Sashe 103
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
Kwananki ka'dan muka tare sabon gidanmu mallakinmu ba wai haya ba.
Cikin dare mun gama mua'amalarmu, mun yi wankanmu a cikin d'akinmu. Munana kwance ya kankame ni, a kunne ya rad'a mini "little kamar yau kike mini kukan band'aki a daki kike so. Na ce miki da sannu zan miki, a wanccan lokacin baki gasgata ni ba, sai kika ce wasikar jaki nake yi. Tun daga waccan rana ban sake yin sujjada ban ro'ki Ubangiji ya bani damar da zan miki band'aki a cikin d'aki. Sai ga shi a kusa na samu damar ba tare da zato ko iyawa ta ba."
A hankali na ce "Baban 2 kana da tashin tashina Wallahi".
Ya yi dariya ya ce "Indai ba sharri ne da ni ba ai da sau'ki Maman 2".
Ban gama wartsake wa daga kunyar da ya saka ni a ciki ba. Ya sake baro wata maganar. Ta hanyar ce wa "Na k'osa ki yi ciki little kada ki fara yi mini borin idan ban miki ciki ba zaki tafi ki bar ni".
Na kai masa duka a k'irjinsa ina kukan shagwaba tare da fa'din "Bana son irin hakan da ka ke yi mini Baban 2".
Ya ri'ke ni yana dariya ya ce "Ba gaskiya na fa'da ba? Kin ga twins sun yi wayo, suna gudunsu ko ina, idan kin samu ciki yanzu babu damuwa, kafin ki haihu sun sake girma. Na ga kuma Babah so take ta rabamu da su. Idan kina da wani a hannun ki ba zaki wani damu ba".
Ban ce komai ba. Domin kunya ta yi mini k'awanya.
A wannan tsukun da'din da Baban 2 ya jiyar da mu ba ka'dan ba ne. Domin suturun da baya samun sukunin yi mini sai da ya mini matsakaita kala biyar. Kusan karamin lefe ya yi mini. Tunda komai sai da ya siya mini daidai misali. Haka yara ma ya yi musu siyayyar kayan sawa da kayan wasa.
Cikin nutsuwa muke rayuwa, ina mutunta shi tare da girmama shi. Haka shima yake kaffa kaffa da ni. Idan ya ga zan rikice masa, zai bar komai ya rarrashe ni, ya kwantar mini da hankali. Domin budin da ya samu, ya sanya shima ya sabunta suturunsa, ya sake zama hadadden gaye. Tunda yanzu ne ya cika shekaru talatin. Ma'ana yana cikin shekarun samartaka da k'arfi. A lokacin ni kuma nake shirin shiga shekaru ashirin.
Gaba'daya na kwarzabi raina, domin ina ganin zai iya samo zabgegiya ya aura.
Ban ta'ba bu'de baki na yi masa k'orafi ba. Amma a ankare nake matu'ka da gaske.
Ba a jima ba motar da ya siya ta golf ta iso.
Ya zaunar da ni ya fa'da mini zai fara kai kayan miya garuwa ranakun kasuwanni. Tunda zaman kasuwar yana neman gagarar sa. A dalilin yadda Alh Auta da sauran wadanda suke ganin ya je ya same su a wajen amma ya kere su. Sun ki fahimtar Ubangiji ne yake raba arziki a sadda ya so.
Cikin nutsuwa na ce "Wai filin nan naka babba ne da suka karbe shi da ku'di masu nauyi irin hakan?".
Shima a nutse ya ce "Babba ne ainun. Idan raba shi za'a yi zai yi fuloti uku manya. Sannan wajen ya yi daraja baya ga hakan a bakin titi wajen yake. Kar kuma ki manta tsawon shekaru biyu suka biya.
Shiyasa nake son na juya ku'din da ya yi saura mu dinga samun na abinci da sauran bu'katun yau da kullum.
