Sashe 81
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Jikinsa ya yi sanyi domin ya ga matsanancin fishi a tare da ni.
Ya numfasa ya ce "Na sani ai ba kya sona Asiya. Ban manta ba, amma na sakankace a d'an zaman da muka yi, zaki iya mini kawaici da alkunya akan abin da kika san zai musguna mini tunda kin sani sarai an jarrabe ni akan son ki. Amma yanzu na gane da gaske ba kya sona tunda akan idona kika k'i gaida Baban Tsakiya cikin mutunci duk da kashedin da nake yi miki da ido. Sannan kika gaida Jabir cikin falli har kina kiransa Yaya alhalin kin kankare zumuntar da ubansa."
Na yi shiru domin kam jikina ya yi tub'us.
Ya cigaba da ce wa "Saboda shi kina sonsa, kuma yafi ni ku'di shi yasa kike ce masa Yaya ni kuma ki gatsa Tijjani gatsal duk da na girme shi kuma ni ne mijin ki. Asiya ba zamu tab'a daidaita wa da ke ba alhalin kin ri'ke BAK'AK'EN TA'ADODI. Yanzu duk k'uruciyar ki ai k'iris ya rage ki yi sha bakwai. Kin san kuma hukuncin wacce ta bu'de baki ta ce mijinta ya sake ta ba tare da gamshasshen dalili ba. Sannan kina da ra'ayin ruk'au na k'ullaci. Hakan kuma ba siffar mace ta gari ba ce. Kamata ya yi zuciyar mace ta zama mai taushi da sassauci ba mai tauri da tsanani ba."
Na ji kunyar kalamansa mussaman akan J.
Na tabbatar shi ba na ce masa Yaya. Amma ban da yau ai nafi wata ban kama sunansa ba, sai dai na yi masa magana kawai. Domin na da'de da daina fa'da a dalilin kunya na kama ni tare da nauyin gatsa sunan nasa.
Na tura baki na juya baya. Cikin k'unk'uni na ce "To ai kai ma kana da Bak'ar Ta'ada din, akan me tun a ranar ba zaka fa'da mini laifina ba, sai kawai ka k'ulla ce ni, ka tsiri fishi. Ni ba Allan musuru ba, ta ina zan san kuskurena?"
Ya matso jikina ya ce "Da kina sona ai tun a lokacin zaki fahimci sauyin nawa, sai ki shawo kaina ki ririta ni, ki mantar da ni b'acin ran da nake ciki. Amma saboda am nothing to you ai share ni kika yi. Kika tattara kika yi wurgi da ni".
Na cuna baki na yi shiru. Ya mik'e dukkan k'afafuwan sa. Ya janyo ni ya kwantar a kai. Ya shiga wasa da gyararren gashina. Murya a dak'ushe tabbacin yana cikin kewa ya ce "Bana son abubuwan da kike yi a gabansu. Su din iyaye ne. Ta ko wacce fuska sune a sama da ke.
Zan yi hakuri da komai akan sha'anin ki, amma ban da na fito na fito da iyaye, bana so, ki bari."
Na yi shiru ban amsa ba.
Ya sassauta murya ya ce "kin yi shiru."
Na sake yin shiru still.
Ya zame ni daga jikinsa ya juya baya ya yi kwanciyarsa.
Ina ganin hakan ai kuwa na tak'ark'are na zunduma masa fallashasshen kukan da baya so.
Ina ce wa "Tunda juninka k'ullaci ne ka mayar da ni gidanmu kawai".
Ya juyo da azama ya ce "Asiya ki cigaba da wula'kanta ni. Amma ki sani komai zaki yi ni ba zan mayar da ke ba, domin ina son ki, ke da ba kya sona sai ki tafiyar ki, hakan kuma ba shine k'arshe farin-ciki a gare ni ba."
Na sassauta kukana domin na ga ya hassala sosai.
Na dinga yinsa kasa kasa irin mai cin rai din nan.
Da ya gaji da jin kukan nawa ya saka hannunsa ya ja ni jikinsa ya ce "Yi shiru Asiyata, amma ba zamu shirya ba sai kin ba ni hakuri dole".
