← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 122 OF 146

Sashe 122

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bamu yi mamakin furucinsa ba domin tamkar dan kama haka Hamim ya ke da magana. Ga kafirin wayo tamkar ya shekara goma.
A sanyaye Tijjani ya jasu jikinsa dukkansu. Yana gode wa Yabi a zuciyarsa da ta rufe masa k'ofar da y'aya'nsa zasu tsane shi. Domin ya riga ya gane Hamim, ba abin da yake so a duniya sama da Yabi. Hanif ne ba shi da alkibla, bai san wa ya fi so a tsakaninsa da ita ba.
Sosai ya tisa mu gaba a da tarairaiya. Rabon da ya yi mini hakan na manta. Gara yara yana ta tasu ni ce dai babu dad'i a tsananinmu. Da wuri ya sa suka kwanta. Suna yin barci kuwa ya ja ni dakinsa. Bamu samu kanmu ba sai tsakiyar dare. Mun tabbatar mun yi kewar junanmu. Haduwar kuma ta yi awon gaba da wani kason bacin ran da ke zukatanmu.
Barci na shirin daukemu ya yi azama ya ce "Mu tashi mu kai kukanmu gun Allah. Ya taimake mu ya kawo mana mafita ya kuma yi mana maganin duk abin da zai farrak'amu". Duk yadda na gaji tikis. Haka na daure na yi wanka, na bishi sallar da ya tayar muka dinga yi har sai da lokacin asuba ya yi.
Kwanakin da suka biyo baya na samu sassauci domin ya yi matukar rage kyara ta. Sannan ya daina fita ya shafe lokaci yna waya a waje. Watak'ila yana yi ne kafin ya shigo.
**
Tunda Babah ta koma Bulkachuwa ta shiga damuwar halin da ta baro d'an uwanta, mahaifin Yabi. Sannan ta shiga alhinin yadda ake ta shirin bikin Tijjani da a Nasiba babu nadamar komai a gidan Marina.
Ta kasa gane kanta sai kawai ta durfafi addu'a tare da fatan Ubangiji ya warware dukkan abin da babu alheri.
Kwanaki biyu kullum sai ta yi mafarkin wai randar Dada ta sanyi akwai maciji mai dafi a ciki.
Kwanaki biyu a jere tana wannan farkin babu tsagaitawa. Tun bata tunawa har ya fara shiga ranta mussaman da take ganin macijin na yunkurin fitowa ya hallaka Dada.
Ta kasa katabus ta fara kokwanto akan lamarin.
Yayin da ya rage saura sati uku biki. Baban Marina ya mik'e ya fara samun sauki a dalilin yadda Yabi ta kwantar da hankalinta. Takanas ta zo har Toro ta bashi tabbacin zata jure matukar ba Tijjani ne ya sake ta ba, to zata yi dukkan iyawarta ta tsallake dukkan kalubalen da yake gabanta. Murya na rawa ta ce ",Ya kamata ka huta Baba. Ya kamata ka samu nutsuwa, sannan mune zamu yi gwagwarmaya mu tsaywa kanmu. Ranar da babu kai kuma waye zai tare mini fad'a ko ya tsaya mini? Bini da addu'a kawai, na karbi wannan kaddarar da dukkan zuciyata, Allah yasa abokiyar arziki ce".
Ya d'ora hannunsa a kaina ya ce "Ina alfahari da haihuwar ki Yabi. Ina samun nutsuwa saboda Ubangiji ya azurta ni da haihuwar ki. Da ikon Allah duk abin da kika saka a gaba na alheri sai kin ga fatahi a cikinsa. Allah ya shirya miki yaranki, Allah ya hore miki mijinki. Ya miki shamaki da dukkan abin da zai cutar da ke, ko ya gigita miki kwanciyar hankalinki".
Cikin jarumta na ce "Ameen na gode Baba".
**
Mafarkin maciji a randar Dada sai idan bata kwnata barci ba. Kan dole ta shirya ta tafi Toro, a lokacin sati biyu ya rage daurin aurensu Nasiba.
Sai didima ake yi tare da kambaba lamarin. Masu adawa da Yabi suna fad'in "Duk d'aya ne to wa za'a ki a tsakaninsu? Tare da fake wa da ce wa rabon aure ai kisa yake yi, gara a yi, kowa rabon ta zata samu".
A wannan tsukun na gasgata k'arfin jini domin hatta su Yaya Indo da suke mana yan'ubanci na gaske sun kaurace wa shiga shirgin auren ko taya masu adawa kanzagi da nuna kowa nasa ne a tsakaninmu. Kafatalin y'an k'ofarmu sun kame daga shiga cikin maganar auren gabadaya. Sun janye jikinsu sai isu isu. Ai kuwa mutanan gidan suka yi ca wajen sakin maganganun tare da ce wa "Kamar gaske. Su a tsakaninsu ma suke son ganin wani a uku shine yanzu zasu nuna mana an tab'asu? Suka dinga furzar da maganganun da su Yaya Indo suke fad'a akanmu a baya. Yaya Ummi kuwa ta k'i yarda da yadda ake son a sake gwara kansu. Tunda yawanci a kanta suke gulmar sai kuwa ni da na ke cikin rufin asiri. Suke taya masu yamididin duk abin da aka gani a jikina ni nake yiwa kaina. Da kuma ce wa duk k'afafar da nake yi bana gaban Tijjani domin har yau bai bar iskancin kule kulen mata ba.
