Sashe 119
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
*Y'ar uwa, ya mukaji da bubukuwa?* *Daga nan fa har january kusan ko wanne sati akwai biki, in ba na kusa ba akwai na nesa, ban da tunanin gudunmuwa da ma kudin man da zakaje bikin ga tunanin abunda zaka saka.*
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
Babah ta kasa ce wa komai domin ita gabad'aya ma alamarin tsoro ya shiga bata. Tana kuma mamakin rashin kunya da son kai irin na Maryo.
Bata yi zaton son zuciyarta ya kai hakan ba.
Ta kasa ce wa uffan saboda tsananin kaduwa da ta yi.
Ita kuwa ta dinga kuka tana face majina tamkar Dada ce ta kwanta dama.
Washagari ko karyawa bata yi ba ta ce zata juya. Da k'yar Babah ta roke ta akan ta bari ta karya.
Rai a bace suka rabu a dalilin Babah ta tabbatar aure kam babu a tsakanin Nasiba da Tijjani.
Rai a matukar bace ta isa Toro. Ta gurfana gaban Dada tana kuka tana fad'a mata karya da gaskiyar cin mutuncin da Hauwa ta yi mata.
Dada ta taya ta bacin rai tare da rarrashinta tamkar yarinya karama. Tana cin alwashin sai ta ci mutumcinta tunda bata san yakamata ba.
Bijirewar da Babah ta yi akan auren tare da fitowa baro baro da ta yi ta ce alamarin ba zai yiwu ba. Sai ya zama d'an zani. Domin hakan ya fusata Baba Maryo tare da cin alwashin sai Tijjani ya auri Nasiba ko zata yi yawo tsirara, ta ga karshen rashin kara da nuna banbanci.
Takanas ta tafi cikin jeji can kudu da Jos. Ta samo asiri da surkullen da muradinta zai cika.
*Bayan waatanni biyu*
A hankali Tijjani ya fara rikice mini fiye da bara. Sai mu kwana gari ya waye bai ce mini uffan ba. Zan masa magana goma bai fi ya amsa ni sau biyu ba a gajarce.
Ya daina shayin yin waya a gabana. Yanzu har an kai jallin da zai bawa twins waya su gaishe ta. Duk da dai bai tab'a kama suna ba.
Sai ya ga dama yake cin abincina. Jiya ma da na zauna kusa da shi ce mini ya na tashi yana bukatar kad'aici. Murjewar da na yi, nan da nan na fara tsomare wa. Sosai ya murde irin yadda ban taba zaton zai yi ba. Na hakurkurtar da zuciyata na dinga ba shi hak'uri tare da rokon ya fad'a mini laifin da na yi masa.
Yana bude baki sai ce wa ya yi "Haihuwa yake so. Tunda ba zan haihu ba, shi aure zai yi, idan zan zauna na zauna idan kuma bazan zauna ba, to bai rik'e ni ba."
Na zuba masa idona da suka soye. Na ce "Tsakanin ka da Allah kana mini adalci Tijjani?"
Ya hassalo ainun tare da ce wa "Ta ya ya zan yi miki adalci Asiya? To ko kawai zaki yi gaba ko zaki samu adalin?"
Na sake daskare wa. Na yi maza na kame bakina domin na gane komai na iya faruwa a tsakaninmu.
Amma hawaye ke tsere babu jinkiri kuncina.
Ya ja tsaki ya fice ya bar ni. Yana fad'in "Me za'a yi da mace mai rainuwa da azababben kishi. A ce mace ba zata taimake ka ta rufa maka asiri, ta taya ka son abin da kake so ba. Sai sarhutu da mance alheri kawai ta iya ".
Na yini cikin bacin rai. Yayin da shi kuma ya yi tafiyarsa Toro da yara bai damu da halin da ya bar ni a ciki ba.
Ina kuka na d'auki waya na bugawa Baban Marina karon farko da na yi hakan tunda ya aurar da ni. Na kasa magana sai kuka nake yi masa mai tsuma zuciya.
Bai katse ni ba. Sai da na gaji dan kaina na katse wayar.
Baban Marina ya dawo gida cikin sanyin jiki a dalilin yadda kukan Yabi ya buge shi.
Ya leka kofar Dada dan ya bata man zafin da ya siyo mata sai kawai ya ga Tijjani da Nasiba a gefen bisihiyar zogale suna zance. Dada na daki abin ta. Duk da ba yau ya saba ganinsu ba, amma yau din sai da zuciyarsa ta buga da tsananin gaske.
Ya amsa gaisuwarsu cikin k'arfin hali. Ya shiga wajen Dada ya fito, ya fita.
Ya zauna kan tabarma amma zufa ta rufe shi. Ya dinga jin wani iri. Duk yadda ya so jurewa kasa wa ya yi. Yana tambayar kansa yanzu Tijjani yana da rigar da za'a bashi aure ke nan?.
Ya tuna irin kukan da Yabi ta kira ta yi masa dazu, ya san kuka ne na neman agaji, kuka ne mai harshen damo. Daren ranar ya yi masa tsawo ainun.
Washagari ana idar da sallar asuba ya ce Salisu ya raka shi Bauchi.
Tamkar jifa haka Yabi ta gansu. Zuciyarta ta karye. Domin ta hango rauni da wata irin soyayyar ta a kan fuskar mahaifinta.
Tare da Tijjani suka musu iso zuwa falo.
