Sashe 123
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ya dai gaishe ta a gajarce.
Tsawon lokaci yana zaune. Rigarsa ta jike ta gaba saboda yadda zurlfa take keto masa tamkar mai hadiyar kunama.
Fiye da shudewar mintina talatin yana zaune ba ya um ba ya um um. Gabadaya Babah ta shafa'a da miyar da take yi wa Dada.
Sai tashin kauri suka ji a hancinansu. Da azama ta yunkura ta sauke. Sannan ta janye wutar ta kashe.
A tausashe ta ce "Dada me za'a d'ora kuma?"
Cikin bagararwa Dadan ta ce "Kashe kawai."
Domin bata sakar mata fuska a dalilin tana taya autarta Maryo fishin cin mutuncin da suke k'irarin ta yi mata da ta je wajenta takanas.
Ta fito da garwashin. Ta kashe sannan ta yayyafa ruwa a murhun ta kashe shi gabad'aya.
Ta dawo ta zauna. Sannu a hankali Tijjani ya fara dawowa cikin nutsuwarsa. Gumin da yake yi, ya fara tsane wa. Mintina kad'an ya mik'e ya ce "Zan tafi. Babah yaushe zaki koma?"
Da mamaki ta ce "Tukunna."
Da hanzari ta fice yana fad'in ",Na tafi Dada".
Bai ko bi takan Nasiba ba, bare ya yi mata sallama.
Babah ta kasa gane al'amarin domin tamkar mai jinnu haka yake canjawa. Ta hakura ta kudiri aniyar tsananta addu'a domin ta yi imanin Ubangiji ba zai juyar da addu'ar ta ba.
Sannu a hankali kwanaki suna ta shude wa har ya zama saura kwanaki goma auren da ake ta cece kuce a kansa.
Lefe ne kawai ba a kai ba, an yanke shawarar idan ta je gidansa ya bata domin zuciyoyi sun kai kololuwa wajen fusata.
*
Da safe bayan ya tafi da yara makaranta, shi kuma ya wuce Dass. Ina zaune a falo ni kad'ai, kuka kawai nake yi, irin kukan nan da yake zuwa ko da baka so ba. Gabad'aya duniyar ta mini zafi. Idan na tuna saura kwanaki 'kalilan na fara raba Bulkachuwa da Nasiba sai na ji ina fatan mutuwa ta dauke ni kawai.
Na kifa kai a hannun kujera ina kuka tamkar mai wake, domin bilhakki na Bude baki nake yi.
Ba zato waya ta hau kuwwa. Na mika hannu a dalilin Gwaggo kawai na saka taken da yake tashi.
Sai da na yi jarumtar shanye kukan sannan na dauka.
Murya ta kawai ta ji. Ta tausasa harshe ta ce "Kuka kike yi ne Yabi?"
Haka kawai ta fad'a na rushe da kuka mai tsananin gaske.
Cikin kuka sosai na ce "Gwoggo ba zan iya ba, zuciyata na mini ciwo, tana zafi mai radadi."
Ta numfasa ta ce ",Zaki iya mana. Ai ba a kanki aka fara yin kishiya ba, ba kuma za'a kare a kanki ba".
Da rawar murya na ce "Amma dai kishiya irin tawa Gwaggo zan zama cikin mutane kad'an da aka yiwa irin ta. Mena yiwa Tijjani da zai mini irin wannan cin mutuncin a rayuwata?"
Da taushi sosai ta ce "Nutsu ki ji ni! Shawara zan ba ki, ba umarni ba, kinsan umarni wajibi ne ki mini biyayya. Ita kuwa shawara sai kin so za ki bi. Amma idan kika bi zai fi miki alheri fiye da barin."
Ta nisa tare da ce wa "Duk runtsi kada ki ce mijinki ya sake ki matukar bai keta haddi da alfarmar shari'a ko ta aure ba. Sannan ki yi dukkan iyawar ki, kada ki nuna damuwa ko gazawarki a gaban mahaifin ki Yabi. Ya damu da halin da kike ciki. Ki daure, ba abin da ba zai wuce ba, sai ikon Allah".