Yaranmu gaba ka'dan makaranta za'a sasu, boko da Islamiya, kin ga duk hidimar ku'di ce. Ga yadda kullum rayuwar take sake tsananta. Akwai bu'katar na yi aiki tuk'uru. Sai na barwa Allah ya taimake ni a inda zan gaza".
A sanyaye na ce "Da ikon Allah na zaka gaza ba Baban 2. Ubangiji ya yiwa kokarinka albarka. Ya tsare ka da dukkan sharrin masu sharri. Allah ya raba ka da sharrin karfe da titi."
Ya rungume ni sosai ya ce "Ameen Maman 2. Ina son ki, ina alfahari da ke. Allah ya barmu tare cikin aminci".
Da rauni na ce "Ameen. Amma kasan ina shiga zullumin kada wata ta zo ta k'wace mini kai?"
Na fa'da hawaye na ziraro mini. Ya tsananta rik'on da ya yi mini ya tausasa harshe ya ce "me yasa kika karaya haka Asiya? Ban ji akwai wata mace da zata firgita ki ai. Ni naki ne, a hannunki na ke. Ki daina damuwa da abin da yake gaibu ne. Al'kawarin da zan miki d'aya ne. Har abada kin wuce wula'kancina. Kina da alfarmomi masu yawa da babu wata macen da zata samu irin alfarmomin ki a waje na."
Bai bar ni ba. Sai da na samu nutsuwa. Can kuma ya ke ce da dariya ya ce "Ubangiji yana ta kama mini Asiyata. Kamar yau take fa'din me zata yi da Basamude irina. Kin tuna amsar da na baki a ranar?"
Na k'yale shi domin yanzu ya riga da ya lakanci tuno mini abubuwan da suke kunyata ni.
Bai bar maganar kamar yadda na barta ba sai da ya ce "A lokacin na ce miki akwai ranar da zaki yi kuka akan son basamuden nan. Sannu a hankali komai na fa'da a kanki Ubangiji yana zartarwa. Na share ban yarda na tanka shi ba.
Cikin Ikon Allah Tijjani ya fara safarar kai kayan miya kasuwanni daban daban na cikin jahar Bauchi da makwabtanta irin su Jigawa.
Da wuri yake fita. Ya je ya kai. Idan zai dawo kuma sai ya lodo mutane. Gaba'daya ya ajiye girman kai, da tunanin yana da kwalin digiri.
Ba'a dauki lokaci mai yawa ba, muka rabu da matsalar babu. Domin sosai yake samun ku'di tunda ba balance yake kai wa ba. Ni ce ma na koya masa dabarar ya dinga ajiye wani abu a banki saboda ko watarana motar zata bukaci gyara. Ko wata lalurar zata gitto bakatatan. Ba ja in ja ya yarda da shawara ta. Akai akai yake yiwa mahaifiyarsa da Baban Marina sako. Dada ma bai barta a baya ba. Wani lokacin idan ya je Jos sai ya tsaya ya musu alheri, sannan ya taho. Hatta su Baban Tsakiya yakan yi musu alheri kai musu kayan miya ko doya.
Ku'di ne dai baya basu.
Wannan rufin asirin da ya samu ya sanya masu yi masa kallon banza suka shiga nan nan da shi. Akai akai ake bugo masa waya, sabanin lokacin baya da ba'a saka shi cikin mutane bare a tuna da shi.
Rannan kwatsam sai ga shi ya dawo da Nasiba tare da akwatinta shake da kayan da suke nuni zata jima tare da mu.
Na gama nazarinta. Gaba'daya ta goge ta yi fes da ita. Ta cika ko ina dam tabbacin yanzu tafi samun nutsuwa.
Ni ce shaida muka akan son da take yiwa Baban 2.
