← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 146

Sashe 60

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 11 min read

Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
*Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*.
✍️
*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUN KI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*

*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES.*

*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

Tsawon lokaci kafin su samu na yi shiru.
A kokarin Dada na son na warware sosai, sai ta fasa tafiyar ta ce ya yi tafiyarsa sai yamma ya dawo ya mayar da ita gida.
Ya fita, sai kuma ya bu'de baki ya ce"Asiya".
Na yi shiru kamar ban ji ba.
Dada ta sassauta ta ce "Kiran ki yake yi fa Yabi.
Ki na son ki k'one ne? Girman sa yawa ne da shi a wajen ki fa".
Na tashi bayan na cuna baki tamkar na buta.
Da fishi sosai na tsaya a gabansa.
A sanyaye kuma murya k'asa ya ce "Zan je na samo ko kifi ne, ki yi girki dan Allah".
Nan da nan na ce "Wallahi bazan dafa da kai ba".
Ya ce "Shike nan ki yi muku. Hakan ma na gode sosai".
Ya fita na bishi da harara. Ba'kin cikin yadda na takarkare na yi masa doya da k'wai ya k'i ci, ba k'aramin cizo na yake yi ba har yanzu.
Sannan girikin da ya sanya aka shigar mini kicin aka yi masa, sai ya gane ni ba irin matan da za'a yi musu hakan ba ne.
Bai wani jima ba, ya dawo. Sai da ya shiga kicin din sannan ya fito ya yi dakina.
Dada ta zuba mini ido alamun na tashi na bi shi.
Akan dole na je din.
Ya mik'o mini leda mai d'auke da sink'in sabulun wanka da kwalin TURAREN
Ismiyaki.
Na kar'ba galala.
Ya ce "Idan zata tafi sai ki bata".
Na gatsina baki na ajiye a bakin gadon ban ce komai ba, na fita na bar shi a tsaye, ya yi wani iri abin tausayi!.
Ya fito ya dan tsokani Dada sannan ya fice.
Zafi ya sanya na yiwa Dada shimfida a baranda.
Ta fito, muna hirarmu ina gyaran kayan miya.
Ina tunanin artabun da zan yi da attaruhu yayin greting. Don kuwa indai na murtsika attaruhu sai na kwana na yini hannuna na yin mini zugi.
Kwatsam aka kawo wuta. Cikin karambani da giggiwa na ha'da bilandar na fara markade.
Sai da na zuba shinkafa a dalilin ruwa ya tafaso.
Sannan na koma wajen Dada.
Da murmushi ta ce "Oh ashe dai da rabon za'a samu mai tu'amalli da injin markade na zamani a jikokina".
Na yi dariya tare da cewa "Dada kenan.
Bari na zauna ki d'ora mini karatu, ina kewar karatun ki."
Ta gyatta, na zauna kusa da ita.
Ta ce "Tunda Ubangiji ya sanya na ga auren ki har ga ni a gidan ki.
To zan 'dora miki karatun da har abada kin wuce yin boranci a idon namiji. Ban ta'ba koya wa kowa wannan addu'ar ba, saboda jarraba namiji ake yi da ita k'warai da gaske. Kema dan ina son ki tsare mijin ki, daga sharholiya ne!".
Ban ce komai ba.
Ta yi waiwaye dan ta sake samun tabbacin babu me jin abin da zata furta.
Ta matso kusa da ni ainun.
Murya k'asa kasa ta ce "A yayin da kuka shiga mayafin aure sai ki yi Bismillah ki ce "Allah daraja, MA'AIKIN Allah daraja a taimake ni akan aure. Zan jarraba y'an maza wane.. Ibnu wance.
Ki kamo ainihin sunan sa da sunan babar taku, sai ki tofo yawun bakinki akan yatsan sai ki yi matsi da wannan yawun addu'ar. Amma a zuci, zaki yi fa". Ta fa'da da dukkan zuciyar ta.
Duk da na saba jin karatun Dada wannan ya yi matu'kar sanya ni mamaki da dariya.
Amma na sanya jarumta na maze, na yi k'asa da kaina a zuwan kunya ce ta hana ni sukuni.
Ta kuwa dage ta ce "Ba kunya zaki ji ba Yabi! Na baki wannan fahamin ne dan na taimake ki, ku zauna lafiya. Amma fa kada ki yarda ki dinga jansa a k'asa. Domin k'arfin addu'ar yawa ne da shi tamkar yankar wuka take".
