'kuri zan yi kokarin koyo ha'kuri idan an nemi ganin rikicina".
Ta kafe ni da ido tana cewa "koya ma zaki yi Yabi?
To fa'da mini zuwa yaushe zaki fara bita?"
Na yi kasa da kaina na ce "Addu'a zaki tsananta yi mini a sanya ni cikin bayi masu ha'kuri da kawaicin cutarwar mutane. Amma a zahiri saboda ke zan yarda na zama mai kawaicin tunda abin da kike so ke nan.
Domin ni dai har yau ban ga ranar da ha'kurinki ya miki ba, ban ga kuma ranar da kawaicin Babanmu yayi masa ba, tunda yau an kai dan-uwansa ne mai kirana da lalatacciya mai bin maza".
Na fa'da hawaye na kwace mini ba tare da na shirya zubarsu ba.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
*VIP 1k, regular 500.*
*2384876855*
*Surayya Ibrahim*
*Zenith Bank.*
*Shaidar biya ta*
*08032773332.*
*BAK'AR TA'ADA*
*NA*
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*
*(MRS M.I.NASHE)*.
*Marubuciyar*
*Halin Yau*
*Sabo da kaza*.
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
11&12.
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn mai kore dukkan kwadayi*.
*07036662633*.
Gwaggo ta ce "Dutse a tsakaninmu da duk masu wannan al'amarin, muna neman tsarin Allah da su, muna kuma nema musu shiriyarsa."
Ta ce "ASMA'U Wallahi kin siffatu da agwagwa, ace wai baki isa ki sarrafa y'ar cikinki ba, ta gallabi kowa a gidan amma ba k'ya yi mata fa'da, saboda tana samun ku'di shiyasa ta gagareku?
Sai ayi ta fankamar ku'din kitso da na lalle ne, alhalin munsan samarin da suke mata layi ne suke bata. Wallahi idan ba sa'a kika yi ba sai Yabi ta hana ki shan ruwa kamar yadda ta fitine mu".
Na fito na ce "Umma ya isa haka nan, ba zai yiwu fa kizo k'ofarmu ki zagi Gwaggo ba".
Ta mini dakuwa ta ce gidanku tabbataciyar yarinya marar albarka".
Tana rufe baki na ce "yarinya tana bayan uwarta Wallahi, albarka kuwa da ikon Ubangiji sai na yi ta".
Gwaggo ta yo kaina na ki guduwa tasan kuma matu'kar ta kawo mini duka ban gudu ba, na riga na shiga yanayin da nake bu'katar a kashe ni kawai na huta.
Inna ta yi maza ta karbe itacen hannun Gwaggo tana fa'din "Wannan ai sai ki sabauta ta".
Yayin da Umma Abu ta juya tana fa'din "Zaman babban gida ko masifa, ba dama a ganka da haske sai an tisa ka a gaba da ba'kin ciki da hassada tamkar dai kai ofne ka tare wa mutum nasa arzikin".
Tana fita Gwaggo ta kalli inda nake a tsaye kik'am tana fa'din "Kin ji da'di ai da wannan wula'kancin da kika janyo mana".
Ban ce komai ba, sannan kuma ban ji a raina cewar zan koyi ha'kurin dole idan an ta'ba ni ba.
Wannan rikicin yana cikin al'amura masu tsananin gaske da ya faru.
Domin da daddare babu kunya bare kawaici Baban kasuwa ya gurfanar da mahaifina a gaban Dada yana ta sababin ya gaji da yadda na takura wa ya'yansa amma ubana ya kasa tsawatarwa.
Da yake Dada bata iya tsallake umarninsa sai kuwa tabi bayansa.
Ta dinga fa'din ai tsoron zuciyata yake yi.
Cikin rishin kuka Baban kasuwa ya ce "Ki gafarce ni Dada! Wani satin zan koma gidana dana kammala gina wa tun bara, amma na kasa tashi saboda ke, to yanzu kam zan tashi na gaji da wannan masifar Wallahi".
Dada ta ce "Wallahi ko ubanta ba zai tashe ka ba tunda matsayinku guda a cikin gidan bare kuma ita.
Share hawayenka ita ce zata bar mini gidan".
Na sake kasa kunne domin tunda aka aiko cewar Babanmu ya zo in ji Dada nasan karata za'a kai sai na bi bayansa ba tare da yasan ina binsa ba.
Na makale a soron Dada ina addu'ar kada Allah ya kawo Bulkachuwa tunda dakinsa a cikin soron yake.
Ta ce "ka fa'dawa Yabi ta tsayar da miji da dukkan yaran ma.
Na umarce ku, ku aurar da su nan da watanni biyu".
Baban kasuwa ya ce "Shi kenan"
Ya fice ya barta da Babanmu."
Ganin zai fito ya gan ni sai na yi maza na fice daga soron na tsaya a bakin k'ofar shashinmu.
Ya zo wuce wa ya dallaro mini ido da sabuwar tocilayit dinsa da alamu suka nuna yau ya zuba mata sabbin batira saboda tsananin hasken ta.
Na dauke kai tare da saka hannunwana na rufe fuskata dan rage wa kaina kaifin hasken da ya dauke mini ido.
Takaicin rashin gaishe shi ya sanya ya ce "Asiya ce?"
