← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 146

Sashe 28

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*

Amma akwai tausayi mussaman idan ya ga kina kuka, to kin karya masa lagonsa, sannan yanzu ya fara sanin kishin kansa har yana taya wani ciwon abin da aka yi masa.
Ashe da ya fita wajen Baban Marina ya raka wannan mutumin da ko sunansa ban sani ba, ya nemi a bashi izinin fara magana da ni.
Baba ya ce "Ya bashi damar neman yardata, amma idan ban amince ba, ba zai mini dole ba.
Shi kenan sai Alhaji Mustapha Zaki yake zuwa, ni da kaina kunyar yadda nake yar mitsil a gabansa nake yi. Dogo ne sosai yana kuma da jiki, ga tumbi sai dai tumbin bai yi muni da yawa ba, ustazu ne sosai domin ya tsayar da gemun sunnah.
Ku'di yake sakar mini da suturu na alfarma, ga kuma mutunta ahalin gidanmu.
Dada kanta sonsa take yi a dalilin idan zai zo sai ya kawo mata rafar sabbin ku'di, y'an 100, da na 50, da na 20.
Yana cewa gashi ta ajiye canji a hannunta, duk zuwa kuwa. Ga ledar tufa da kilishi.
Nawa kuwa y'an 500 da 200 ne.
Bulkachuwa ya zama magayak'insa.
Kullum sai ya masa kamfen, fa'di yake "Gidan ki daban zai baki Asiya, idan kika yi sa'a ma Umrar bana da ke za'a yi, aikin hajji kuwa tabbas ne.
Ba ruwanki da tsufansa, lallaba ki zai yi.
Ni kaina alherin da nake samu a jikinsa ba ka'dan ba ne.
Kin ga "Na kalli hannunsa da yake karkada wa.
Mukulli na ga ni ya ce "Mashin ya ba ni sabo dal, gwamnatin jahar Bauchi take raba wa matasa, shine ya saka sunana.
Dan Allah Asiya ki so mutumin nan, oh wani hanin ga Allah baiwa.
Yarinya kin tako arziki, na tabbatar Gwaggo data haife ki da akwai wutar Nepa a time din Wallahi.
Na miki murna ma da wannan dan tsurut din bai same ki ba.
Ai ke babbar mace ce, sai manyan maza, amma yana tafiya tamkar iska ta hure, kirjinsa duk bai fi allona na makarantar tsangaya ba".
Na b'ata rai na ce "Yaya J din kake yiwa haka akan bare?
Sannan nima ai y'ar tsurut ce ta ina na zama babbar mace?"
Ya murmusa ya ce "Ba sai na bu'de maganar ba, ke ma kinsan yadda ake miki layi ai akwai sirri na mussaman a tare da ke. Na'kasunki biyu ne tsayayyiyar zuciya, kuma taurarriya, da fitsara, dole handle dinki sai tsayyayen namiji k'arfaffa ba lusari irinsa ba".
Na sake b'ata rai na ce "To yadda kake ganin zuciyata, tasa har tafi tawa tsayuwa da jarumta".
"Ke tafi can, me kika sani? Wai har yau son Jabir kike yi? Tabdi jam lallai so ba k'arya ba ne. Jiya fa na gan shi goye da Maijidda a mashin ina ga d'an yawon shan iska suka fito".
Nan da nan idona ya k'ada sosai hawaye ya cika su, ya mike yana fa'din "So sorry Asiya Toro. Ki gode Allah da ya kawo miki Honarable Zaki. Domin da ki yi kuka a inda kike so, gara ki yi a inda ake son ki, da ki yi kuka a gidan cin abinci gara ki yi kuka a gidan daula sosai, domin mu maza da kika ganmu so baya hanamu murza kanku".
Na girgiza kai na ce "Zan amince ne idan kai ma ka yarda
zaka shirya da Nasiba, ni shaida ce akan ba wanda take kula wa saboda kai".
Ya bata fuska ya ce "Kin san Allah?
Zan ci mutuncinki Asiya Toro! Kada ki saurare shi mana, shawara na baki saboda ina nufin ki da alheri, idan baki so ba, ki sallame shi, ki jira wanda zaki dinga kuka a gaban murhun gawayi, da kishiya.
Ga kuma ba'kin cikin da zaki kunsa a wajen ahalinsa, shasha da bata san me ya dace ba".

*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.

✍️
*BAKAR TA'ADA*
*NA*
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*
*(MRS M.I.NASHE)*

*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•

*ALBISHIRINKU*
*MASOYAN LITTAFAN MARUBUCIYA HAFSAT C SODANGI*!
*DUBA DA YADDA KUKE KEWAR RUBUTUNTA YA SANYA TA YI SHIRIN SAKE DAWOWA DAN TA SAKE MUKU WANI RUBUTUN SABO DAL*
*AMMA KAFIN HAKAN TA DAWO MUKU DA TSOFAFFIN LITTAFAN TA ZUWA KAN WAYA, DAN KU SAKE BITA TARE DA NAZARIN KYAWAWAN SAKON DA TAKE NUFIN ISARWA GAREMU*.

*A YANZU HAKA LITTAFAI HUDU NE RIGIS*

*WAYYO DUNIYA 1-3*
*KYAUTATA 1-3*
*DAGA K'IN GASKIYA 1-3*
*MATA MASU DUNIYA 1-3*
*KO WANNE 1K NE AMMA AKWAI DISCOUNT IDAN ZA'A SIYA SAMA DA GUDA DAYA*

*MISALI GUDA BIYU-1500*
*GUDA UKU 2500*
*GUDA HUDU 3500*

*ZA'A TURA KUDIN TA ASUSUN MARUBUCIYAR KAMAR HAKA*
*0082739293, ACCESS BANK HAFSAT YUNUS ABDULLAHI*

*SAI A TURO MINI SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*SAI NA BADA LITTAFIN DA AKE SO*

*MADALLAH DA KARFAFA GUIWARKU*
*MADALLAH DA SOYAYYARKU GA RUBUTUNMU*

*AKWAI LITTAFANTA SAMA DA GUDA GOMA DA A YANZU SUKE SOFT COPIES, KAWAI KI TAMBAYI DUK WANDA KIKE NEMA A WAJENA CIKIN LITTAFANTA NA BAYA*.

*Saura kiris shaufakan kyauta su k'are*
*Turka turkar da ke cikin labarin nan kabiran ne. Har yanzu shimfi'da kawai muke yi bamu kutsa labarin ba tukun*.
*HANZARTA ki shiga tafiyar dan karfafa guiwarki ga marubuciya da karatun cikin SALAMA.*
*Kudin karatun ki 500/1k*
*Via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Dahiru*
*Zenith Bank*.
*Ko*
*7061488065*
*Surayya Dahiru Ibrahim*
*Opay Bank*.
Chapter 28 · 0% Book details