Duk yadda na k'agu mu shirya fuska na yi da ce wa "Ai ban maka laifi ba. Sannan ba dan komai nake ce wa Jabir Yaya ba sai dan yana ce mini Yabi ne. Amma kai sai ka dinga ce mini Asiya Toro babu ko sha'awa ma".
Ina rufe baki ya ce "Har abada ba zan ce Yabi ba, idan ya so ba Tijjani kawai ba, ki fa'di cikakken sunan nawa Tijjani Yusuf Bulkachuwa! Marar kunya. Shine rannan kika yiwa yaro sababi akan ya k'ira ni da Tijjani to ke d'in kin saya ne bare ki ji ciwon wani bai saya ba. Kuma ni ban damu sai kin saya d'in ba".
Na nisa na saki ajiyar zuciya irin wacce ake yi idan an ci kuka sosai. Na ce "Ni fa tuni na samo maka sunan da zan fa'da maka, amma sai na haihu".
Maganar ta zo masa a bazata. Ya ru'ko ni ya ce "Kina son haihuwa ne Asiya?"
Da sauri na ce "Ina so sosai, domin duk wanda muka taso ko wacce ta haihu. Wadanda aka yi aurenmu tare Nasiba da Ubaida dukkansu ciki ne da su, ni ce kawai ba ni da shi".
Na fa'da da karyayyar murya.
Ya sassauta ya ce "Asiya haihuwa lokaci ne da sannu ke ma wataran zaki gan ki da naki cikin. Tunda kin daina guduna, sannan nima ina iyakacin k'ok'ari, kawai mu dinga addu'a".
Na ce "To. Ka ga Gwaggo ma ta ce ba zata zo gidan nan ba sai na haihu".
Ya rungume ni sosai ya ce "In sha Allah zaki haihu Asiyata. Mace kike so ko namiji?"
Kai tsaye na ce "Ni dai na samu cikin nafi so. Ko mai na haifa ina so ba ni da za'bi."
Ya yi dariya ya ce "Tom shike nan Allah zai bamu In sha Allah! Kawai ki kara zama jaruma, ko sau nawa za'a yi kada ki yi musu ko ki ce kin gaji".
Na ce "Da gaske idan na yi haka zan samu cikin ko dai wayo zaka yi mini?"
Ya k'yal-k'yale da dariya ya ce "Ba wani wayo gaskiya nake fa'da miki Asiyata".
Daga hakan kuma ya shiga kissing d'ina tare da zafafan sakonni masu rikita ni. Sai da ya tabbatar ya rura mini jiki. Sannan ya sake ni ya kwanta tare da ce wa "Au ashe baki ba ni ha'kuri ba fa, bamu shirya ba".
A hankali na ce ", Mun shirya mana, ba har ka yi dariya ba yanzu".
Ya ce "Ai ba ki bani hakurin da na ce ki ba ni ba".
Na fara kukan shagwaba, ya juyo ya ce "To fa'da mini a kunne na ji".
Cikin kuka kuka na ce "Allah ya baka hakuri".
Ina fa'din hakan ya rungume ni yana cewa"Ameen little girl na ha'kura na huce gaba'daya".
Daga hakan kuma ya dinga b'arin jiki a kaina, komai ha'dama ha'dama yake yinsa har na gamsu k'arfin hali ya yi a kwanakin amma ba samu yake yi a waje ba. Domin duk kulafacina sai da na k'osa amma shi bai k'osa din ba".
Haka muka cigaba da gurgurawa ciikin rufin asiri. Dai-dai gwargwadon k'arfinsa yana yi mini komai.
Matsalar da ta fara damuna har cikin zuciyata rashin samun cikina gashi watanmu goma da aure Nasiba jiya ta haihu Ubaida kuwa har an saka ranar da za'a yi mata tiyata(c.s).
Da aka sanar mini da haihuwar yini na yi cikin sanyin jiki.
Sai kuma matsalar Rafi'a. Wata guda da kammala karatunta na digiri ta tattaro ta dawo gida gaba'daya.