Na ha'diye komai na yi mata uzziri tunda shi so Ubangiji ne yake kitsa shi a zukatan bayinsa. Sannan a lokacin da aka zartar da aurena da shi bata yi mini koamai ba, sai fatan alheri duk da kuwa yadda al'amarin ya buge ta. Dan haka nima a yanzu zan mata kawaici ka'dan. Amma ban da aurensa. Wannan kam bazan iya ba. Na kuma tabbatar da niyyar hakan aka turo ta. Uwarta zata yi komai dan ganin Tijjani ya aure ta ba tare da ta jin kunyar ubana ba. Ta manta yadda ta ture komai ta yi sanadin datse soyayyarsu. A yanzu kuma da ake ganin ya samu mamora shine za'a lika masa ita. Ko kunyar ha'damu kishi bata yi. Kiri-kiri take nuna mini tsana tamkar wadda agola ce ni a gidan haka take yi mini.
Da daddare muna kwance gaba'daya na kasa sakin raina. Har shi ma na ji haushinsa ya turnik'e ni, akan wanne dalilin zai dauko ta tunda ga Toro su taho Bauchi?
Ya kasa ha'kuri ya ce "Little wai mene ne?"
Na yi masa banza. Ya tunzura ya ce "Amma dai kin san na tsani na miki magana ki share ni ko?"
Na kasa bu'de baki na ce mass komai a dalilin kuka nake yi irin na sharbe.
Jin shesshekar kukana ya sanya ya shiga rud'u.
Ya dinga tambayar ba'asin kukan nawa. Sai da na tabbatar na rikita shi matu'ka da gaske sannan na ce masa "A kan me za'a sa ya kawo mini Nasiba gida ba tare da yarda ta ba?"
A hankali ya ce "Dada ta ce na taho da ita ta mana kwana biyu. Ita ma kuma ta da'de tana fa'da mini tana son zuwa ta ga sabon gidanmu. Shine yau da ta ce zata biyo ni na ce to".
Na tashi na zauna na ce "Hakan ya yi. Wato har waya kuke yi ko Tijjani?"
Ya zuba mini ido sosai domin yasan tunda na gatsa sunasa gatsal to zan iya yin komai na rikici a tsakaninmu.
Ya sassauta ya ce "Dan ta zo mana bakunta mene ne a ciki?"
A tunzure na ce "akwai komai ma. Bana son bakuntar ta, ba kuma zata zauna mini a gida ba".
Ga mamakina sai ce mini ya yi "Wai gidan na ki ne?"
Na kad'u matu'ka da gaske. A matu'kar sanyaye na ce "A a naka ne mantawa na yi, amma ka tabbatar ba zan yarda da kai alhalin ina ganinku a gida daya ba." Na koma na kwanta, shi ma ya kwanta bayan ya juya mini baya da alamu ya yi matu'kar fusata da na ce Ban yarda da shi ba. Ya sani kuma ina da hujjar da zan guji zamansu a gida daya, mussaman karamin gida irin namu.
Washagari muka tashi kowa na ganin laifin d'anuwan sa. Na yi matu'kar boye wa Nasiba halin da muke ciki. Tare da ita muka karya a kwano daya. Tunda shi ya fice bai saurari abincin ba.
Da daddare ma hakan muka sake kwana babu jituwa. Domin nasan jira yake na ba shi hakuri, na kuma rarrashe shi. Ni kuwa al'amarin da yake cina ba k'arami ba ne.
Ko magana bama yi ni da shi.
Ba dan bana son ta fahimci akwai matsala a tsakaninmu ba da ko dakinsa ba zan je ba.
Amma ina zuwa bayan mun sha hira ni da ita.
Ranar da ta yi kwanaki biyu da daddare mun kwanta. Na bu'de baki na ce "Tijjani gobe bakuwarka zata yi kwanaki uku a gidanka. A ka'idar shari'a kuma bakunta ta kwanaki uku ce. To kasan yadda zaka yi ta bar maka gidan a gobe, ko kuma ka ga abin da baka so".
A tunzure ya ce ",Tun yaushe na ga abin da bana so Asiya? Ai tunda babu yarda a tsakaninmu magana ta k'are. Ba kuma zan kore ta a gidana ba. Ni da kika gan ni bana manta alheri komin tarin kalubale da rashin kirkin mutane. Dan haka komai zaki yi Bismillah".
