← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 146

Sashe 51

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

*MARUBUCIYA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
*Tana farincikin sanar muku da sabon littafin ta mai suna YA ZA A YI? Wanda za ta sake shi ranar d'aya ga watan Oktoba (first October) wannan karon ma marubuciyar taku ta shirya sosai domin nishad'antar daku tare da fad'akarwa🥰 Ba sai na tsaya yi muku bayanin rubutunta ba domin da yawa daga cikin masu bibiyar litattafanta sun san cewa tana k'okari gurin ganin ta yi rubutu akan abubuwan da suke faruwa, mussaman a zamantakewar aure da tarbiyar yaranmu, Uwa uba kuma litattafanta akwai soyayya mai tsafta da nishadi da 'karuwa! Kada dai ku sake a baku labarin wannan littafin mai suna( YA ZA A YI)❓ Zaku iya yi mata magana ta Whatsapp da wannan numbers*
*08089965176*
*07084653262*

✍️
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*

*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*

*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.

*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.

37&38.
Da yamma lis sai ga Yaya Ummi da tarkacen su tsintsiya da sauran kayayyaki har da su kuloli masu kyau da zannuwan gado na sani wanda aka samu na gudunmawa ne aka karo zabo mini masu kyaun cikinsu.
Ta sake gyara mini kicin din. Na bata tarkacen robobi da wani flask din roba irin mai biyun nan.
Kayan lefena kuwa turamen atamfofi biyu na bata da hijabi hadi da kayayyakin kwalliya.
Ta dinga yi mini addu'ar Allah ya zaunar da ni lafiya.
Ta bu'de jakar hannunta ta dauko wata yar roba mai dauke da garin magani kore. Ta sassauta murya ta ce ko zaki dinga shan wannan a cikin madara ko yoghurt?"
Na kar'ba na ce "Na menene?"
Ta yi k'asa da kai ta ce "farin ciki da dokin juna zai sanya muku"
Na yi maza na mayar mata cikin jakarta. Tare da cewa "Da dai ba irin wannan mutumin aka aura mini ba."
Ta ce "shikenan da har da INGANTATUN SAIWOWIN DAHUWAR GIMBIYAR KAZA. Amma zan ajiye miki. Na sani wataran zaki nema da kan ki.
Idan kuma na yi amfani da su, sai a kawo miki wani ta hannun kanwar kawata Aisha Lame mai siyar da kayan kwalliya masu daraja (oriflame).
Tasan Surayya Dee da take kawo su daga chadi.
Baki na tab'e baki, ina kallonta kawai, domin har abada ni Yabi bazan yi wani abu dan na sanya Tijjani farin ciki ba.
Muna haka ya shigo, suka gaisa sosai cikin walwala da tsokanar juna.
Bai jima da dawowa ba, ta yi haramar tafiya nata gidan.
Da yake mutumiyarsa ce.
Ya ce "Ta jira ya kai ta a mashin".
Ta galla masa harara da cewa "Ni zaka goya Yaya Bulkachuwa?Wallahi ba zan sake biye wa tsokanar da kake yi mini ba, dan ka riga ka zama k'anina".
Ya kwashe da dariya ya ce wannan kuwa shine tatsuniyar gizo da k'oki. Ke yanzun nuna mini kika yi Asiya Toro ta fini a wajen ki?"
Ta mak'e kafa'da ta ce "Ato Wallahi ka kama k'afata dai".
Ya tsugunna a gaban ta ya ce "Dai-dai ina zan kama Ummi?"
Ta yi gaba ta bar shi tana fa'din "Hmm sai ka yi kai ka'dai".
Ta goyi y'arta shi kuma ya d'aukar mata ledar kayanta.
Ya yi gaba ya na jiranta.
Da k'yar muka rabu. Cikin lallashi take ta nanata "Ki zauna lafiya, ki kwantar da hankalinki da na iyayenmu dan Allah. Kin ga dai an riga an yi auren nan. Allah ya taimake ki, ya hore miki shi. Nan da wata daya ki cigaba da sana'ar ki, domin mace mai neman na kanta ta huce takaicin babu".
Ta bata rai ta ce "kinsan dai ba'kin cikin da na kwankwada a dalilin bani da yar'uwar da aka aurar da muke daki daya. Yanzu murna nake yi kema an aurar da ke na samu abokiyar ha'di. Komai ya taso miki ni ce a hakku saura ki ce zaki bayar da ni a wajensu ta hanyar nunawa duk daya muke ni da su a wajen ki.
Gasu nan su hudu ne dakinsu daya."
Nima na bata rai na ce "To idan hakane ita kuma Ubaida dawa zata hada kai kenan?
Ko so kike ita ma ta fuskanci tsananin da kika fuskanta? Ni fa dukkan y'ay'an Babanmu ina sonsu da dukkan zuciyata".
Ta zaburo mini ta ce "Ban ce kada ki so su ba, amma ai wata kusan tafi wata".
Na yi dariya na ce "To kawai ki ha'da ni da Nazira da kuma Ubaida ki jamu a jikinki, ki dai-daita su da ni. Shikenan Kinga kin samu k'anne uku aurarru tashi guda.
Da sannu suma manyan sai su dawo cikinmu mu zama madaurin tsintsiya".
Ta yi gaba tana fa'din "To uwar Iyah! Ta ya ya zan ha'da shakikiyata da dan uba su zama duka daya ne?"
Na k'yal-k'yale da dariya tare da fa'din "Yaushe zaki dawo?".
Ta ce "sai an kwana biyu".
Na zauna ina nazarin Yaya Ummi mutumiyar kirki ce, amma rashin adalcin da manyanmu suke yi mata da kuma yadda kishiyarta ta jefa yan'ubanci a tsakanin y'ay'ansu ya sanya ta k'yamaci dan uba. Na yi mata uzziri domin ita da yaranta suna fuskantar zazzafan yan'ubanci.
Ina fatan watarana duka y'ay'an Babanmu mu zama abu guda, ina matu'kar son mu gane girman nasaba irin ta uba daya.
Chapter 51 · 0% Book details