Kusan ko yaushe a k'ofata take. Idan ina k'unshi sai ta hakince a falo da sunan kallo. Ko Tijjani ne ya dawo ba zata tashi ba, sai ma ta yi ta jansa da zancen makaranta su yi ta hirarsu. Ko idan ta ga ya fita sai ita ma ta bi shi su fita tare.
Ranar da na yi masa k'orafi ya balbale ni da sababin wai na raina shi, ban yarda da shi ba.
Na kame baki na yi shiru, kuma sai da na ba shi hakuri akan hakan.
Tunda ya ja ya tsaya ba shine yake zuwa wajenta ba, ba shi yake kiranta ba, tunda bana so ta zo mini gida to na hanata zuwa kawai.
Na rasa ta yadda zan kore ta domin dai gaskiyar magana uwarta tana mini kirki da alheri mai yawa a matsayin ta na babba. Bayan haka ita kanta Rafi'a din kirki ne da ita. Bai zame mata komai ba ta yi mini gyaran gida ba. Kawai ni yadda take shige wa Tijjani ne bana so, domin na riga da nasan shi akan lutayen mata.
Wadannan matsaloli sai suke neman sauya zaman aurenmu. Domin ni a k'arancin shekaruna dauka na yi Tijjani ne ya ki yi mini cikin kawai. Sannan yana son Rafia.
A hankali na fara janye masa, abubuwa suka fara sauya wa a tsakaninmu.
Na daina sauraronsa ko na saurare shi ma to kuwa sau daya ne shima ba cikin da'din rai ba.
Ranar da na dawo daga sunan Nasiba kuwa. Kuka na zauna na yi masa mai d'aga hankali k'warai da gaske. Ina yi ina ce wa "Akan me zaka matsa mini sai ka ta'ba ni bayan bana so, na riga na gane ba cikin nan zaka yi mini ba, dan haka na gaji da nukurkusata da kake yi babu sassauci babu kuma wani abu da zan samu."
Ya zuba mata ido yana kallon yadda take kuka bilhakki. Ya tafi tunanin shekarunta. Watan da ya shud'e ta ciki shekaru sha bakwai.
Ke nan akwai k'uruciya mai yawa a tare da ita. Bai kamata kuma ya biye mata ba, domin ya fahimci da dukkan zuciyarta take ganin shine bai mata ciki ba.
Ya numfasa ya saki gauron numfashi kafin ya ce "Asiya Allah ne fa mai bayarwa, kuma ba mantawa ya yi damu ba. Kika san tanadin da yake yi mana?"
Cikin kuka na ce "Ba wani, ni kawai ciki nake so, ai ko wacce ta haihu saboda mazansu suna sonsu, sai ni ce kawai saboda baka sona, kowa wani gani gani yake yi mini ba'a yi mini ciki ba".
Dariya ta so subuce masa, amma ya maze ya ce "Asiya zai yi wahalar gaske a samu wacce ake takarta irin yadda nake yi miki a cikinsu. Kin san da yawan yi ne sanadin samun ciki da yanzu kin haihu sau uku.
Amma shi samuwar ciki ai ikon Allah ne."
Da rawar murya na ce"Ba wani kawai dai ni ce baka so na samu ba, ga Ubaida nan yarinya da ita jibi za'a ciro mata d'a ko y'arsu, kai ma da su Nasiba ka aura ai da tuni ka yi musu.
Ina goge idona na ce "Wallahi na baka nan da wata d'aya, idan ban samu ciki ba to ba zan zauna ba".
Ya sake zuba mini ido cikin mamaki mai yawa. Ni kuwa ko d'ar ban ji ba.
Ya ha'diye komai ya ce "Shike nan Allah ka taimaki Tijjani ya yiwa Asiya Toro cikin y'an-uku".
Na yi maza na ce y'an uku tashi guda? Y'an biyu ko daya ma ya isa."
Ya fara ta'ba ni, na bige hannun na ce "Ni fa yau na gaji Wallahi".
Ya ce "To shike nan Asiya Toro Allah ya kai mu gobe, tunda ciki kike so ki sani fa babu ke babu hutu, amma na yarda ki huta yau din".