Na ce "Hakane. Madallah da Tijjani".
Kasan zuciyata kuwa tamkar na tashi na cinnawa gidan wuta haka nake ji.
Washa gari ya saka kai ya fice bayan ya amsa gaisuwar ta a tsaitsaye ba tare ma da ya kalle ta ba. Haka kuma yake yi mata tunda ta zo.
Mun gama karyawa na kalle ta na ce "Nasiba zan je Kangire dubiya. Wata'kila na kwana, wata'kila kuma na dawo. Na tafi da yaran nan ko na bar miki su?"
Zucyarta daya ta ce "Ki barsu mana indai baza su yi rikici ba. Idan suna ganin Babansu baza su yi kuka ba ai babu damuwa".
Na ce "Hakane.
Na shirya kayana set uku a dan k'aramin akwatina, na yi sallama bayan na yi dabarar tura tagwaye kwaso shanya a baya. Na fice a hankali, bayan na ce mata na bar ki da wahalarsu kuma".
Ina jin ta tana fa'din 'yayanki ba nawa ba nawa ba ne ke nan Yabi?"
Ban tsaya bata amsa ba gudun kada su fito, su ga tafiya ta.
Da azahar ya koma gidan a dalilin ya dawo daga Dass.
Ya tarar da yara na kukan neman Amminsu. Ya fahimci Yabi ta fice ta bar gidan babu izininsa. Hankalinsa ya kai k'ololuwar tashi, ransa ya baci ainun.
Cikin hikima ya ce "Da nasan da wuri zan dawo ai bazan bari ta fita ba.".
Nasiba da take kicin ta ce "Nima da ta ce mini zata iya kwana a can na shiga zullumi."
Ya mik'e ya ri'ke hannun yaran suka fita, ya rasa inda zai tsoma ransa da wannan tashin hankalin da ya kewaye shi.
"Sha'anin mata yana da gigitarwa. Mene ne abin tafiya ki bar dakinki idan ba kalen masifa ba little?" Ya furta a fili a kuma ki'dime.
Cikin dare mun gama mua'amalarmu, mun yi wankanmu a cikin d'akinmu. Munana kwance ya kankame ni, a kunne ya rad'a mini "little kamar yau kike mini kukan band'aki a daki kike so. Na ce miki da sannu zan miki, a wanccan lokacin baki gasgata ni ba, sai kika ce wasikar jaki nake yi. Tun daga waccan rana ban sake yin sujjada ban ro'ki Ubangiji ya bani damar da zan miki band'aki a cikin d'aki. Sai ga shi a kusa na samu damar ba tare da zato ko iyawa ta ba."
A hankali na ce "Baban 2 kana da tashin tashina Wallahi".
Ya yi dariya ya ce "Indai ba sharri ne da ni ba ai da sau'ki Maman 2".
Ban gama wartsake wa daga kunyar da ya saka ni a ciki ba. Ya sake baro wata maganar. Ta hanyar ce wa "Na k'osa ki yi ciki little kada ki fara yi mini borin idan ban miki ciki ba zaki tafi ki bar ni".
Na kai masa duka a k'irjinsa ina kukan shagwaba tare da fa'din "Bana son irin hakan da ka ke yi mini Baban 2".
Ya ri'ke ni yana dariya ya ce "Ba gaskiya na fa'da ba? Kin ga twins sun yi wayo, suna gudunsu ko ina, idan kin samu ciki yanzu babu damuwa, kafin ki haihu sun sake girma. Na ga kuma Babah so take ta rabamu da su. Idan kina da wani a hannun ki ba zaki wani damu ba".
Ban ce komai ba. Domin kunya ta yi mini k'awanya.
A wannan tsukun da'din da Baban 2 ya jiyar da mu ba ka'dan ba ne. Domin suturun da baya samun sukunin yi mini sai da ya mini matsakaita kala biyar. Kusan karamin lefe ya yi mini. Tunda komai sai da ya siya mini daidai misali. Haka yara ma ya yi musu siyayyar kayan sawa da kayan wasa.
