Sashe 128
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
✍️
*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1
Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
Washagari duku duku Baba Maryo ta zo.
Domin na je gaida Dada na juyo muryarta tana ce wa "Ai ko baki bijire mini ba gabad'aya ba zai aure ki ba, wane shi. Ashe dama arzikin da ake ga ni a tare da shi kazami ne? To ba zata sabu ba. Aure kam tabbas ya fasu fas. Dama ai ba so kike ba, tunda kin ringa kin tsorata da iblishiyar mata tasa. To ta je ta samu sai ta tabbata a matar d'an safarar kwaya ita kad'ai. Mutane babu Allah a ransu. Ka dinga neman arziki yaki haram yaki halal. Dama so na yi na nuna wa uwarta da ita Yaya Hauwa iyakarsu. To tunda bai shiryu ba, huta toro an bar musu shi. Watak'ila ma daurin rai da rai za'a yi masa. Ai da a sau'udiyya aka kama shi fille wa d'an banza mai yiwa iyayensa kallon raini za'a yi".
A sanyaye Dada ta ce "Ai kuwa mai sunan manya ya yi hankali da girmamawa yake gaida kowa kamar ba shi ba. Kawai dai yana nuna son kai ne, ya fi nan nan da k'ofar Alhaji. To wannan kuma dariyar matarsa yake so, ya za'a yi tunda ya jarabtu akan ta.!"
Baba Maryo ta ce "Ban da ni din, ni ce ai ko gaishe ni ba zai yi ba, ya kullace ni ainun. Tunda ake fad'in labarin wadatar da yake ciki, ashana bata tab'a had'a mu ba. Kai ya taka ya je gidana bai san wannan ba. Idan ya gan ni tamkar zai doke ni. Amma yanzu da yake ba shi da kunya har zarya yake yi mini. To na fasa ba shi Nasibar. Ba zai yiwu ba, ya je dai ya k'arata da afiruwar matarsa mai izgili. Kai ahalin Tijjani da Yabi za'a yi majununai, biyu ta had'u y'aya'n iska marasa albarka".
Na sake jin cikin rauni Dada ta ce "Yanzu fa sun yi hankali suna girmama kowa. Yabi da kanta jiya ta zo har nan ta tafi da Nasiba wajen mai sunan manya. Kin san idan Yabin da ce ba za'a yi hakan da ita ba".
Ta saki tsaki ta ce "Yo tunda ya rikice mata ai dole ta kai ta. Amma daga yau zan yanke komai."
Dada ta kame bakin ta. Ita kuwa ta ci gaba da sakin maganganu masu nuni da dama ba Tijjanin take so ya zama surikinta ba. Wadatar da ake kallon ya samu ne ake son su lasa. A yanzu da ya hadu da ibtila'i kuma an janye saboda dama ba da zuciya d'aya aka yi abin da aka yi ba.
Na shiga daga bakin kofa na gaida Dada, duk da tana ce wa "iso mana, ina tagwaye ko basu farka ba?"
"Eh suna barci Dada".
Na gaida Baba Maryo a gajarce. Ta amsa fuska babu walwala. Har na juya sai ce wa ta yi "Yabi ashe haka ya faru da Tijjani?"
Na ce "Eh!
Sai ji na yi ta ce "To wadannan kadarorin da suke yatsun ki da kunnawan ki sai ki hanzarta kad'ar da su dan ki dauka masa lauya domin dai a gindinki da na iyayen ki ya k'are. Gyatumar sa ma yar amshin shata aka mayar da ita. Watak'ila hakkin ta ne ya sanya yake gani a k'waryarsa.
Na juya da nufin bata amsa sai na tuna kanwar mahaifina ce. Ba zai yiwu na yi fad'a da ita a yanzu da hankali ya ratsa ni ba. Nasan kuma dole ni ce a ciki tunda shi da kansa Baban Marina zai ce ai kanwarsa ce ta shiga rigarsa mana.
Dan haka sai na hadiye na ce "To Baba Maryo zan yi hakan".
Ta tunbatsa domin ta washi mu fad'i sunan ta.
