Sashe 97
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.
Ta sake rank'wafawa da nufin yin abin da ta yi niyya. Ma'aikaciyar ta ce "A a Dada daure ki yi hakuri. A yanzu Asiya ba a hannunku take ba. Tana hannun gwamnati ne da kuma hukumar lafiya. Dan haka duk abin da za'a yi mata dole zai kasance k'arkashin kulawar hukumar asibiti ne. Bijire wa hakan kuma yana iya sawa mu gurfanar da mutum gaban kuliya. Dan haka ki yi ha'kuri ki bar hukuma ta yi aikinta.
Wannan karon kam a zabure ta ce "ke yarinya kar ki mini iyashege kin ji. Dan Allah falfala da gudu ki kirawo mini hukumar mu yi arangama domin mutuwa ce ka'dai zata hana ni matse wa Yabi mataccen nono marar amfani, ba ku da kuke yiwa masu jajayen kunne bauta ba."
Ta murmusa ka'dan ganin Dada ta kufula da yawa. Ta ce "Dada abin bana b'acin rai ba ne. Ki Fahimci bayanina. A da an rayu cikin duhun kan cewar nonon farko mai kalar rawaya matacce ne kuma mai illah. A yanzu da ilimi ya cika duniya masana kimiyya sun gano d'inbin amfanin da Allah ya ajiye a nonon uwa. Mussaman na awannin farko da haihuwa. Yana rigakafin ciwon hanta, k'oda, huhu. Yana hana tasirin ciwon k'yanda da tarin fuka, da shawara. Yana k'arawa jariri kaifin k'wak'walwa, yana kuma daidaita k'asusuwansu".
Dada ta dauki salati tare da cewa "Ni Binta ina ga ni da sauraron kinaya. To da kunsan da hakan amma kuka sake k'ak'alo allaurar da ake daukar watanni ana yiwa yara babu tausayi bare imani da sunan rigakafi ce. Yanzu wanne ne gaskiyar magana kenan?"
Malamar ta yi murmushi ta ce ko wanne gaskiya ne Dada".
Ta ce "To ku ri'ke gaskiyarku, amma ni ban yarda da ita ba, bare kuma na yi muku biyayya"
Da walwala ta ce "Shike nan Dada ki ri'ke fahimtarki. Amma tunda har aka kawo Asiya asibiti to wajibi ne abi ka'idojin hukumar lafiya. Idan ba hakan ba zamu sallame ku ne. Komai ya biyo baya kuma babu ruwanmu. Kafin haka kuma, zan rubuta tirjiyar da kuka yi, idan abu marar da'di ya biyo baya ke ce da d'aukar alhakin komai. Domin na tabbatar za ki ga ni".
Nan da nan Dada ta d'auki salati tare da fashe wa da kuka ta koma gefe tana ce wa "Yau ko da wa kike tak'ama sai na yi sharia da ke tunda kika ce zan ga ni."
Ita kuwa bata damu ba, da alamu ma dariya Dadan ta bata. Domin sai guntse bakinta take yi. Ta kuma d'ora mini yaron tana nuna mini yadda zan tallafe shi a duk sadda zan shayar da su gudun kada su dinga kware wa ko su kasa samun iska.
A lokacin da yaron ya fara tsotso wani irin rad'ad'i ya ratsa ni. Na zabura ta ce "Sannu".
Na kasa amasawa, kunyar idon su Babah ya hana na yi kwarmato. A daddafe ya sha. Ta dauke shi, ta dauko d'ayan.
Ya fara sha ke nan Tijjani ya iso da kayayyaki a hannunsa. Ya ci birki ya tsaya yana kallon yadda take rurrufe ido tana cije wa ga yaro yana sha. Farin cikin Asiya ta zama uwar y'ay'ansa har biyu tashi guda yana matu'kar saka shi tsumaye.
Amma ganin Dada na kuka ya takaita masa murnar da yake ciki.
Ya ajiye kayan a gefe ya isa kusa da da ita.
Yasa hannu ya ru'ko hannunta da take share hawaye. A tausashe ya ce "Dada kukan me kike yi haka ne? Ina ce d'azu kika dinga rangwad'a murnar alherin da ya samu a cikin alhalinki na samun tagwaye?"
Cikin kuka mai yawa ta ce "Ayyah mai sunan manya ai wannan ja'irar yarinya tana neman mayar mini da murnar tawa ciki. Ba yadda ban yi ba kada ta bawa yaran nan dattin nono amma sai da ta kafe ta basu suka shanye. Idan an yi sa'a sun rayu, to tabbas zasu tashi da kukan da baya jin rarrashi ga yawan kumburin ciki, sannan mafi muni suna iya samun tawaya a hankalinsu". Ta ke ce da kuka mai tsananin gaske.