Cikin nutsuwa muke rayuwa, ina mutunta shi tare da girmama shi. Haka shima yake kaffa kaffa da ni. Idan ya ga zan rikice masa, zai bar komai ya rarrashe ni, ya kwantar mini da hankali. Domin budin da ya samu, ya sanya shima ya sabunta suturunsa, ya sake zama hadadden gaye. Tunda yanzu ne ya cika shekaru talatin. Ma'ana yana cikin shekarun samartaka da k'arfi. A lokacin ni kuma nake shirin shiga shekaru ashirin.
Gaba'daya na kwarzabi raina, domin ina ganin zai iya samo zabgegiya ya aura.
Ban ta'ba bu'de baki na yi masa k'orafi ba. Amma a ankare nake matu'ka da gaske.
Ba a jima ba motar da ya siya ta golf ta iso.
Ya zaunar da ni ya fa'da mini zai fara kai kayan miya garuwa ranakun kasuwanni. Tunda zaman kasuwar yana neman gagarar sa. A dalilin yadda Alh Auta da sauran wadanda suke ganin ya je ya same su a wajen amma ya kere su. Sun ki fahimtar Ubangiji ne yake raba arziki a sadda ya so.
Cikin nutsuwa na ce "Wai filin nan naka babba ne da suka karbe shi da ku'di masu nauyi irin hakan?".
Shima a nutse ya ce "Babba ne ainun. Idan raba shi za'a yi zai yi fuloti uku manya. Sannan wajen ya yi daraja baya ga hakan a bakin titi wajen yake. Kar kuma ki manta tsawon shekaru biyu suka biya.
Shiyasa nake son na juya ku'din da ya yi saura mu dinga samun na abinci da sauran bu'katun yau da kullum.
Yaranmu gaba ka'dan makaranta za'a sasu, boko da Islamiya, kin ga duk hidimar ku'di ce. Ga yadda kullum rayuwar take sake tsananta. Akwai bu'katar na yi aiki tuk'uru. Sai na barwa Allah ya taimake ni a inda zan gaza".
A sanyaye na ce "Da ikon Allah na zaka gaza ba Baban 2. Ubangiji ya yiwa kokarinka albarka. Ya tsare ka da dukkan sharrin masu sharri. Allah ya raba ka da sharrin karfe da titi."
Ya rungume ni sosai ya ce "Ameen Maman 2. Ina son ki, ina alfahari da ke. Allah ya barmu tare cikin aminci".
Da rauni na ce "Ameen. Amma kasan ina shiga zullumin kada wata ta zo ta k'wace mini kai?"
Na fa'da hawaye na ziraro mini. Ya tsananta rik'on da ya yi mini ya tausasa harshe ya ce "me yasa kika karaya haka Asiya? Ban ji akwai wata mace da zata firgita ki ai. Ni naki ne, a hannunki na ke. Ki daina damuwa da abin da yake gaibu ne. Al'kawarin da zan miki d'aya ne. Har abada kin wuce wula'kancina. Kina da alfarmomi masu yawa da babu wata macen da zata samu irin alfarmomin ki a waje na."
Bai bar ni ba. Sai da na samu nutsuwa. Can kuma ya ke ce da dariya ya ce "Ubangiji yana ta kama mini Asiyata. Kamar yau take fa'din me zata yi da Basamude irina. Kin tuna amsar da na baki a ranar?"
Na k'yale shi domin yanzu ya riga da ya lakanci tuno mini abubuwan da suke kunyata ni.
Bai bar maganar kamar yadda na barta ba sai da ya ce "A lokacin na ce miki akwai ranar da zaki yi kuka akan son basamuden nan. Sannu a hankali komai na fa'da a kanki Ubangiji yana zartarwa. Na share ban yarda na tanka shi ba.
Cikin Ikon Allah Tijjani ya fara safarar kai kayan miya kasuwanni daban daban na cikin jahar Bauchi da makwabtanta irin su Jigawa.
