Sashe 91
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Na gama komai na kai falo kamar yadda na saba. Shi kuma ya zama mutum mutumi.
Na fito na ce "Ga abinci ko sai ka dawo daga masallaci?"
Ya zuba mini ido ya rasa abin fa'da.
Ya tashi ya ce "Da sauran lokaci ai."
Na zuba mana kamar yadda na I'm. Amma gaba'daya mun kasa ci sai faman juya shi muke yi.
Gara ni na ci loma biyu na ji mak'oshina ya cushe na ajiye. Shi kuwa yama kasa kai wa ba'kin nasa.
Ya gaji ya kalle ni ya ce Dan Allah Yabi ki yi ha'kuri, ki yafe mini".
Ba ja in ja na ce "To".
Daga haka kuma ban sake ce wa komai ba. Ya yi maganganu na ban ha'kuri da nuna nadama masu yawa amma ban ko kalle shi ba. Aka kira sallah ban yarda na bu'de baki mun yi magana kamar yadda yake fata. Ya yi alwala ya tafi masallaci.
Har muka haramar kwanciya ban bu'de baki na ce k'ala ba. Duk jaye-jayen maganarsa kuwa. Da muka kwanta ya fara lalubata ban hana shi ba, amma ko kwakkwaran motsi ban yi ba. Ya yi duk abin da zai yi dan na motsa ko na mayar masa martani amma tamkar an shuka dusa.
Ya gaji ya koma ya kwanta yana fa'din "Innalillahi wa ilaihir rajiun" .
Ya ru'ko ni da rawar murya ya ce "Yabi ki yiwa Allah, ki bu'de baki mu yi magana".
Yana rufe baki na ce"To".
"Asiya ki yi ha'kuri, ki yafe mini, dan Allah, dan Annabi, ki yafe mini".
Na yi shiru. Ya sake ce wa Bansan me ya same ni ba Yabi. Dan Allah ki mini uzziri ki yi ha'kuri ki gafar ce ni".
Nan ma na ce "To".
Ya yi iya ban hakuri, amma ban yarda na ce komai ba.
Da gari ya waye da wuri ya dawo daga masallaci ya hau hidimar gyaran gida.
Ya yi abin karya wa. Har d'aki ya kawo mini amma ina ci sau daya ban sake kai wa na biyu ba, na ce na koshi. Ya yi shiru ya rasa yadda zai yi.
Bai fita ko ina ba. Yini aka yi ana zuwa lalle amma ban iya yiwa ko mutum daya ba. Sai ha'kuri nake basu tare da uzzirin cewa bani da lafiya ne.
Hakan da ya ga ni ya sake rib'anya tashin hankalinsa. Domin yasan yadda nake matu'kar son sana'ata. Bana son abin da zai hana ni yin lalle ko kitso.
Amma da bakina nake sallamar mutane yasan al'amarin da yake zuciyata ba k'ank'ani ba ne.
Kwanaki uku muna cikin wannan halin. Daga ni har shi, mun yi matu'kar rame wa tunda bama iya cin abinci ga rashin nutsuwar zuciya.
Ya yi juyin duniya mu yi magana na ki, domin har yau ban yarda na yi masa korafi ba. Komai kuma zai ce sai na amsa da "To". Kullum safiya zan gaishe shi, zan kuma amsa sallamar sa idan ya shigo. Daga hakan kuma bazan sake yarda na ce komai ba. Rashin yin lallen har zuwa lokacin ya fara ta'bamu tunda shi ma baya iya fita, ko ya fitan ma baya nisan kiwo zai dawo.
Ranar da aka yi kwanaki biyar da faruwar al'amarin, ya zauna ya bani hakuri tamkar yawun bakinsa zai k'afe. Har da k'wallarsa. Amma ban ce komai ba, sai ma murmushi mai ciwo da na yi na ce masa "To me ka yi ne?"
Duk da k'arancin shekaruna amma na fahimci shirun da na yi masa ba k'aramin dafa shi take yi ba. Ba abin da yake so irin na yarda mun yi magana ko da rashin kunya ne na yi masa. Amma ban yi hakan ba. Ni a karan kaina so nake na yi kuka, na caccaba masa maganganun da zasu gasa masa zuciya tamkar yadda ya yi dalilin da tawa zuciyar take gasuwa, amma na kasa.
Tsawon sati guda muna cikin wannan matsanancin halin, daga ni har shi mun zama wasu iri. Gidanmu ya koma tamkar na zaman makokin mutuwar uwa mahaifiya.
Sannan na k'i yin k'unshi har lokacin. Al'amarin da ya sake damalmala mana komai.
Shi kam kawai k'arfin halin da aka san maza da shi ne. Amma kana kallonsa kasan yana dandanar kudarsa da shiruna. Yadda bana cin abinci haka shi ma baya ci. Gara ma ni da daddare na kan yi barci, amma shi duk juyin da zan yi zan gan shi kan sallaya ko yana zaune ko kuma yana sallah.