Na dauke kai a shak'e na ce "Yabi ce?"
Ya kuwa bu'de murya ya ce "Ja'irar yarinya mai mugun y'anci dama nasan ke ce zaki gan ni ki mini irin wannan iyashegen. Na ce ba, zaki yiwa ubanki Sani hakan?"
Na dauke kai ina kunkunin fa'din "Ai kai ma ba zaka yiwa su Maijidda irin hakan ba".
"Me kika ce? Bude Baki sosai ki fa'di abin da kike ce wa shedaniya."
Ganin Baban Tsakiya dawo ya nufo mu dan ya shiga wajensa ya sanya Baban kasuwa ya d'auki k'arfaffan salati.
Ganinmu hakan ya sanya Baban Tsakiya ya dakata ya ce "ya ya ne Iliya?"
Ai kuwa ya hau rattab'a masa bayanin da aka yi masa na karya akan fad'anmu da Maijidda.
Wani abin mamaki a gabana ya lauya zance yana fa'din a gabansa ma, na zage shi yanzu nan. Da kunnensa ya ji ina zaginsa.
Baban Tsakiya yana bu'de baki sai ce wa ya yi "Tuni fa na d'iga alamar tambaya akan yarinyar nan domin wacce ta saba cudanya da maza ne take irin wannan dibar albarka."
Gabana ya yanke ya fa'di wacce irin magana ce mai muni ta fito a bakin kanin mahaifina kuma uban wanda nake burin aure?"
Na yunkura da nufin mayar masa da zazzafar magana sai kuma na tuna girman aika aikar da zan janyo wa kaina da uwata.
Na sani mahaifina ba zai d'auki al'amarin da sauki ba, domin kuwa zai ce tunda na iya zagin dan-uwansa shima zan zage shi, hukuncin da zai biyo baya kuwa na tabbatar zai zama mai tsananin gaske.
Na ha'diye maganar na juya na tafi na barsu dan kada na yi subutul kalam.
Sai na sake juyo muryar Baban kasuwa yana sake cewa "Na kagu a samu mai tsautsayin daukar kara da kiyashi ya zo ya kwashe ta, ko zamu sarara da musibarta domin ta riga ta zame mana tamkar annoba" .
Baban Tsakiya ya ce "Lallai kuwa kara da kiyashi daukar marar sani, na tausaya wa ahalin gidan Sarkin gida q tunda ina ganin d'ansu a wajenta"
"To namu d'an fa? In ji Baban kasuwa.
Baban Tsakiya ya yi wata irin dariya ya ce "Ta yaro ai kyau take yi bata k'arko, yaushe kana ganin kashi a jikin mutum, za kuma ka yi kuskuren bari naka ya dauki abin nan?"
Kai-tsaye dakin Gwaggo na fa'da na zauna akan tabarmar da take shinfide, yayin da take zaune gefe daya, yanayinta ya nuna a takure take ma'ana tana cikin zullumin kiran da aka yiwa Babanmu me zai haifar mata.
Na sassauta murya na ce "Gwaggo ki yi ha'kuri dan Allah"
Ta muskuta ta ce "Idan ban yi ha'kuri ba ya ya zan yi ne Yabi?
Ai a gabanki aka tabbatar mini ni agwagwa ce akan ki.
Kinsan me hakan yake nufi kuwa?"
Manufa kina gaba ina bin ki a baya, saboda gudun zuciyarki da nake yi.
Ace yanzu kullum a cikin d'aukar wa kanki baki kike, sai ka ce ke kad'ai ce a gidan?
Ga yar'uwarki nan ban ta'ba jin an kawo togaciyar Nazira ba.
Amma ke idan ba'a kawo k'ararki ba, sai idan baki fita ba, ko kuma kin ha'du da masu alkunya, anya Yabi kina ganin kin hau turba mai b'ille wa?
Jikina ya yi sanyi sosai na ce "Duk fa'dan da nake yi kowanne takala ta ake yi, ba wanda nake yin sa na rashin gaskiya, amma ki yi ha'kuri zan yi kokarin koyo ha'kuri idan an nemi ganin rikicina".
Ta kafe ni da ido tana cewa "koya ma zaki yi Yabi?
To fa'da mini zuwa yaushe zaki fara bita?"
Na yi kasa da kaina na ce "Addu'a zaki tsananta yi mini a sanya ni cikin bayi masu ha'kuri da kawaicin cutarwar mutane. Amma a zahiri saboda ke zan yarda na zama mai kawaicin tunda abin da kike so ke nan.
Domin ni dai har yau ban ga ranar da ha'kurinki ya miki ba, ban ga kuma ranar da kawaicin Babanmu yayi masa ba, tunda yau an kai dan-uwansa ne mai kirana da lalatacciya mai bin maza".
Na fa'da hawaye na kwace mini ba tare da na shirya zubarsu ba.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
*VIP 1k, regular 500.*
*2384876855*
*Surayya Ibrahim*
*Zenith Bank.*
*Shaidar biya ta*
*08032773332.*
*BAK'AR TA'ADA*
*NA*
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*
*(MRS M.I.NASHE)*.
*Marubuciyar*
*Halin Yau*
*Sabo da kaza*.
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
11&12.