Da wuri yake fita. Ya je ya kai. Idan zai dawo kuma sai ya lodo mutane. Gaba'daya ya ajiye girman kai, da tunanin yana da kwalin digiri.
Ba'a dauki lokaci mai yawa ba, muka rabu da matsalar babu. Domin sosai yake samun ku'di tunda ba balance yake kai wa ba. Ni ce ma na koya masa dabarar ya dinga ajiye wani abu a banki saboda ko watarana motar zata bukaci gyara. Ko wata lalurar zata gitto bakatatan. Ba ja in ja ya yarda da shawara ta. Akai akai yake yiwa mahaifiyarsa da Baban Marina sako. Dada ma bai barta a baya ba. Wani lokacin idan ya je Jos sai ya tsaya ya musu alheri, sannan ya taho. Hatta su Baban Tsakiya yakan yi musu alheri kai musu kayan miya ko doya.
Ku'di ne dai baya basu.
Wannan rufin asirin da ya samu ya sanya masu yi masa kallon banza suka shiga nan nan da shi. Akai akai ake bugo masa waya, sabanin lokacin baya da ba'a saka shi cikin mutane bare a tuna da shi.
Rannan kwatsam sai ga shi ya dawo da Nasiba tare da akwatinta shake da kayan da suke nuni zata jima tare da mu.
Na gama nazarinta. Gaba'daya ta goge ta yi fes da ita. Ta cika ko ina dam tabbacin yanzu tafi samun nutsuwa.
Ni ce shaida muka akan son da take yiwa Baban 2.
Na ha'diye komai na yi mata uzziri tunda shi so Ubangiji ne yake kitsa shi a zukatan bayinsa. Sannan a lokacin da aka zartar da aurena da shi bata yi mini koamai ba, sai fatan alheri duk da kuwa yadda al'amarin ya buge ta. Dan haka nima a yanzu zan mata kawaici ka'dan. Amma ban da aurensa. Wannan kam bazan iya ba. Na kuma tabbatar da niyyar hakan aka turo ta. Uwarta zata yi komai dan ganin Tijjani ya aure ta ba tare da ta jin kunyar ubana ba. Ta manta yadda ta ture komai ta yi sanadin datse soyayyarsu. A yanzu kuma da ake ganin ya samu mamora shine za'a lika masa ita. Ko kunyar ha'damu kishi bata yi. Kiri-kiri take nuna mini tsana tamkar wadda agola ce ni a gidan haka take yi mini.
Da daddare muna kwance gaba'daya na kasa sakin raina. Har shi ma na ji haushinsa ya turnik'e ni, akan wanne dalilin zai dauko ta tunda ga Toro su taho Bauchi?
Ya kasa ha'kuri ya ce "Little wai mene ne?"
Na yi masa banza. Ya tunzura ya ce "Amma dai kin san na tsani na miki magana ki share ni ko?"
Na kasa bu'de baki na ce mass komai a dalilin kuka nake yi irin na sharbe.
Jin shesshekar kukana ya sanya ya shiga rud'u.
Ya dinga tambayar ba'asin kukan nawa. Sai da na tabbatar na rikita shi matu'ka da gaske sannan na ce masa "A kan me za'a sa ya kawo mini Nasiba gida ba tare da yarda ta ba?"
A hankali ya ce "Dada ta ce na taho da ita ta mana kwana biyu. Ita ma kuma ta da'de tana fa'da mini tana son zuwa ta ga sabon gidanmu. Shine yau da ta ce zata biyo ni na ce to".
Na tashi na zauna na ce "Hakan ya yi. Wato har waya kuke yi ko Tijjani?"
Ya zuba mini ido sosai domin yasan tunda na gatsa sunasa gatsal to zan iya yin komai na rikici a tsakaninmu.
Ya sassauta ya ce "Dan ta zo mana bakunta mene ne a ciki?"
A tunzure na ce "akwai komai ma. Bana son bakuntar ta, ba kuma zata zauna mini a gida ba".