Ya numfasa ya ce "Na sani ai ba kya sona Asiya. Ban manta ba, amma na sakankace a d'an zaman da muka yi, zaki iya mini kawaici da alkunya akan abin da kika san zai musguna mini tunda kin sani sarai an jarrabe ni akan son ki. Amma yanzu na gane da gaske ba kya sona tunda akan idona kika k'i gaida Baban Tsakiya cikin mutunci duk da kashedin da nake yi miki da ido. Sannan kika gaida Jabir cikin falli har kina kiransa Yaya alhalin kin kankare zumuntar da ubansa."
Na yi shiru domin kam jikina ya yi tub'us.
Ya cigaba da ce wa "Saboda shi kina sonsa, kuma yafi ni ku'di shi yasa kike ce masa Yaya ni kuma ki gatsa Tijjani gatsal duk da na girme shi kuma ni ne mijin ki. Asiya ba zamu tab'a daidaita wa da ke ba alhalin kin ri'ke BAK'AK'EN TA'ADODI. Yanzu duk k'uruciyar ki ai k'iris ya rage ki yi sha bakwai. Kin san kuma hukuncin wacce ta bu'de baki ta ce mijinta ya sake ta ba tare da gamshasshen dalili ba. Sannan kina da ra'ayin ruk'au na k'ullaci. Hakan kuma ba siffar mace ta gari ba ce. Kamata ya yi zuciyar mace ta zama mai taushi da sassauci ba mai tauri da tsanani ba."
Na ji kunyar kalamansa mussaman akan J.
Na tabbatar shi ba na ce masa Yaya. Amma ban da yau ai nafi wata ban kama sunansa ba, sai dai na yi masa magana kawai. Domin na da'de da daina fa'da a dalilin kunya na kama ni tare da nauyin gatsa sunan nasa.
Na tura baki na juya baya. Cikin k'unk'uni na ce "To ai kai ma kana da Bak'ar Ta'ada din, akan me tun a ranar ba zaka fa'da mini laifina ba, sai kawai ka k'ulla ce ni, ka tsiri fishi. Ni ba Allan musuru ba, ta ina zan san kuskurena?"
Ya matso jikina ya ce "Da kina sona ai tun a lokacin zaki fahimci sauyin nawa, sai ki shawo kaina ki ririta ni, ki mantar da ni b'acin ran da nake ciki. Amma saboda am nothing to you ai share ni kika yi. Kika tattara kika yi wurgi da ni".
Na cuna baki na yi shiru. Ya mik'e dukkan k'afafuwan sa. Ya janyo ni ya kwantar a kai. Ya shiga wasa da gyararren gashina. Murya a dak'ushe tabbacin yana cikin kewa ya ce "Bana son abubuwan da kike yi a gabansu. Su din iyaye ne. Ta ko wacce fuska sune a sama da ke.
Zan yi hakuri da komai akan sha'anin ki, amma ban da na fito na fito da iyaye, bana so, ki bari."
Na yi shiru ban amsa ba.
Ya sassauta murya ya ce "kin yi shiru."
Na sake yin shiru still.
Ya zame ni daga jikinsa ya juya baya ya yi kwanciyarsa.
Ina ganin hakan ai kuwa na tak'ark'are na zunduma masa fallashasshen kukan da baya so.
Ina ce wa "Tunda juninka k'ullaci ne ka mayar da ni gidanmu kawai".
Ya juyo da azama ya ce "Asiya ki cigaba da wula'kanta ni. Amma ki sani komai zaki yi ni ba zan mayar da ke ba, domin ina son ki, ke da ba kya sona sai ki tafiyar ki, hakan kuma ba shine k'arshe farin-ciki a gare ni ba."
Na sassauta kukana domin na ga ya hassala sosai.
Na dinga yinsa kasa kasa irin mai cin rai din nan.
Da ya gaji da jin kukan nawa ya saka hannunsa ya ja ni jikinsa ya ce "Yi shiru Asiyata, amma ba zamu shirya ba sai kin ba ni hakuri dole".