Fargaba ta shige shi ainun. A ki'dime ya ce "jariran aka yiwa sanadin raunin k'wak'walwa Dada?"
Ta kad'a masa kai tabbacin eh. Tare da ce wa "Kuma Wallahi tunda ta ce mini zan ga ni, sai na yi shari'a da ita ko da me take tak'ama kuwa. Ba zata lahanta mini tattaba kunne, sannan ta bini da mugun k'ulli na kuma ha'kura ba. Ko waye ubanta a garin Toro da kewaye sai mun je gaban gatan marar gata wato kuliya".
Ya sake ta ya isa gaban su yana leka yadda a ke bawa yaron nono. A gigice ya ce "Baiwar Allah ya zaki dage sai sun sha abin da zai zame musu illah?"
Ya fara k'ok'arin karb'e yaron.
Babah ta Bulkachuwa ta yi wani irin tari mai kama da kashedi. Nan da nan ya ankara ya fahimci gargadi ta yi masa.
Ya d'aure ya saki yaron. Ya koma gefe amma zuciyarsa ta dinga wani irin tsalle.
Dada kuma ta sake tsananta kukan tana fa'din "Duk wannan iyakacin da aka nuna mini akan y'ay'an nan baki ji ciwo ba ashe? Ba ki hana ta ci mutuncin uwarki ba, baki hana ta nakasa rayuwar y'an mala'ikun Lillahi ba. Shi ya zo zai kwatar mana yancinmu ni da su shine zaki hana shi?
Eh lallai! To ki je na barwa hukumar asibitin ke, ranar da zamu yi shari'a da su ki zame musu shaida ki kwaye wa uwarki da jikokinki baya".
Ta juya ta fice tana kuka bilhakki.
Yayin da Babah da Inna da kuma Mama suka bita da nufin lallashi da ban baki a gare ta.
D'akin ya yi saura daga mu sai Yaya Ummi.
Ya d'auki yaron ya rungume shi tsam tsam. Yana ta tofa masa addu'ar da ta zo bakinsa. Ya kalle ni ya ce "Sannu Asiya! Ubangiji ya yi miki albarka, ya baki lafiya, ya baki hakuri da kuma juriyar raino da tarbiya".
Na kalle shi ina jin wata irin soyayyarsa na kekketa ni fiye da ko wanne lokaci. Wata'kila kuma kasancewar sa uban y'ay'an da nake jin kaunarsu har a cikin b'argona yana da alak'a da sake jin ninkin soyayyar sa.
Na murmusa na masa ameen a zuciyata.
Ya mik'awa Yaya Ummi wanda yake hannunsa ya karbi d'aya yaron da ya kammala sha yanzu a hannun malamar.
Cikin nutsuwa ta kalle shi ta ce "Mr Tijjani kada Kaka ta rikita ka." Ta shiga fado masa muhimmancin fara bawa yaro nonon uwa a farkon awanninsa a duniya. Ta sake ce wa "Tunda mu musulmai ne mun yi sa'a kuma muna d'abbaka sunnar manzo. Da zarar uwa ko uba sun tauna dabino sun guntsawa yaronsu a baki bayan sun yi Bismillah. Ba abin da zai fi dace wa da lafiyarsa illah wannan nono da mutanan jiya suka tafi a fahimtar ce wa cuta ce. Babban sirrika ne da Ubangiji ya zuba a ciki".
Ya gyada kai cike da gamsuwa. Ya yi mata godiya sosai tare da bata ha'kuri akan maganganun Dada. Ta murmusa ta ce "Ai babu komai nima kafin na fito sai da muka haura da tawa kakar. Sai ana yi musu uzziri. Da zarar sun kai shekarun girma irin haka, sai an sake yin hakuri da sha'aninsu ana mayar da komai zasu ce a matsayin girma ne. Shi kuwa tsufa ba k'aramin nauyi ne da shi ba. Domin Allah da kansa sai da ya yi ta jan kunnenmu a cikin kura'aninsa mai girma akan idan iyayenmu suka kai shekarun girma kada mu fa'da musu munanan kalamai, komai zasu yi mana, kada mu ce musu uffan, balle a yi sa'insa da su".
Ya sake ce wa "Haka ne. Na gode sosai".
✍️.
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.
*Masu fitarwa bazance muku komai ba. Kowa ya yi mai kyau kansa.*
*Wacce ta karanta mini labarin nan bata biya ba tabbas ina binta bashi*.
*Masu jiran na kammala su had'a mini document, kada ku yi hakan, na ro'ke ki a littafaina na baya amma still baku ji ba.*
*Bana son a had'a mini document*
*Bana son a had'a mini document*
*Wacce kuwa ta hada na kai ta k'ara wajen Ubangiji*.