Na ka'du k'warai da Nazira take mayar mini wadannan maganganun da ake ta fitowa da su tare da ce wa a bakin su Yaya Indo aka fara ji. Amma yanzu sun fitittke wai suna kishin kanwarsu sai ka ce gaske.
***
Babah sai dube dube take yi a tsakanin randunar Dada amma bata ga komai ba.
Ta kasa samun nutsuwa. Rashin ganin macijin, ga shi bata daina ganisa a mafarkinta ba. A yanzu al'amarin ma yafi ta'azzara ko barcin rana ta yi sai ta ga ni.
Tana zaune a gefen randar Aliyu ya k'ira ta a waya wanda a yanzu likita ne a F.M.C Azare.
Cikin rauni ya ce "Babah kina yawaita addu'a kuwa? Tunda kika fad'a mini auren Yaya Tijjani da yarinyar nan ban sake samun nutsuwa ba. Anya kuwa! Ke ce da kanki kika mara bayan irin wannan kwamacalar a zuria guda? Duk matan duniya a rasa wacce zai aura sai wannan abar da aka tozarta ki saboda ita?"
Ta kasa ce wa komai a dalilin yadda take jin an danne zuciyarta. Ga kuma sanyin da yake bin zuciyarta da gangar jikinta gabad'aya.
Ya numfasa ya ce "Ki tsananta addu'ar tsari. Ina yawan mafarkin wani abu kamar tulu ya danne ki. Sannan a k'ofar Dada nake ganin abun. Na kasa gane mene ne shi."
Jikinta ya sab'e da rawa. A rarrabe ta ce "ko randa ka ke ga ni?"
Kai tsaye ya ce "Abu dai da ake zuba ruwa. Amma ba randa ba ce".
Ta ce "Ai kuwa nima kullum sai na ga ni duk yadda aka yi akwsi wani abu a randar nan."
Ta katse wayar, ta zabura ta mike ta dauko tabarya.
Ta yi a'uziya, tare da ce wa "Innahu Sulaimanu wa Innahu Bismillahir rahamanin Rahim".
Ta kuwa fasa gindimemiyar randar da tashi ta yi ta ganta a wajen.
Dada ta fashe da kuka tana ce wa "Hauwa kika fasa mini randa ta. Kinsan ke ma kanki tare da aba ta kika gan ni. Kwanaki biyu tak a duniya Malam ya siyo mini ita tare da katangar wankan jegon ki. Amma yau kika fasa mini da gangan?".
Ita kuwa tunda ta fasa gumi yake yanko mata. Wani irin abu tamkar kiyashi take jin yana sauka daga kanta. Bakinta ya yi nauyi ainun. Daidai lokacin da Innarsu Ubaida ta shigo yiwa Dada sallama zata gidan suna.
Tana ganin ruwa ya jik'a tsakar gidan ga fasasshiyar randa ta hau jaje tana ce wa "Yanzu randar nan mai kafirin sanyi yau ta hadu da ajalinta?"
Da kuka Dada ta ce "Eh kuma kisan wulakanci da rainin wayo a hadu da shi. Ta ajiye ledar kayanta, ta shiga kwashe rugurguzun randar. A nan ta ga k'atuwar laya.
A tsorace ta ce "Dada a 'kona wannan ko ta tsari ce?"
Murya babu amo ta ce "Jefa ta a wuta bansan ko ta mece ce ba. Gidan nan kam ai tuni Malam ya kafe shi. Ba dai mugu ya ga kofar shigowa ba.
Ai kuwa ana kona layar Baba ta ji nauyin da zuciyarta ta yi ta ware. Sanyin da yake ratsa ta na tsoro da zullimin yin jayayaya ta ji duk ya gudu. Ta dinga Hamdala. A zuciyarta kuwa sai gasgata surkulle a ka yi mata ita kanta.
A haka Tijjani suka shigo tare da Nasiba asibiti suka je yin gwaji.
Bin su kawai take yi da ido. Bak'inta sai ambaton "Hasbunallahu wa ni'imal wakil yake yi.
Zufa kuma bata fasa feso mata ba. Gabadaya ta shiga alhinin BAK'AR TA'ADAR da y'ar uwarta shakikiya ta aikata a dalilin son kai da na zuciya.
Ta zuba ido tana nazarin Tijjani. Gabadaya ya kasa sukuni. Idonsa ya kad'a tamkar gauta. Shima sai zufar yake yi. Ya gaishe ta a sanyaye. Ta amsa masa murya babu amo domin gabad'aya ta duniyata ta yi mata tsanani.
Jira take ta ji ya yi sallama ko ta fita. Amma yana zaune, duk da bai sake Bude baki ya yi magana ba.
Duk takalarsa da magana da Dada take yi.

*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
Chapter 122 · 0% Book details