Duk yadda na k'agu mu shirya fuska na yi da ce wa "Ai ban maka laifi ba. Sannan ba dan komai nake ce wa Jabir Yaya ba sai dan yana ce mini Yabi ne. Amma kai sai ka dinga ce mini Asiya Toro babu ko sha'awa ma".
Ina rufe baki ya ce "Har abada ba zan ce Yabi ba, idan ya so ba Tijjani kawai ba, ki fa'di cikakken sunan nawa Tijjani Yusuf Bulkachuwa! Marar kunya. Shine rannan kika yiwa yaro sababi akan ya k'ira ni da Tijjani to ke d'in kin saya ne bare ki ji ciwon wani bai saya ba. Kuma ni ban damu sai kin saya d'in ba".
Na nisa na saki ajiyar zuciya irin wacce ake yi idan an ci kuka sosai. Na ce "Ni fa tuni na samo maka sunan da zan fa'da maka, amma sai na haihu".
Maganar ta zo masa a bazata. Ya ru'ko ni ya ce "Kina son haihuwa ne Asiya?"
Da sauri na ce "Ina so sosai, domin duk wanda muka taso ko wacce ta haihu. Wadanda aka yi aurenmu tare Nasiba da Ubaida dukkansu ciki ne da su, ni ce kawai ba ni da shi".
Na fa'da da karyayyar murya.
Ya sassauta ya ce "Asiya haihuwa lokaci ne da sannu ke ma wataran zaki gan ki da naki cikin. Tunda kin daina guduna, sannan nima ina iyakacin k'ok'ari, kawai mu dinga addu'a".
Na ce "To. Ka ga Gwaggo ma ta ce ba zata zo gidan nan ba sai na haihu".
Ya rungume ni sosai ya ce "In sha Allah zaki haihu Asiyata. Mace kike so ko namiji?"
Kai tsaye na ce "Ni dai na samu cikin nafi so. Ko mai na haifa ina so ba ni da za'bi."
Ya yi dariya ya ce "Tom shike nan Allah zai bamu In sha Allah! Kawai ki kara zama jaruma, ko sau nawa za'a yi kada ki yi musu ko ki ce kin gaji".
Na ce "Da gaske idan na yi haka zan samu cikin ko dai wayo zaka yi mini?"
Ya k'yal-k'yale da dariya ya ce "Ba wani wayo gaskiya nake fa'da miki Asiyata".
Daga hakan kuma ya shiga kissing d'ina tare da zafafan sakonni masu rikita ni. Sai da ya tabbatar ya rura mini jiki. Sannan ya sake ni ya kwanta tare da ce wa "Au ashe baki ba ni ha'kuri ba fa, bamu shirya ba".
A hankali na ce ", Mun shirya mana, ba har ka yi dariya ba yanzu".
Ya ce "Ai ba ki bani hakurin da na ce ki ba ni ba".
Na fara kukan shagwaba, ya juyo ya ce "To fa'da mini a kunne na ji".
Cikin kuka kuka na ce "Allah ya baka hakuri".
Ina fa'din hakan ya rungume ni yana cewa"Ameen little girl na ha'kura na huce gaba'daya".
Daga hakan kuma ya dinga b'arin jiki a kaina, komai ha'dama ha'dama yake yinsa har na gamsu k'arfin hali ya yi a kwanakin amma ba samu yake yi a waje ba. Domin duk kulafacina sai da na k'osa amma shi bai k'osa din ba".
Haka muka cigaba da gurgurawa ciikin rufin asiri. Dai-dai gwargwadon k'arfinsa yana yi mini komai.
Matsalar da ta fara damuna har cikin zuciyata rashin samun cikina gashi watanmu goma da aure Nasiba jiya ta haihu Ubaida kuwa har an saka ranar da za'a yi mata tiyata(c.s).
Da aka sanar mini da haihuwar yini na yi cikin sanyin jiki.
Sai kuma matsalar Rafi'a. Wata guda da kammala karatunta na digiri ta tattaro ta dawo gida gaba'daya.