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*.
Ta sake rank'wafawa da nufin yin abin da ta yi niyya. Ma'aikaciyar ta ce "A a Dada daure ki yi hakuri. A yanzu Asiya ba a hannunku take ba. Tana hannun gwamnati ne da kuma hukumar lafiya. Dan haka duk abin da za'a yi mata dole zai kasance k'arkashin kulawar hukumar asibiti ne. Bijire wa hakan kuma yana iya sawa mu gurfanar da mutum gaban kuliya. Dan haka ki yi ha'kuri ki bar hukuma ta yi aikinta.
Wannan karon kam a zabure ta ce "ke yarinya kar ki mini iyashege kin ji. Dan Allah falfala da gudu ki kirawo mini hukumar mu yi arangama domin mutuwa ce ka'dai zata hana ni matse wa Yabi mataccen nono marar amfani, ba ku da kuke yiwa masu jajayen kunne bauta ba."
Ta murmusa ka'dan ganin Dada ta kufula da yawa. Ta ce "Dada abin bana b'acin rai ba ne. Ki Fahimci bayanina. A da an rayu cikin duhun kan cewar nonon farko mai kalar rawaya matacce ne kuma mai illah. A yanzu da ilimi ya cika duniya masana kimiyya sun gano d'inbin amfanin da Allah ya ajiye a nonon uwa. Mussaman na awannin farko da haihuwa. Yana rigakafin ciwon hanta, k'oda, huhu. Yana hana tasirin ciwon k'yanda da tarin fuka, da shawara. Yana k'arawa jariri kaifin k'wak'walwa, yana kuma daidaita k'asusuwansu".
Dada ta dauki salati tare da cewa "Ni Binta ina ga ni da sauraron kinaya. To da kunsan da hakan amma kuka sake k'ak'alo allaurar da ake daukar watanni ana yiwa yara babu tausayi bare imani da sunan rigakafi ce. Yanzu wanne ne gaskiyar magana kenan?"
Malamar ta yi murmushi ta ce ko wanne gaskiya ne Dada".
Ta ce "To ku ri'ke gaskiyarku, amma ni ban yarda da ita ba, bare kuma na yi muku biyayya"
Da walwala ta ce "Shike nan Dada ki ri'ke fahimtarki. Amma tunda har aka kawo Asiya asibiti to wajibi ne abi ka'idojin hukumar lafiya. Idan ba hakan ba zamu sallame ku ne. Komai ya biyo baya kuma babu ruwanmu. Kafin haka kuma, zan rubuta tirjiyar da kuka yi, idan abu marar da'di ya biyo baya ke ce da d'aukar alhakin komai. Domin na tabbatar za ki ga ni".
Nan da nan Dada ta d'auki salati tare da fashe wa da kuka ta koma gefe tana ce wa "Yau ko da wa kike tak'ama sai na yi sharia da ke tunda kika ce zan ga ni."
Ita kuwa bata damu ba, da alamu ma dariya Dadan ta bata. Domin sai guntse bakinta take yi. Ta kuma d'ora mini yaron tana nuna mini yadda zan tallafe shi a duk sadda zan shayar da su gudun kada su dinga kware wa ko su kasa samun iska.
A lokacin da yaron ya fara tsotso wani irin rad'ad'i ya ratsa ni. Na zabura ta ce "Sannu".
Na kasa amasawa, kunyar idon su Babah ya hana na yi kwarmato. A daddafe ya sha. Ta dauke shi, ta dauko d'ayan.
Ya fara sha ke nan Tijjani ya iso da kayayyaki a hannunsa. Ya ci birki ya tsaya yana kallon yadda take rurrufe ido tana cije wa ga yaro yana sha. Farin cikin Asiya ta zama uwar y'ay'ansa har biyu tashi guda yana matu'kar saka shi tsumaye.
Amma ganin Dada na kuka ya takaita masa murnar da yake ciki.
Ya ajiye kayan a gefe ya isa kusa da da ita.
Yasa hannu ya ru'ko hannunta da take share hawaye. A tausashe ya ce "Dada kukan me kike yi haka ne? Ina ce d'azu kika dinga rangwad'a murnar alherin da ya samu a cikin alhalinki na samun tagwaye?"
Cikin kuka mai yawa ta ce "Ayyah mai sunan manya ai wannan ja'irar yarinya tana neman mayar mini da murnar tawa ciki. Ba yadda ban yi ba kada ta bawa yaran nan dattin nono amma sai da ta kafe ta basu suka shanye. Idan an yi sa'a sun rayu, to tabbas zasu tashi da kukan da baya jin rarrashi ga yawan kumburin ciki, sannan mafi muni suna iya samun tawaya a hankalinsu". Ta ke ce da kuka mai tsananin gaske.
