← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 144 OF 146

Sashe 144

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A daddafe kwanakin suka cika muka tattaro muka dawo cikin tsananin farinciki da murna.
Aliyu bai samu sukunin zuwa daukarmu ba. Muna dira ya kira Baban Marina tamkar mai auna lokaci. Ya ce mu dauko shatar mota ta kawomu. Da yake karfe takwas muka sauka a Kano na safiya. Hakan kuwa muka yi. Ban tab'a ganin nisan tazarar Kano zuwa BAUCHI na sai yaiy. Jin na yi gabad'aya na kosa.
Haka muka isa Lafiya muka tarar da gida cike da mutanan Toro da na Bulkachuwa. Ana murna tare da dawowa lafiya. Na kalle shi yana kan kujera ya yi wanka yana sanye da k'ananun kayansa. Ya rame kam. Amma ya yi kyau. Ya yi aski saisaye. Ya yi fes, twins suna gefen hagu da damansa ma'ana sum sanya shi a tsakiya. Sai satar kallon juna muke muna murmusshi. Gabadaya mutanan da suka cika gidan sun gundure ni. So nake kawai su kauce su bamu waje.
Sai la'asar suka dunguma suka tafi Toro tare da Dada da Baban Marina.
Yayin da Aliyu ya tafi da Baba da twins gidansa. Kafin ta koma Bulkachuwa tunda Tijjani ya fito.
Bamu samu sararin marabtar juna ba sai da ya dawo daga sallar Isha, ya rufe gidan. Ko da mutanan Toro suka tafi, jama'ar unguwar sai shige dagice suke mana da sunan murna da kuma yi mini sannu da dawowa.
Da kansa ya yiwa Husna wanka yana ta tsala kukan kiwa. Daga karshe sai na fahimci da ruwan zafi sosao ya yi mata. Dan haka kukan har da dalili. Ya shafe ya da mantaleta, ya Sha nono. Ba'a jima da yin wankan ba kuwa barci ya sure ta irin mai nauyin nan.
Daga haka ya tisa ni a gaba da rawar jiki. Bamu iya ce wa komai ba illa barin da jikinmu yake yi. A matukar matse muke da juna. Abubuwan da suka biyo baya masu nauyi ne.
Sai dai bai yarda min yi barci ba, wanka muka yi muka dinga sallar godiya. Dukkanmu kuka muke yi. Domin al'amuran da muka tsallake taimakonsa ne kawai. Ba dan ikon Allah ba da tuni aurenmu ya dad'e da daidaicewa. Muna cikin bala'in asiri sai kuma k'azafi da hassada ya sake gigitamu. Amma cikin hucewar Ubangiji komai ya wuce.
Da asuba ma da ya dawo rufe gidan ya sake yi. Dai-dai loakcin Husna ta farka. Na canja mata pampers da ta cika shi da fitsari. Na d'ora ta kan fo. Na gyata ta sha nono sai ta sake komawa barcinta. Na kwantar da ita a gadonta tunda Hajiya mai magana da yawun first lady har gado ta kawo mata na garari lokacin haihuwar ta. Na lallaba na shige jikin Tijjani domin barci da gajiya ne a jikina ainun. Tara muka tashi shima kukan Husna ya tayar da mu.
Ya bude ido ya ga na yi mata wanka na ina shirya ta.

*Ba da jimawa ba zan kai Sabo da kaza da Kuma Halin Yau arewa*.