Na yi shiru illah kukan da nake yi mata tamkar zan shid'e. Cikin jarumta ainun ta ce "Allah ya sassauta miki, ba komai kin ji. To ban da ma kin saka damuwa a ranki ai bai kamata al'amarin duniya ya susuta ki irin haka ba Yabi. Kinsan kalubalen da yake gaban ki kuwa?
Kwanciyar kabari kad'ai da muna saka ta a gabanmu da bamu bari kalubalen duniya ya kidima mu ya shagaltar da mu yiwa kanmu tanadin kwanciyar da Ubangiji kad'ai yasan adadin tsayin ta ba.
Me yasa kishi ya ke sawa mu manta Annabi ya ce mu yawaita sadaka, sallah da istigifari. Domin ya hango mataye da yawa yan'wuta ne. Kuma tsananta kishi alamu ne, na mace ta barranta kanta daga ayar da Ubangiji ya saukar. Wacce kuwa ta barranta daga imani da ayar Allah. La budda tana cikin hatsarin kafirta matukar bata gaggauta tuba tare da yin hak'uri cikin hukuncin da Ubangiji ya halasta ba."
Tsikar jikina ta zuba k'warai da gaske. Na sassauta kukan da nake yi. Ta sake sassauta wa ta ce "Ki yawaita karatun kura'ani domin karanta shi kad'ai yana wanke tsatsar zuciya. Ki yawaita sallah. Ki rungumi y'aya'nki da sana'ar ki. Miji kuwa kada ki zalunce shi, kada ki tauye shi, kada ki hana shi samun nutsuwa da ke ko a gidansa. Illah iyaka ki sassauta zazzafar soyayyar da zata saka ki halaka, ki kuma halaka shi".
Na numfasa tare da ajiyar zuciya mai nauyi na ce "To"
Ta shiga jero mini albarka. Ta ce "Idan akwai abin da yafi albarka da yafiyar uwa na roki Ubangiji ya yi miki da ke da zuriarki. Idan har Ubangiji baya juyar da addu'ar uwa akan d'anta , to alafamar ma'aiki ba zaki wulakanta a wannan duniyar ba. Duk inda rayuwa zata kai ki, komin tsanani zaki zama cikin rufin asiri mai yawa. Da ikon Allah wani mahaluki ba zai ga gazawar ki ba Yabi".
Da rawar murya na ce "Na gode Gwaggo! Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana mai albarka".
Na jiyo ajiyar zuciyarra alamun ta samu nutsuwa da yadda na karbi ban hak'uriinta. Ta ce "Ameen, ina tagwaye?"
Na ce "suna makaranta".
"To ke me kike yi yanzu?"
Ta tambayar cike da soyayya mai yawa.
A hankali na ce "A zaune kawai nake Gwaggo ".
"Tashi ki yi nafila, ki daina bari wannan lokacin mai tsada na wuce ki, baki yi salatul duha ba. Kinsan duk abin da Ubangiji ya rantse da shi mai falala ne, mai daraja ne. Allah ya ce "Wad Duha!
Lalle ki yawaita neman gafara da rahamar Allah a wannan lokacin, Ubangiji baya juyar da addu'ar da aka yi ta a wannan sa'ar sai dai jinkiri, ko ya mussnya maka fiye da abin da ka roka alheri".
Na ce "To!Da budaddiyar murya.
Ina jin soyayyar Gwaggo na sake tunbatsa a dukkan sassan jikina. Kwalla ta zubo mini wacce bata ciwo ba ce, ta tausayinta ne, tare da tausayin wacce duk bata girma da uwa mahaifiya ba. Tabbas soyayyar uwa ita ce mafi kololuwa a wannan duniyar. Muka yi sallama na tashi na dauro alwallah, na yi walaha. Akan sallayar barci ya sure ni, irin wanda na jima ban samu yin sa ba.
Akai Babah take yi mini waya, tana tambayar lafiyata da lafiyar yara. Na dinga mamakin yadda ta sauko. Na sani tana sona. Amma a kwanakin baya gabadaya ta canja mini. Yanzu kuma ta dawo mini Babah tawa Mai kaunata. Na dinga mamakin haka, da na ga kaina zai dauki caji Sau kawai nayi Hamdala a raiana tare da rok'on Ubangiji ya sake tsare mu daga sharrin masu tofi a cikin kulle kulle.
