← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 134 OF 146

Sashe 134

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1

*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*MASU SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S ONLY*.

Da zamu tafi aka zuba mana leshina da atamfofi da kayan yara fall leda. Ga Kuma kayan ciye ciye da soyayyun nama. Sai da na nutsu sai na gane har da material din Malaysian Fabrics na umm Nihla.
Ta ce kuma Hajiyar ta sallame ni. Murya na rawa Babah ta ce "Baby wata sallama Kuma. Ai kin nuna mana ke din uwar kowa ce a wannan jahar. Allah ya kare ki, ya dora mijin ki akan magauta. Ya dauwamar da arziki ya shirya muku zuria "
Cikin Jin dad'i take fad'in Ameen amen".
Har gida Hajiyar ta kawo mu . Ta shigo ta huta. Kafin ta bar gidan Baba ta zayyane mata matsalar da mkue ciki akan lamarin Tijjani.
Ta ka'du k'warai da gaske. Sannan ta ce zata shigar da maganar gaban first lady da IZININ UBANGIJI.
Ta ajiye envelope tana ce wa "Ga albashin ki na farko costumes din matar gwamna. Kafin kuma ki fara karboa na gwamnati. Cikin satin nan zan kawo miki upper din ki har gida "
Na dinga yi mata addu'ar fatan alheri da godiya mai yawa. Ta karbi takarduna ta tafi da su.
Kwanaki uku ta dawo mini da upper kamar yadda ta yi alkawarin kawo mini har gida. Sannan women center din unguwarmu aka tura ni. Wnai abin burgewa a weekend ne aikin nawa. Ga albashina da tsoka babu laifi.
Sati na zagowa muka tafi wajen Tijjani muka yi masa bayanin halin da ake ciki. Ya yi murna, ya yi fatan alheri.
Ya sake jaddada mini bai yarda na dinga zuwa gidajen mutane ba. Gidan gwamnati ya amice Slshima sai tare da Babah zamu je. Da girmamawa nake ce wa to, domin ya samu nutsuwa. Nima kuma bana k'aunar abin da zai bata masa rai. Domin a yanzu na gasgata bayan iyayena ba abin da nake so a duniya irin Tijjani da y'aya'nsa. Hatta uwarsa da y'an uwansa ina jinsu daban a duniyata.
Ganin ya amince na ce wa Babah zamu je Toro na KAIWA su Baban Marina su ga upper ta."
Ta ce "hakan ya yi. Washagari kuwa muka tafi Toro.
Murna kan murna Baban Marina ya yi. Ya dafa kaina ya ce "Nasan zaki yi albarka Yabi. Na sani akwai babban al'amari a tare da ke. Na sani zaki daukaka. Alhamdulillah! Ubangiji ya fito mana da Tijjani. Allah ya shirya miki zuria. Allah yasa albarka a cikin komai na ki. Yadda kike tsaye a kaina da iyalina Ubangiji ya tsaya miki ke da ahalin ki fiye da haka. Asiya ke kad'ai gayya ce a gidan Marina".
Na yi k'asa da kaina ina hawaye. Ina Jin rashin Tijjani ne cikas dina.

Amma babu abinda ban samu ba na rufin asiri a duniyar nan ba.
Kafin ka ce miye wannan sai na fara Tara kudade masu nauyi. Domin dai ban fasa yin lalle a gida ba. Duk wata albashi biyu nake ja. Ga wanda gwamnati zata ba ni. Ga wanda ake ba ni a envelope idan na je gidan gwamnati na yiwa Madam da iyalin ta kunshi da kitso.
Bana tab'a su tunda har yau Yaya Aliyu bai tab'a yin lako lako da abincinmu da kuma kula da yara ba. Iya na lalle dai da shi nake hidimar da nake yi. Domin so nake na yiwa Baban Marina ba zata ta ban mamaki.
A hankali alherin da ya same ni ya fara shiga kunnuwan mutanan gidan Marina.
Nan da nan aka fara cece kuce. Ko a biki aka taru saa'anninmu da na yi musu zarrra zasu yi ta sakin baki a gaban Nazira suna ce wa "Ai yanzu na zama y'ar siyasa ba kuma siyasar ce abin kaico ba. Manyan mata ne suke dauka ta muke sheke ayarmu. Ta ya ya za'a ce wai matar gwamna nake yiwa kunshi. Wace ce ni? A wanne karatun da bai fi cikin cokali ba. Tun Nazira na hak'uri, tana tankawa cikin dad'in rai tana fahimtar da su, har ta shiga yin tashin hankali da duk wanda zai soke ni. Hatta yaran dakin inna k'ananunmu ke nan da a yanzu suke y'anmata matukar suka ji wani ya soke ni sai dai aji na gwabza fad'a. Tunda ce wa suke hi karuwanci nake yi. Gabadaya y'an k'ofarmu ba yadda za'a yi a tab'asu su kyale a yanzu. Ganin hakan sai aka koma fad'in ni ce nake musu huduba tunda nima hakan na yi , sannan na mayar da dukkan ahalin Babanmu agwagi sai abin da na ce tunda na fisu kudi. Dan ma sunsan kudin nawa da ake famkama na kazanta ne. Sannan mugun k'ullin da yake raina ne ya sanya aka gane mijina dilar k'waya ne.
Dana zauna na nutsu sai na gane tabbas wata k'iyayyar bata da dalilin yin ta. Mafi yawa hassada ne da kyashi. Ba kuma zai yiwu kowa ya so ka ba. Babbar godiyar da nake tsananta yi ban tab'a zuwa gidan Marina na tsugunna a gaban wani na ce a taimake ni ba. Duk yadda aka yi mini aure dan a kassara ni, sai Ubangiji ya yi kishina. Wahala kam na sha ta, amma ba mai yawa ba ce. Sannan Ubangiji ya yi mini rufin asiri irin wanda ko y'aya' mazan gidanmu basu same shi ba.
Mafi girman Niimar da Ubangiji ya yi mini, itace ta lafiya da kuma sana'ar hannu, ya kuma ba ni haihuwa, ya sake ba ni mijin da yake tsananin sona. Bugu da kari ina cikin wadanda Ubangiji ya yi musu gata irin na gam da katar na girma da iyayena guda biyu. Wannan kad'ai babbar niimace a wajen bawa. Domin ko da ban san zafin rashin iyaye ba. Allah ya sani ina matukar tausayin wanda iyayen sa suka rasu domin al'amarin da suke fuskanta mai tsananin gaske ne. Ka ga masu iyaye suna samun TAGOMASHIN addu'a, suna samun tallafi, suna zuwa su yi hira da su, domin sun san zasu boye damuwarsu, sabanin wadanda basu dasu a raye sun dinga tiri tiri da matsalar da ta dame su saboda gudun za'a fantsama matsalarsu a duniya.
Da na tattara wadannan ni'imomin sai na ga ba zai yiwu kuma a ce kowa ya so ni ba. Ba zai yiwa kuma na ga yadda nake so ba. Tunda sunnar rayuwa ce kowa da irin k'alubalen da zai fuskanta a duniyarsa. Sai na gamsu kalubalena rufe Tijjani da aka yi. Ina rayuwa babu miji tsawon shekara guda. Sai kuma rashin soyayya daga dangi, da rashin hadin kai a tsakaninmu.
Na numfasa na ce Alhamdulillah. Ubangiji ka yi mini komai. Allah ka fito mini da Mijina. Ubangiji a sanya soyayya da tausayi a zukatan ahalin gidan Marina gabad'aya. Domin na riga da na gaji da gutsiri tsoma Wallahi.
Chapter 134 · 0% Book details