Ya mik'e ya ce "Asiya rabon da na yi barci haka da safe har na manta. Wato mutum baya gane darajar y'anci sai ya rasa y'ancinsa. Gidan gyaran hali babu dad'i! Masifar da na gani ko makiyina bana fatan ya shiga wajen nan. Sannan babu abin da yake sake rikita ni irin Barnar da ta yi katutu a wannan wajen. A had'a masu k'ananun laifuka da manya. Sannan gwamnati bata yi tsarin yiwa masu laifin allurar kashe sha'awa na wani lokaci ba. Ko kinsan luwadi ya yi yawa a gudajen kurkuku?"
Cikin gigita na ce "Subhanallah! Ya rausayar da kai ya ce "Barna kan b'arna sai dai kawai Ubangiji ya yafe mana.
Abin tausayi wani abin da ya sata bai fi dubu biyar ba, amma rashin gata ya sanya an daure shi sherkaru sama da goma. Wani sharri ne irin nawa, wanni sawun barawo ya taka. Wani bisa kuskure ya aikata laifin. Amma duk an runtse ido an ki yiusu sassauci ta ya ya rayuwa ba zata tsananta mana ba? Addu'ar wadanda aka zalunce su babu hijabi. Sannan yanke hukunci babu hujja yana janyowa al'umma fishin Ubangiji.
Bakar Taada ta shiga ko ina a wannan duniyar Asiya."
A raunane na ce "ALLAH ya shiryemu ya kuma kawo mana fita.
Na yi matukar tsorata da yadda ake b'arna a gidan da ake masa lakabi da gidan gyaran hali.
Kwnanaki biyu da fitowarsa muka sami saukin zaryar jama'a. Takanas aka turo mota daga gidan gwamnati. Domin na yi waya da Hajiya akan ina son zu je mu yiwa first lady godiya. Domin na sani abubuwan da aka yiwa Tijjani na alheri har da arzikina da ya ci. Muna zube a gabanta, muna ta godiya. Mai girma gwamana ya ce "Tijjani kana ta sun gurbin aiki a ma'aikatu daban daban saboda a tayaka alhinin halin da ka shiga. Amma Hajiya ta ce "Wanda muka baka zaka yi. Domin ta dad'e da yiwa matarka al'kawarin zata fito da kai, bisa adalcinmu muka jinkirta sai azumi sai ka shiga sahun wadanda gwamnati zata yafe musu, duk da laifin ka mai girmane. Sai kuma gaskiya ta yi halinta. Hajiya ta roki arzikin na rik'e mata kai da kai da kyau dan matarka ta huce wahalar da ta sha ta rashinka. Dan haka zaka zauna a jihar me dan al'ummarka su amafana da kai."
Tijjani ya hau godiya da murna, yayin da kaina ke kasa nake taya shi godiya.
Cikin kasaita first lady ta ce "Sai a kula, a kuma rik'e mini diyata da kyau domin samun yarinya jaruma ikarama kamar Asiya za'a dad'e . Mace ce mai kamar maza. Na shiga zullimi akan sha'anin ka. Saboda soyayya da sadaukarwa da na ga ni a wajenta. Tana son ka. Ka rik'e a ranka ba zan laminci ka juya mata baya ba".
Ga mamakin Tijjani sai ya ji gwamna ya ce "Hajiya yo me yi miki shara ma ai ta wuce ta yi boranci bare y'ar boko irin wannan mai cike da kuruciya."
Tijjani ya ka'du k'warai da gaske. Domin ya fahimci tasirin da uwar dakin Yabi yake da shi a wajen mijinta. Sannan ya gane dukkan alfarmomim da gwamnati ta yi masa da iznin Hajiya ne. Ita kuwa saboda Yabi ta yi hakan. Da gaske nasararorin rayuwarsa na d'amfare da Yabi ne.
Ya sake yin kasa da kai ya shiga yi mata godiya tare da ce wa ", Za'a kiyaye Hajiya!.
Ni kuwa murya na rawa na ce "Na gode mamana. Na sani mahaifiya daya ce, amma idan mutum ya girmama mutane, ya sanyawa harshensa linzami akan sha'anin da ba nasa ba, sannan ya yi gaskiya da juriya sannu a hankali sai Ubangiji ya bashi uwaye masu yawa. Tabbas ina da mahaifiya. Amma ke din uwa ce a waje na. Allah ya kara miki lafiya. Ina fatan idan kin kammala shekarun biyar din data yi muku saura ki zama first lady din Nigerita ba iya ta jihar Bauchi ba."
Dad'i ya kama su daga ita har mijinta. Da barin baki ya ce "Ameen yarinya. Hajiya me za'a bata tukuicin wannan farin fatan da yi mana gabadaya?"
Da murmushin kasaita ta ce "A maye mijinta da gurbin Kwamishinan ma'aikatu da ya rasu satin da ya wuce mutane suke ta zawarcin kujerar."
Ya ce "Angama ranki ya dad'e Tijjani ka zama kwamsinan ma'aikatu na jaha gabadaya. Zan mika sunanka majalisar zartawa ka zama cikin shirin zasu gayyace ka domin tantace ka".
Gabadaya muka rikice da murna da godiya. Yayin da ta ce "Ita kuma a mayar mini da ita wata ma'aikata haka mai dama".
Take ya buga waya akan a kai ni college of education a matsayin non academic staff.".
Ta sake ce wa idan har na zama first lady din k'asa Asiya ki dinga jin ke ce magajiyata."
Na ce "Ina godiya k'warai mamana, alherinki mai yawa ne, ba kya fad'ar magana da zummar wake. Allah ya kai fata mizani".
Muka taho cikin rakiyar jami'an ican tsaro. Kafin kace miye har an sanar gwamna ya nada Tijjani Yusuf Bulkachuwa a matsayin kwaishinan aiyukan jihar.
Ta ko ina murna ake yi. Da kansa Tijjani ya sake gane al'amarin Yabi babba ne. Tabbas ita ce sababin arzikinsa. Sana'ar lallen dai da aka ce zata rike su itace sanadin zargo musu hamshakan matan da suka sada ta da mai dakin gwamna. Babu abin da zai ce da Yabi da sana'arta sai Hamdala. Zai cigaba da girmamata tare da kauce wa dukkan abin da zai had'a su. Domin ya ga ta k'ra wayo. Ta hadu da manyan mata da zasu yi masa fatafata idan ya ce zai taka ta. A ransa sai fad'i yake gwamna na tattala bacin ran Hajiya, bare ni?. Shi kad'ai ya yi dariya tare da kame bakinsa domin ya fahimci sha'anin babbane. Bayan haka Yabi ta yi hak'uri, ta yi juriya, ta yi masa komai. Shi ma zai yi dukkan iyawarsa ya saka mata da alheri kan alheri.