Fargaba ta shige shi ainun. A ki'dime ya ce "jariran aka yiwa sanadin raunin k'wak'walwa Dada?"
Ta kad'a masa kai tabbacin eh. Tare da ce wa "Kuma Wallahi tunda ta ce mini zan ga ni, sai na yi shari'a da ita ko da me take tak'ama kuwa. Ba zata lahanta mini tattaba kunne, sannan ta bini da mugun k'ulli na kuma ha'kura ba. Ko waye ubanta a garin Toro da kewaye sai mun je gaban gatan marar gata wato kuliya".
Ya sake ta ya isa gaban su yana leka yadda a ke bawa yaron nono. A gigice ya ce "Baiwar Allah ya zaki dage sai sun sha abin da zai zame musu illah?"
Ya fara k'ok'arin karb'e yaron.
Babah ta Bulkachuwa ta yi wani irin tari mai kama da kashedi. Nan da nan ya ankara ya fahimci gargadi ta yi masa.
Ya d'aure ya saki yaron. Ya koma gefe amma zuciyarsa ta dinga wani irin tsalle.
Dada kuma ta sake tsananta kukan tana fa'din "Duk wannan iyakacin da aka nuna mini akan y'ay'an nan baki ji ciwo ba ashe? Ba ki hana ta ci mutuncin uwarki ba, baki hana ta nakasa rayuwar y'an mala'ikun Lillahi ba. Shi ya zo zai kwatar mana yancinmu ni da su shine zaki hana shi?
Eh lallai! To ki je na barwa hukumar asibitin ke, ranar da zamu yi shari'a da su ki zame musu shaida ki kwaye wa uwarki da jikokinki baya".
Ta juya ta fice tana kuka bilhakki.
Yayin da Babah da Inna da kuma Mama suka bita da nufin lallashi da ban baki a gare ta.
D'akin ya yi saura daga mu sai Yaya Ummi.
Ya d'auki yaron ya rungume shi tsam tsam. Yana ta tofa masa addu'ar da ta zo bakinsa. Ya kalle ni ya ce "Sannu Asiya! Ubangiji ya yi miki albarka, ya baki lafiya, ya baki hakuri da kuma juriyar raino da tarbiya".
Na kalle shi ina jin wata irin soyayyarsa na kekketa ni fiye da ko wanne lokaci. Wata'kila kuma kasancewar sa uban y'ay'an da nake jin kaunarsu har a cikin b'argona yana da alak'a da sake jin ninkin soyayyar sa.
Na murmusa na masa ameen a zuciyata.
Ya mik'awa Yaya Ummi wanda yake hannunsa ya karbi d'aya yaron da ya kammala sha yanzu a hannun malamar.
Cikin nutsuwa ta kalle shi ta ce "Mr Tijjani kada Kaka ta rikita ka." Ta shiga fado masa muhimmancin fara bawa yaro nonon uwa a farkon awanninsa a duniya. Ta sake ce wa "Tunda mu musulmai ne mun yi sa'a kuma muna d'abbaka sunnar manzo. Da zarar uwa ko uba sun tauna dabino sun guntsawa yaronsu a baki bayan sun yi Bismillah. Ba abin da zai fi dace wa da lafiyarsa illah wannan nono da mutanan jiya suka tafi a fahimtar ce wa cuta ce. Babban sirrika ne da Ubangiji ya zuba a ciki".
Ya gyada kai cike da gamsuwa. Ya yi mata godiya sosai tare da bata ha'kuri akan maganganun Dada. Ta murmusa ta ce "Ai babu komai nima kafin na fito sai da muka haura da tawa kakar. Sai ana yi musu uzziri. Da zarar sun kai shekarun girma irin haka, sai an sake yin hakuri da sha'aninsu ana mayar da komai zasu ce a matsayin girma ne. Shi kuwa tsufa ba k'aramin nauyi ne da shi ba. Domin Allah da kansa sai da ya yi ta jan kunnenmu a cikin kura'aninsa mai girma akan idan iyayenmu suka kai shekarun girma kada mu fa'da musu munanan kalamai, komai zasu yi mana, kada mu ce musu uffan, balle a yi sa'insa da su".
Ya sake ce wa "Haka ne. Na gode sosai".
✍️.
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.
*Masu fitarwa bazance muku komai ba. Kowa ya yi mai kyau kansa.*
*Wacce ta karanta mini labarin nan bata biya ba tabbas ina binta bashi*.
*Masu jiran na kammala su had'a mini document, kada ku yi hakan, na ro'ke ki a littafaina na baya amma still baku ji ba.*
*Bana son a had'a mini document*
*Bana son a had'a mini document*
*Wacce kuwa ta hada na kai ta k'ara wajen Ubangiji*.