Da asuba ya dawo ya tarar har na koma na kwanta.
Ya zauna a bakin gadon. A sanyaye ya ce "Yabi wai a haka zamu rayu ne? Bazan iya wannan rayuwar ba. Ki yiwa Allah da ma'aiki ki bu'de baki ki fa'di duk abin da kike so. Na ro'ke ki ba dan ni ba, da Allah nake ha'da ki."
Ko motsi ban yi ba. Bare na tanka masa.
Ya tsananta da magiya. Sai kawai ji na yi cak ya dauke ni ya yi nufin d'ora ni kan cinyoyinsa. Ai gaba'daya wani irin k'arfi mai tattare da matsanancin fishi ya taso mini. Da dukkan zuciyata na fisge na ingiza shi ya fadi k'asa warwas.
Na dinga huci mai zafi, amma na kasa bu'de baki na yi magana.
K'irjina sai harbawa yake yi da tsananin gaske.
Ya mik'e ya kafe ni da ido, cikin kad'uwa da tashin hankali. Ya ce "Dan Allah bu'de baki ki yi magana. Fadi me zaki ce, idan kuma na zauna ki mini duka zai fi mini akan irin halin da nake ganin ki, ki yafe wa mijinki, ki yafe wa masoyinki, ki yafe mini, kaddara ce ta hau kaina Asiya".
Na juya na kwanta ba tare da na ce uffan ba.
Kukan kuma bai zo ba.
Ya kasa hakuri ya sake biyo ni inda nake kwance ya hau lalubata, ban hana shi ba, ban kuma yi wani yun'kurin da zan tankwabar da shi ba. Ya yi abin da zai yi. Yana gamawa na lalubi zanina na daura na fice.
Wanka na yi, sannan na dawo na kwanta. Bayan na mulke jina da hadadden man oriflame. Wanda jakadiyar kamfani ce ta za'ba mini shi fa kanta, q cewarta shi zai fi dace wa ta tarar fatata.
*Kunsan dai Aisha Lame make up artist din Guduyo ce. Yanzu ma bata bata bar fatar Yabi babu gyara ba*.
*Kun tandadi fame wash din nan kuwa da na yi ta jaddada muku muhimmancinsa a wajenku?*
*Ku tuntu'be ta a wannan lambar dan samun sabbin kayanta masu kyau da farashi mai sau'ki da ya zarta na saura*.
*07036662633*.
Na fito na ce "Ga abinci ko sai ka dawo daga masallaci?"
Ya zuba mini ido ya rasa abin fa'da.
Ya tashi ya ce "Da sauran lokaci ai."
Na zuba mana kamar yadda na I'm. Amma gaba'daya mun kasa ci sai faman juya shi muke yi.
Gara ni na ci loma biyu na ji mak'oshina ya cushe na ajiye. Shi kuwa yama kasa kai wa ba'kin nasa.
Ya gaji ya kalle ni ya ce Dan Allah Yabi ki yi ha'kuri, ki yafe mini".
Ba ja in ja na ce "To".
Daga haka kuma ban sake ce wa komai ba. Ya yi maganganu na ban ha'kuri da nuna nadama masu yawa amma ban ko kalle shi ba. Aka kira sallah ban yarda na bu'de baki mun yi magana kamar yadda yake fata. Ya yi alwala ya tafi masallaci.
Har muka haramar kwanciya ban bu'de baki na ce k'ala ba. Duk jaye-jayen maganarsa kuwa. Da muka kwanta ya fara lalubata ban hana shi ba, amma ko kwakkwaran motsi ban yi ba. Ya yi duk abin da zai yi dan na motsa ko na mayar masa martani amma tamkar an shuka dusa.
Ya gaji ya koma ya kwanta yana fa'din "Innalillahi wa ilaihir rajiun" .
Ya ru'ko ni da rawar murya ya ce "Yabi ki yiwa Allah, ki bu'de baki mu yi magana".
Yana rufe baki na ce"To".
"Asiya ki yi ha'kuri, ki yafe mini, dan Allah, dan Annabi, ki yafe mini".
Na yi shiru. Ya sake ce wa Bansan me ya same ni ba Yabi. Dan Allah ki mini uzziri ki yi ha'kuri ki gafar ce ni".
Nan ma na ce "To".
Ya yi iya ban hakuri, amma ban yarda na ce komai ba.
Da gari ya waye da wuri ya dawo daga masallaci ya hau hidimar gyaran gida.
Ya yi abin karya wa. Har d'aki ya kawo mini amma ina ci sau daya ban sake kai wa na biyu ba, na ce na koshi. Ya yi shiru ya rasa yadda zai yi.
Bai fita ko ina ba. Yini aka yi ana zuwa lalle amma ban iya yiwa ko mutum daya ba. Sai ha'kuri nake basu tare da uzzirin cewa bani da lafiya ne.