Tsawon lokaci yana zaune. Rigarsa ta jike ta gaba saboda yadda zurlfa take keto masa tamkar mai hadiyar kunama.
Fiye da shudewar mintina talatin yana zaune ba ya um ba ya um um. Gabadaya Babah ta shafa'a da miyar da take yi wa Dada.
Sai tashin kauri suka ji a hancinansu. Da azama ta yunkura ta sauke. Sannan ta janye wutar ta kashe.
A tausashe ta ce "Dada me za'a d'ora kuma?"
Cikin bagararwa Dadan ta ce "Kashe kawai."
Domin bata sakar mata fuska a dalilin tana taya autarta Maryo fishin cin mutuncin da suke k'irarin ta yi mata da ta je wajenta takanas.
Ta fito da garwashin. Ta kashe sannan ta yayyafa ruwa a murhun ta kashe shi gabad'aya.
Ta dawo ta zauna. Sannu a hankali Tijjani ya fara dawowa cikin nutsuwarsa. Gumin da yake yi, ya fara tsane wa. Mintina kad'an ya mik'e ya ce "Zan tafi. Babah yaushe zaki koma?"
Da mamaki ta ce "Tukunna."
Da hanzari ta fice yana fad'in ",Na tafi Dada".
Bai ko bi takan Nasiba ba, bare ya yi mata sallama.
Babah ta kasa gane al'amarin domin tamkar mai jinnu haka yake canjawa. Ta hakura ta kudiri aniyar tsananta addu'a domin ta yi imanin Ubangiji ba zai juyar da addu'ar ta ba.
Sannu a hankali kwanaki suna ta shude wa har ya zama saura kwanaki goma auren da ake ta cece kuce a kansa.
Lefe ne kawai ba a kai ba, an yanke shawarar idan ta je gidansa ya bata domin zuciyoyi sun kai kololuwa wajen fusata.
*
Da safe bayan ya tafi da yara makaranta, shi kuma ya wuce Dass. Ina zaune a falo ni kad'ai, kuka kawai nake yi, irin kukan nan da yake zuwa ko da baka so ba. Gabad'aya duniyar ta mini zafi. Idan na tuna saura kwanaki 'kalilan na fara raba Bulkachuwa da Nasiba sai na ji ina fatan mutuwa ta dauke ni kawai.
Na kifa kai a hannun kujera ina kuka tamkar mai wake, domin bilhakki na Bude baki nake yi.
Ba zato waya ta hau kuwwa. Na mika hannu a dalilin Gwaggo kawai na saka taken da yake tashi.
Sai da na yi jarumtar shanye kukan sannan na dauka.
Murya ta kawai ta ji. Ta tausasa harshe ta ce "Kuka kike yi ne Yabi?"
Haka kawai ta fad'a na rushe da kuka mai tsananin gaske.
Cikin kuka sosai na ce "Gwoggo ba zan iya ba, zuciyata na mini ciwo, tana zafi mai radadi."
Ta numfasa ta ce ",Zaki iya mana. Ai ba a kanki aka fara yin kishiya ba, ba kuma za'a kare a kanki ba".
Da rawar murya na ce "Amma dai kishiya irin tawa Gwaggo zan zama cikin mutane kad'an da aka yiwa irin ta. Mena yiwa Tijjani da zai mini irin wannan cin mutuncin a rayuwata?"
Da taushi sosai ta ce "Nutsu ki ji ni! Shawara zan ba ki, ba umarni ba, kinsan umarni wajibi ne ki mini biyayya. Ita kuwa shawara sai kin so za ki bi. Amma idan kika bi zai fi miki alheri fiye da barin."
Ta nisa tare da ce wa "Duk runtsi kada ki ce mijinki ya sake ki matukar bai keta haddi da alfarmar shari'a ko ta aure ba. Sannan ki yi dukkan iyawar ki, kada ki nuna damuwa ko gazawarki a gaban mahaifin ki Yabi. Ya damu da halin da kike ciki. Ki daure, ba abin da ba zai wuce ba, sai ikon Allah".