Ga mamakina sai ce mini ya yi "Wai gidan na ki ne?"
Na kad'u matu'ka da gaske. A matu'kar sanyaye na ce "A a naka ne mantawa na yi, amma ka tabbatar ba zan yarda da kai alhalin ina ganinku a gida daya ba." Na koma na kwanta, shi ma ya kwanta bayan ya juya mini baya da alamu ya yi matu'kar fusata da na ce Ban yarda da shi ba. Ya sani kuma ina da hujjar da zan guji zamansu a gida daya, mussaman karamin gida irin namu.
Washagari muka tashi kowa na ganin laifin d'anuwan sa. Na yi matu'kar boye wa Nasiba halin da muke ciki. Tare da ita muka karya a kwano daya. Tunda shi ya fice bai saurari abincin ba.
Da daddare ma hakan muka sake kwana babu jituwa. Domin nasan jira yake na ba shi hakuri, na kuma rarrashe shi. Ni kuwa al'amarin da yake cina ba k'arami ba ne.
Ko magana bama yi ni da shi.
Ba dan bana son ta fahimci akwai matsala a tsakaninmu ba da ko dakinsa ba zan je ba.
Amma ina zuwa bayan mun sha hira ni da ita.
Ranar da ta yi kwanaki biyu da daddare mun kwanta. Na bu'de baki na ce "Tijjani gobe bakuwarka zata yi kwanaki uku a gidanka. A ka'idar shari'a kuma bakunta ta kwanaki uku ce. To kasan yadda zaka yi ta bar maka gidan a gobe, ko kuma ka ga abin da baka so".
A tunzure ya ce ",Tun yaushe na ga abin da bana so Asiya? Ai tunda babu yarda a tsakaninmu magana ta k'are. Ba kuma zan kore ta a gidana ba. Ni da kika gan ni bana manta alheri komin tarin kalubale da rashin kirkin mutane. Dan haka komai zaki yi Bismillah".
Na ce "Hakane. Madallah da Tijjani".
Kasan zuciyata kuwa tamkar na tashi na cinnawa gidan wuta haka nake ji.
Washa gari ya saka kai ya fice bayan ya amsa gaisuwar ta a tsaitsaye ba tare ma da ya kalle ta ba. Haka kuma yake yi mata tunda ta zo.
Mun gama karyawa na kalle ta na ce "Nasiba zan je Kangire dubiya. Wata'kila na kwana, wata'kila kuma na dawo. Na tafi da yaran nan ko na bar miki su?"
Zucyarta daya ta ce "Ki barsu mana indai baza su yi rikici ba. Idan suna ganin Babansu baza su yi kuka ba ai babu damuwa".
Na ce "Hakane.
Na shirya kayana set uku a dan k'aramin akwatina, na yi sallama bayan na yi dabarar tura tagwaye kwaso shanya a baya. Na fice a hankali, bayan na ce mata na bar ki da wahalarsu kuma".
Ina jin ta tana fa'din 'yayanki ba nawa ba nawa ba ne ke nan Yabi?"
Ban tsaya bata amsa ba gudun kada su fito, su ga tafiya ta.
Da azahar ya koma gidan a dalilin ya dawo daga Dass.
Ya tarar da yara na kukan neman Amminsu. Ya fahimci Yabi ta fice ta bar gidan babu izininsa. Hankalinsa ya kai k'ololuwar tashi, ransa ya baci ainun.
Cikin hikima ya ce "Da nasan da wuri zan dawo ai bazan bari ta fita ba.".
Nasiba da take kicin ta ce "Nima da ta ce mini zata iya kwana a can na shiga zullumi."
Ya mik'e ya ri'ke hannun yaran suka fita, ya rasa inda zai tsoma ransa da wannan tashin hankalin da ya kewaye shi.
"Sha'anin mata yana da gigitarwa. Mene ne abin tafiya ki bar dakinki idan ba kalen masifa ba little?" Ya furta a fili a kuma ki'dime.