Hakan da ya ga ni ya sake rib'anya tashin hankalinsa. Domin yasan yadda nake matu'kar son sana'ata. Bana son abin da zai hana ni yin lalle ko kitso.
Amma da bakina nake sallamar mutane yasan al'amarin da yake zuciyata ba k'ank'ani ba ne.
Kwanaki uku muna cikin wannan halin. Daga ni har shi, mun yi matu'kar rame wa tunda bama iya cin abinci ga rashin nutsuwar zuciya.
Ya yi juyin duniya mu yi magana na ki, domin har yau ban yarda na yi masa korafi ba. Komai kuma zai ce sai na amsa da "To". Kullum safiya zan gaishe shi, zan kuma amsa sallamar sa idan ya shigo. Daga hakan kuma bazan sake yarda na ce komai ba. Rashin yin lallen har zuwa lokacin ya fara ta'bamu tunda shi ma baya iya fita, ko ya fitan ma baya nisan kiwo zai dawo.
Ranar da aka yi kwanaki biyar da faruwar al'amarin, ya zauna ya bani hakuri tamkar yawun bakinsa zai k'afe. Har da k'wallarsa. Amma ban ce komai ba, sai ma murmushi mai ciwo da na yi na ce masa "To me ka yi ne?"
Duk da k'arancin shekaruna amma na fahimci shirun da na yi masa ba k'aramin dafa shi take yi ba. Ba abin da yake so irin na yarda mun yi magana ko da rashin kunya ne na yi masa. Amma ban yi hakan ba. Ni a karan kaina so nake na yi kuka, na caccaba masa maganganun da zasu gasa masa zuciya tamkar yadda ya yi dalilin da tawa zuciyar take gasuwa, amma na kasa.
Tsawon sati guda muna cikin wannan matsanancin halin, daga ni har shi mun zama wasu iri. Gidanmu ya koma tamkar na zaman makokin mutuwar uwa mahaifiya.
Sannan na k'i yin k'unshi har lokacin. Al'amarin da ya sake damalmala mana komai.
Shi kam kawai k'arfin halin da aka san maza da shi ne. Amma kana kallonsa kasan yana dandanar kudarsa da shiruna. Yadda bana cin abinci haka shi ma baya ci. Gara ma ni da daddare na kan yi barci, amma shi duk juyin da zan yi zan gan shi kan sallaya ko yana zaune ko kuma yana sallah.
Da asuba ya dawo ya tarar har na koma na kwanta.
Ya zauna a bakin gadon. A sanyaye ya ce "Yabi wai a haka zamu rayu ne? Bazan iya wannan rayuwar ba. Ki yiwa Allah da ma'aiki ki bu'de baki ki fa'di duk abin da kike so. Na ro'ke ki ba dan ni ba, da Allah nake ha'da ki."
Ko motsi ban yi ba. Bare na tanka masa.
Ya tsananta da magiya. Sai kawai ji na yi cak ya dauke ni ya yi nufin d'ora ni kan cinyoyinsa. Ai gaba'daya wani irin k'arfi mai tattare da matsanancin fishi ya taso mini. Da dukkan zuciyata na fisge na ingiza shi ya fadi k'asa warwas.
Na dinga huci mai zafi, amma na kasa bu'de baki na yi magana.
K'irjina sai harbawa yake yi da tsananin gaske.
Ya mik'e ya kafe ni da ido, cikin kad'uwa da tashin hankali. Ya ce "Dan Allah bu'de baki ki yi magana. Fadi me zaki ce, idan kuma na zauna ki mini duka zai fi mini akan irin halin da nake ganin ki, ki yafe wa mijinki, ki yafe wa masoyinki, ki yafe mini, kaddara ce ta hau kaina Asiya".
Na juya na kwanta ba tare da na ce uffan ba.
Kukan kuma bai zo ba.
Ya kasa hakuri ya sake biyo ni inda nake kwance ya hau lalubata, ban hana shi ba, ban kuma yi wani yun'kurin da zan tankwabar da shi ba. Ya yi abin da zai yi. Yana gamawa na lalubi zanina na daura na fice.
Wanka na yi, sannan na dawo na kwanta. Bayan na mulke jina da hadadden man oriflame. Wanda jakadiyar kamfani ce ta za'ba mini shi fa kanta, q cewarta shi zai fi dace wa ta tarar fatata.
*Kunsan dai Aisha Lame make up artist din Guduyo ce. Yanzu ma bata bata bar fatar Yabi babu gyara ba*.
*Kun tandadi fame wash din nan kuwa da na yi ta jaddada muku muhimmancinsa a wajenku?*
*Ku tuntu'be ta a wannan lambar dan samun sabbin kayanta masu kyau da farashi mai sau'ki da ya zarta na saura*.
*07036662633*.