Kusan ko yaushe a k'ofata take. Idan ina k'unshi sai ta hakince a falo da sunan kallo. Ko Tijjani ne ya dawo ba zata tashi ba, sai ma ta yi ta jansa da zancen makaranta su yi ta hirarsu. Ko idan ta ga ya fita sai ita ma ta bi shi su fita tare.
Ranar da na yi masa k'orafi ya balbale ni da sababin wai na raina shi, ban yarda da shi ba.
Na kame baki na yi shiru, kuma sai da na ba shi hakuri akan hakan.
Tunda ya ja ya tsaya ba shine yake zuwa wajenta ba, ba shi yake kiranta ba, tunda bana so ta zo mini gida to na hanata zuwa kawai.
Na rasa ta yadda zan kore ta domin dai gaskiyar magana uwarta tana mini kirki da alheri mai yawa a matsayin ta na babba. Bayan haka ita kanta Rafi'a din kirki ne da ita. Bai zame mata komai ba ta yi mini gyaran gida ba. Kawai ni yadda take shige wa Tijjani ne bana so, domin na riga da nasan shi akan lutayen mata.
Wadannan matsaloli sai suke neman sauya zaman aurenmu. Domin ni a k'arancin shekaruna dauka na yi Tijjani ne ya ki yi mini cikin kawai. Sannan yana son Rafia.
A hankali na fara janye masa, abubuwa suka fara sauya wa a tsakaninmu.
Na daina sauraronsa ko na saurare shi ma to kuwa sau daya ne shima ba cikin da'din rai ba.
Ranar da na dawo daga sunan Nasiba kuwa. Kuka na zauna na yi masa mai d'aga hankali k'warai da gaske. Ina yi ina ce wa "Akan me zaka matsa mini sai ka ta'ba ni bayan bana so, na riga na gane ba cikin nan zaka yi mini ba, dan haka na gaji da nukurkusata da kake yi babu sassauci babu kuma wani abu da zan samu."
Ya zuba mata ido yana kallon yadda take kuka bilhakki. Ya tafi tunanin shekarunta. Watan da ya shud'e ta ciki shekaru sha bakwai.
Ke nan akwai k'uruciya mai yawa a tare da ita. Bai kamata kuma ya biye mata ba, domin ya fahimci da dukkan zuciyarta take ganin shine bai mata ciki ba.
Ya numfasa ya saki gauron numfashi kafin ya ce "Asiya Allah ne fa mai bayarwa, kuma ba mantawa ya yi damu ba. Kika san tanadin da yake yi mana?"
Cikin kuka na ce "Ba wani, ni kawai ciki nake so, ai ko wacce ta haihu saboda mazansu suna sonsu, sai ni ce kawai saboda baka sona, kowa wani gani gani yake yi mini ba'a yi mini ciki ba".
Dariya ta so subuce masa, amma ya maze ya ce "Asiya zai yi wahalar gaske a samu wacce ake takarta irin yadda nake yi miki a cikinsu. Kin san da yawan yi ne sanadin samun ciki da yanzu kin haihu sau uku.
Amma shi samuwar ciki ai ikon Allah ne."
Da rawar murya na ce"Ba wani kawai dai ni ce baka so na samu ba, ga Ubaida nan yarinya da ita jibi za'a ciro mata d'a ko y'arsu, kai ma da su Nasiba ka aura ai da tuni ka yi musu.
Ina goge idona na ce "Wallahi na baka nan da wata d'aya, idan ban samu ciki ba to ba zan zauna ba".
Ya sake zuba mini ido cikin mamaki mai yawa. Ni kuwa ko d'ar ban ji ba.
Ya ha'diye komai ya ce "Shike nan Allah ka taimaki Tijjani ya yiwa Asiya Toro cikin y'an-uku".
Na yi maza na ce y'an uku tashi guda? Y'an biyu ko daya ma ya isa."
Ya fara ta'ba ni, na bige hannun na ce "Ni fa yau na gaji Wallahi".
Ya ce "To shike nan Asiya Toro Allah ya kai mu gobe, tunda ciki kike so ki sani fa babu ke babu hutu, amma na yarda ki huta yau din".