*INA KAWO MAGANIN MATA MASU KYAU DAGA CHAD DA SUDAN*
*MAGANIN SANYI SADIDAN*
*INA AIKAWA KO INA A K'ASAR NAN*
*BA ZAI YIWU NA TALLATA MUKU ABIN DA BA SHI DA KYAU KO INGANCI BA. DOMIN SOYAYYA DA AMINCI NE A TSAKANINA DA KU MASOYA RUBUTUNA*
*KU JARRABA SAIWOWIN DAHUWAR KAZA DA TATTABARU KU GA NI*

*KAZALIKA MAGANIN SANYI DA TSUMIN GORAN TULA BABU NA BIYUNSU*
*GA Y'AYA'N GADALI DA YAKE SHA YANZU MAGANI YANZU*
*ASALIN DAKA NA EMERGENCY*
*DA GUMBA DA KUMA TSUMIN KWAKWA DA ZUMA NA SHARHOLIYA*
*TUNTUBE NI KAWAI TA WHAT'S APP.DAN SAMUN BAYANI NA SOSAI*
*KU GYARA KANKU, KU GYARA Y'AYA'LNKU*
*MASU SHIRIN AURAR DA YARANSU KO KANNENSU A ZO A SAMA MASU KAYA MASU NAGARTA*
*08032773332*
*NA GODE
Chapter 144 · 0% Book details