Na k'yal-k'yale da dariya saboda bilhakki take maganar zan jarabta shi da wannan karatun surkullen.
Sai da dariya ta tsagaita mini na ce "Allah ya bada lada Dada. Amma ni bazan yi a kansa ba. Baya sona, bana sonsa. Kowa harkar gabansa yake yi."
Ta dauki salati tana fa'din"Ashe har yau baku zama d'aya ba? Tisa ki yayi a gaba yake kallon ki kawai?
To idan na tafi zan fara tsayawa wajen Malam Nata'ala na ji ya ya matsayin aurenku.
Domin nasan duk ma'auratan da suka shafe kwanaki arba'in basu hadu ba, tabbas aure ya haranta. To ku kwanaki talatin da biyu da aurenku. Zan je na sake jin fatawar kada aje ko auren ya b'aci ba'a sani ba".
Na yi shiru domin na kasa gane bayanin na ta. Ban ce komai ba, domin kuwa ban ta'ba jin makancin hakan ba.
Ta numfasa ta ce "Yabi kin san duk macen da ta ki d'agawa mijin auren ta k'afa. Zata zama makamashi ne a cikin wutar jahimu?"
Na yi shiru tare da b'ata fuska. Ta sake ce wa "Wannan hukuncin lahira ne. A duniya kuwa babu ita babu ganin hasken rayuwa tunda malaiku dubu maitan ne zasu yi ta kabarbari suna d'ebe mata albarka. Kin san kuwa ko limamin unguwarku ne ya tsine miki, kin yi hannun riga ke da walwalar rayuwa bare kuma ma'asumai irin malaikun Allahu".
Jikina ya yi sanyi da wannan karatun na karshe. Wanda babu kuskure ko shaci fa'da a cikinsa.
Amma da na tuna ai bai ta'ba nema na hana ba, ke nan bana cikin tsinuwar malaiku, sai na samu sau'kin tsoratar da na yi.
Kafin ta sake magana na zabura na tashi ina ce wa "Bari na duba girikina".
Na tace shinkafa, na yi k'asa da wutar na mayar.
Na duba ledar da ya ajiye na ga salak da kuma ledar soyayyen kifi.
A gurguje na yanka na wanke da gishiri na bar shi a kwandon tsane wa bayan na rufe.
Daidai lokacin na sauke sanwar, na d'ora ta miya.
Na juye a flask na fito da tukunyar na jika ta da ruwa.
Na ce "Dada mu shiga ki yi kallo. Rana ta fara kusantomu.
Ta ce "Zan tashi dai saboda rana, amma ba dan na yi kallon shagala ba.
Na kunna na kamo mata wa'azin Malam Guruntun tana saurare can ta nisa ta ce "ya iya karatu kuwa. Amma dai wannan ba namu ba ne ko Yabi?"
Cikin k'arfin hali na ce "Musulmi ai d'anuwan musulmi ne Dada. Bare wannan bijimin Malami ne. Ke dai ba ki ji abin da Allah da ma'aiki suka ce ba ne na ki?"
"Ta kyabe baki ta ce"Masu daddagen wando ai tsakaninmu da su sai a lahira. Tunda suna raina karamar shehu".
Dariya ta kwace mini. Na dinga yi sosai.
Na canja tashar cikin sa'a kuwa sai ga sheikh Mak'ari yana bayani irin wanda ta gamsu da shi.
Na gama abinci tsaf. Bamu ci ba sai da muka yi salla sannan na kawo mana. Tare ta ce na zuba mana. Muna ci tana yaba girkin nawa.
Tana kuma ta yi mini maganganun da suke nuna girman da miji yake da shi.
Ban ce uffan ba, sai da ta ce "Ki kwantar da hankalinki ki zauna lafiya. Nan da kwanaki ka'dan zan sake kewayo ku. Idan har kika bari kwanakin auren ki ya kai arba'in baki bari ya ri'ke hannun ki ba. Tabbas zan fa'dawa mahaifin ki. A san halin da kuke ciki. Kada ku fara zaman haranci".
Na fara kuka tare da ce wa "Ba ruwan ki Dada! Kada ki ha'da ni da ubana, kada ki janyo mini fishin sa."
Ga mamakina sai ta sassauta ta ce "Idan kuwa har irin haka kike gudun fishin uban ki. Kamata ya yi ki guji fishin Allah fiye da hakan. Ai ba Babanku ba ne ya hukunta faruwar al'amarin ba. Allah ne da kansa. Fishin Ubangiji akan bawansa kuwa yana nufin tabarbarewar dukkan al'amuran rayuwa".
Na kasa bu'de baki na ce "Bai ta'ba nuna wa yana da bu'katar hakan daga gare ni ba. Saboda yana samu a waje. Sai kawai na sake tsananta kukan da nake yi. Domin har ciki mak'oshina nake jin ba'kin cikin halin da nake ciki.
Har la'asar ta kawo kai, bata fasa sakin maganganu ba. Wasu na gaskiya, wasu na barkwanci wasu kuwa masu nauyi ne. Ita kuwa ko a jikinta.