Na yi shiru illah kukan da nake yi mata tamkar zan shid'e. Cikin jarumta ainun ta ce "Allah ya sassauta miki, ba komai kin ji. To ban da ma kin saka damuwa a ranki ai bai kamata al'amarin duniya ya susuta ki irin haka ba Yabi. Kinsan kalubalen da yake gaban ki kuwa?
Kwanciyar kabari kad'ai da muna saka ta a gabanmu da bamu bari kalubalen duniya ya kidima mu ya shagaltar da mu yiwa kanmu tanadin kwanciyar da Ubangiji kad'ai yasan adadin tsayin ta ba.
Me yasa kishi ya ke sawa mu manta Annabi ya ce mu yawaita sadaka, sallah da istigifari. Domin ya hango mataye da yawa yan'wuta ne. Kuma tsananta kishi alamu ne, na mace ta barranta kanta daga ayar da Ubangiji ya saukar. Wacce kuwa ta barranta daga imani da ayar Allah. La budda tana cikin hatsarin kafirta matukar bata gaggauta tuba tare da yin hak'uri cikin hukuncin da Ubangiji ya halasta ba."
Tsikar jikina ta zuba k'warai da gaske. Na sassauta kukan da nake yi. Ta sake sassauta wa ta ce "Ki yawaita karatun kura'ani domin karanta shi kad'ai yana wanke tsatsar zuciya. Ki yawaita sallah. Ki rungumi y'aya'nki da sana'ar ki. Miji kuwa kada ki zalunce shi, kada ki tauye shi, kada ki hana shi samun nutsuwa da ke ko a gidansa. Illah iyaka ki sassauta zazzafar soyayyar da zata saka ki halaka, ki kuma halaka shi".
Na numfasa tare da ajiyar zuciya mai nauyi na ce "To"
Ta shiga jero mini albarka. Ta ce "Idan akwai abin da yafi albarka da yafiyar uwa na roki Ubangiji ya yi miki da ke da zuriarki. Idan har Ubangiji baya juyar da addu'ar uwa akan d'anta , to alafamar ma'aiki ba zaki wulakanta a wannan duniyar ba. Duk inda rayuwa zata kai ki, komin tsanani zaki zama cikin rufin asiri mai yawa. Da ikon Allah wani mahaluki ba zai ga gazawar ki ba Yabi".
Da rawar murya na ce "Na gode Gwaggo! Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana mai albarka".
Na jiyo ajiyar zuciyarra alamun ta samu nutsuwa da yadda na karbi ban hak'uriinta. Ta ce "Ameen, ina tagwaye?"
Na ce "suna makaranta".
"To ke me kike yi yanzu?"
Ta tambayar cike da soyayya mai yawa.
A hankali na ce "A zaune kawai nake Gwaggo ".
"Tashi ki yi nafila, ki daina bari wannan lokacin mai tsada na wuce ki, baki yi salatul duha ba. Kinsan duk abin da Ubangiji ya rantse da shi mai falala ne, mai daraja ne. Allah ya ce "Wad Duha!
Lalle ki yawaita neman gafara da rahamar Allah a wannan lokacin, Ubangiji baya juyar da addu'ar da aka yi ta a wannan sa'ar sai dai jinkiri, ko ya mussnya maka fiye da abin da ka roka alheri".
Na ce "To!Da budaddiyar murya.
Ina jin soyayyar Gwaggo na sake tunbatsa a dukkan sassan jikina. Kwalla ta zubo mini wacce bata ciwo ba ce, ta tausayinta ne, tare da tausayin wacce duk bata girma da uwa mahaifiya ba. Tabbas soyayyar uwa ita ce mafi kololuwa a wannan duniyar. Muka yi sallama na tashi na dauro alwallah, na yi walaha. Akan sallayar barci ya sure ni, irin wanda na jima ban samu yin sa ba.
Akai Babah take yi mini waya, tana tambayar lafiyata da lafiyar yara. Na dinga mamakin yadda ta sauko. Na sani tana sona. Amma a kwanakin baya gabadaya ta canja mini. Yanzu kuma ta dawo mini Babah tawa Mai kaunata. Na dinga mamakin haka, da na ga kaina zai dauki caji Sau kawai nayi Hamdala a raiana tare da rok'on Ubangiji ya sake tsare mu daga sharrin masu tofi a cikin kulle kulle.