***
*BAUCHI*
*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1
Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
Washagari duku duku Baba Maryo ta zo.
Domin na je gaida Dada na juyo muryarta tana ce wa "Ai ko baki bijire mini ba gabad'aya ba zai aure ki ba, wane shi. Ashe dama arzikin da ake ga ni a tare da shi kazami ne? To ba zata sabu ba. Aure kam tabbas ya fasu fas. Dama ai ba so kike ba, tunda kin ringa kin tsorata da iblishiyar mata tasa. To ta je ta samu sai ta tabbata a matar d'an safarar kwaya ita kad'ai. Mutane babu Allah a ransu. Ka dinga neman arziki yaki haram yaki halal. Dama so na yi na nuna wa uwarta da ita Yaya Hauwa iyakarsu. To tunda bai shiryu ba, huta toro an bar musu shi. Watak'ila ma daurin rai da rai za'a yi masa. Ai da a sau'udiyya aka kama shi fille wa d'an banza mai yiwa iyayensa kallon raini za'a yi".
A sanyaye Dada ta ce "Ai kuwa mai sunan manya ya yi hankali da girmamawa yake gaida kowa kamar ba shi ba. Kawai dai yana nuna son kai ne, ya fi nan nan da k'ofar Alhaji. To wannan kuma dariyar matarsa yake so, ya za'a yi tunda ya jarabtu akan ta.!"
Baba Maryo ta ce "Ban da ni din, ni ce ai ko gaishe ni ba zai yi ba, ya kullace ni ainun. Tunda ake fad'in labarin wadatar da yake ciki, ashana bata tab'a had'a mu ba. Kai ya taka ya je gidana bai san wannan ba. Idan ya gan ni tamkar zai doke ni. Amma yanzu da yake ba shi da kunya har zarya yake yi mini. To na fasa ba shi Nasibar. Ba zai yiwu ba, ya je dai ya k'arata da afiruwar matarsa mai izgili. Kai ahalin Tijjani da Yabi za'a yi majununai, biyu ta had'u y'aya'n iska marasa albarka".
Na sake jin cikin rauni Dada ta ce "Yanzu fa sun yi hankali suna girmama kowa. Yabi da kanta jiya ta zo har nan ta tafi da Nasiba wajen mai sunan manya. Kin san idan Yabin da ce ba za'a yi hakan da ita ba".
Ta saki tsaki ta ce "Yo tunda ya rikice mata ai dole ta kai ta. Amma daga yau zan yanke komai."
Dada ta kame bakin ta. Ita kuwa ta ci gaba da sakin maganganu masu nuni da dama ba Tijjanin take so ya zama surikinta ba. Wadatar da ake kallon ya samu ne ake son su lasa. A yanzu da ya hadu da ibtila'i kuma an janye saboda dama ba da zuciya d'aya aka yi abin da aka yi ba.
Na shiga daga bakin kofa na gaida Dada, duk da tana ce wa "iso mana, ina tagwaye ko basu farka ba?"
"Eh suna barci Dada".
Na gaida Baba Maryo a gajarce. Ta amsa fuska babu walwala. Har na juya sai ce wa ta yi "Yabi ashe haka ya faru da Tijjani?"
Na ce "Eh!
Sai ji na yi ta ce "To wadannan kadarorin da suke yatsun ki da kunnawan ki sai ki hanzarta kad'ar da su dan ki dauka masa lauya domin dai a gindinki da na iyayen ki ya k'are. Gyatumar sa ma yar amshin shata aka mayar da ita. Watak'ila hakkin ta ne ya sanya yake gani a k'waryarsa.
Na juya da nufin bata amsa sai na tuna kanwar mahaifina ce. Ba zai yiwu na yi fad'a da ita a yanzu da hankali ya ratsa ni ba. Nasan kuma dole ni ce a ciki tunda shi da kansa Baban Marina zai ce ai kanwarsa ce ta shiga rigarsa mana.
Dan haka sai na hadiye na ce "To Baba Maryo zan yi hakan".
Ta tunbatsa domin ta washi mu fad'i sunan ta.
***
*BAUCHI*