Ina kuka sosai amma bata damu ba sai ce wa ta yi "Da kin san kanki ai da tuni kin mayar da shi bita zaizai. Mata irinmu masu k'aramin ruwa ai mafi yawa murza maza muke yi. Kin ga duk haiba da siffar mijin ki. Da kin kwantar da hankalinki, kina masa biyayya, kina ba shi kanki ai wataran ma sai ya shirya zai fita, idan kika ce kada ka fita ce wa zai yi to."
Na cuna baki na ce "Da dai ba dan-iskan duniya ba ne".
Ta kuwa zabura ta jefe ni da kofin kusa da ita.
A ki'dime ta ce "Mijin ki kika zaga kai tsaye babu nadama bare shakka?
Tabbas kin kafurta, kin halaka Yabi. Dole sai kin sake karban shahadar shiga musulunci.
Na kasa kunshe dariya ta. Na k'yal-k'yale da dariya sosai.
Ranta ya baci k'warai da gaske. Ta shiga share hawayen takaici.
Murya na rawa ta ce "Ki aikata kaba'ira sannan ki yi dariya? Saboda ku yaran yau babu darhamin imani a zuciyarku?"
Na ha'diye dariyar a dalilin kukan gaske take yi.
Da sanyin murya na ce "Ki yi hakuri Dada."
Ta ce "Na ha'kura amma, ai dole ki sabunta musuluncinki Yabi. In kuwa ba hakan ba, tabbas kin zama arniya.
Cikin k'arfin hali na ce "Ba ni kalmar shahadar na sabunta din."
Ta rike baki ta ce "Wace ni na shiga sahun Malamai. Ni almajira ce me neman sani. Gaban babban malami za'a kai ki ya baki shahada ki kar'ba. Ko kuma ki yi tuba a gaban mijinki ki nemi afuwa sannan ya baki kalmar ki kar'ba".
Na bata rai na ce "Haba Dada tunda ba'a gabansa aka yi ba, ina dalilin sai ya ji. Tunda kin ce na sabawa Allah. Ki bari na ce Astagafirillah! Amma kada ki fa'da masa. Dukana zai yi, son girmansa yawa ne da shi".
"To shikenan bazan fa'da masa ba.
Amma ki tsananta intigifari Yabi".
Daga haka muka yi haramar sallar la'asar.
Na tattare kwanukan na share wajen kafin ta fito daga bayi.
Mun jima da idar da salla sannan ya dawo.
Kallonsa kawai na yi na gane bai ci abinci ba.
Dada ta dinga yi masa barka da dawowa. Ya amsa yana murmushi wanda na tabbatar na yak'e ne.
Ta zuba masa ido ta ce "Ya na ganka haka ne?"
Ya ce "Babu komai. Sauri nake yi kada ki ce ban zo da wuri ba."
Bata ba shi amsa ba ta kalle ni.
A dole na ce "Sannu da dawo wa".
Ya amsa da walwala sosai".
Ya ce "Na kai ki yanzu, ko na watsa ruwa?"
A tausashe ta ce "Yunwa kake ji, ka fara cin abinci, nasan baka shiri da yunwa".
Ya yi k'asa da kansa. Bai ce komai ba.
Ta ce "Yabi ki kawo masa ruwa da abinci mana".
Na daure fuska matu'ka da gaske sannan na ce "Baya cin abincina ai".
Ta fara fa'din "Allahu Akbar kabiran, wa subhanallahi bukuratan wa asila. Wanne irin zama kuke yi ne na kafirci ni Binta?
Baya cin abincin ki sai na wa to?"
Da yake abin na yi mini ciwo sosai. Cikin rawar murya na ce "Sai na y'ar iska mana."
Dada ta kalle ni da kyau tamkar me yin nazari. Sannan ta mayar da kallonsa kansa. Gaba'daya ya yi laushi tabbacin ya buga bai samu abin da ya sanya a bakinsa ba.
Tsawon lokaci ta ce "Kira mini lambar Alhaji. Da alamun al'amarin naku ya yi munin da ba zan iya gyara shi ba."
Tana rufe baki na fashe da kuka Ina cewa "Saboda son kai sai ki kira mahaifina ki bata ni a wajensa, ki tayar masa da hankali. Alhalin tunda na zo gidan nan ba abin da nake ga ni sai wula'kanci da tozarci. Ai ni an cuce ni karshen cuta kuwa".
Na fa'di hakan cikin kuka mai tsananin gaske.
Ta saki ajiyar zuciya ta ce "To kira mini Hauwa tunda ita din kin yarda uwar ki ce".
Shima cikin sauri ya ce "A a Dada kinsan dai bayan ta zata bi. Sannan fishi zata yi da ni! Yanzun ma ya nake fama ne a rayuwar nan bare kuma ace ina cikin fishin uwa. Rabu da ita kawai Dada. Idan na fa'di na mutu ba shi kenan ba. Sai ta je ta auri wanda take so."
Chapter 60 · 0% Book details