Yana amsa gaisuwarsu ya yi gyaran murya ya ce "Zuwa na yi takanas dan na fad'a miki ce wa ki yi hakuri ki zauna a dakin ki. Ki kuma sauke dukkan hakkina da kika san Ubangiji ya dora miki. Daga nan har zuwa lokacin da Allah ya kaddara muku zaman kada ki yarda ki zalunce shi. Kada kuma ki fito babu izininsa. Aure da kike ga ni darajar sa ta wuce duk zaton mai zato. Sai dai bisa adalcin Ubangiji ya kewaye shi da dokoki da kuma sharudda daban daban. Bai barmu kara zube ba. Ina rokon ki, ki k'ara hak'uri a cikin wannan tsukun da ake son kaimu k'asa da bak'inciki mai tsanani. Idan har kika yarda kika yi hak'uri, ni kuma na miki alkawarin zan jaddada damar da shari'a ta baki na zabin cigaba da zaman ko akasin hakan matukar zalunci da cin fuska ya shigo gidan auren ki".
Cikin kuka da rawar murya na ce "To Babanmu".
Ina fad'in haka ya mik'e tare da ce wa "Allah ya yi miki albarka. Ya fice bai ko bi takan tagwaye da suke ta rige rigen gaishe shi ba. Yaya Salisu ne kawai ya amsa musu tare da ciro ledar alawowi a aljihunsa ya damka kowa tasa ledar.
K'warai Tijjani ya muzanta da yadda suka fice basu bi takansa ba. Ya bi bayansu. Ba jimawa ya shigo ya zauna. Ya ce "Baban Marina ya canja, ya yi bangaranci. To wai a kaina aka fara k'arin aure ne da za'a mini wulakanci irin haka?"
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633
*Balle ace maaikaciya ce ko CEO ce kina business din ki, kinsan all eyes on you🧐, ke ba sayen atamfa ba komi tsadanta anyo copynta, shima lace haka, cabdi! To albishirinki yar uwa!*
*UMM NIHLA malaysianfabrics ta dauke miki damuwa, tana da fabrics kala kala masu sauki da inganci kuma babu inda zaki samesu in ba wurinta ba, kije taro ki haska kowa sai ya tambaye ki me kika saka ina kika samu💃 maza garzaya gurinta kusa labule.* https://wa.me/message/F3EWRSHQPQAAH1
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
Babah ta kasa ce wa komai domin ita gabad'aya ma alamarin tsoro ya shiga bata. Tana kuma mamakin rashin kunya da son kai irin na Maryo.
Bata yi zaton son zuciyarta ya kai hakan ba.
Ta kasa ce wa uffan saboda tsananin kaduwa da ta yi.
Ita kuwa ta dinga kuka tana face majina tamkar Dada ce ta kwanta dama.
Washagari ko karyawa bata yi ba ta ce zata juya. Da k'yar Babah ta roke ta akan ta bari ta karya.
Rai a bace suka rabu a dalilin Babah ta tabbatar aure kam babu a tsakanin Nasiba da Tijjani.
Rai a matukar bace ta isa Toro. Ta gurfana gaban Dada tana kuka tana fad'a mata karya da gaskiyar cin mutuncin da Hauwa ta yi mata.
Dada ta taya ta bacin rai tare da rarrashinta tamkar yarinya karama. Tana cin alwashin sai ta ci mutumcinta tunda bata san yakamata ba.
Bijirewar da Babah ta yi akan auren tare da fitowa baro baro da ta yi ta ce alamarin ba zai yiwu ba. Sai ya zama d'an zani. Domin hakan ya fusata Baba Maryo tare da cin alwashin sai Tijjani ya auri Nasiba ko zata yi yawo tsirara, ta ga karshen rashin kara da nuna banbanci.
Takanas ta tafi cikin jeji can kudu da Jos. Ta samo asiri da surkullen da muradinta zai cika.
*Bayan waatanni biyu*
A hankali Tijjani ya fara rikice mini fiye da bara. Sai mu kwana gari ya waye bai ce mini uffan ba. Zan masa magana goma bai fi ya amsa ni sau biyu ba a gajarce.
Ya daina shayin yin waya a gabana. Yanzu har an kai jallin da zai bawa twins waya su gaishe ta. Duk da dai bai tab'a kama suna ba.
Sai ya ga dama yake cin abincina. Jiya ma da na zauna kusa da shi ce mini ya na tashi yana bukatar kad'aici. Murjewar da na yi, nan da nan na fara tsomare wa. Sosai ya murde irin yadda ban taba zaton zai yi ba. Na hakurkurtar da zuciyata na dinga ba shi hak'uri tare da rokon ya fad'a mini laifin da na yi masa.
Yana bude baki sai ce wa ya yi "Haihuwa yake so. Tunda ba zan haihu ba, shi aure zai yi, idan zan zauna na zauna idan kuma bazan zauna ba, to bai rik'e ni ba."
Na zuba masa idona da suka soye. Na ce "Tsakanin ka da Allah kana mini adalci Tijjani?"
Ya hassalo ainun tare da ce wa "Ta ya ya zan yi miki adalci Asiya? To ko kawai zaki yi gaba ko zaki samu adalin?"
Na sake daskare wa. Na yi maza na kame bakina domin na gane komai na iya faruwa a tsakaninmu.
Amma hawaye ke tsere babu jinkiri kuncina.
Ya ja tsaki ya fice ya bar ni. Yana fad'in "Me za'a yi da mace mai rainuwa da azababben kishi. A ce mace ba zata taimake ka ta rufa maka asiri, ta taya ka son abin da kake so ba. Sai sarhutu da mance alheri kawai ta iya ".
Na yini cikin bacin rai. Yayin da shi kuma ya yi tafiyarsa Toro da yara bai damu da halin da ya bar ni a ciki ba.
Ina kuka na d'auki waya na bugawa Baban Marina karon farko da na yi hakan tunda ya aurar da ni. Na kasa magana sai kuka nake yi masa mai tsuma zuciya.
Bai katse ni ba. Sai da na gaji dan kaina na katse wayar.
Baban Marina ya dawo gida cikin sanyin jiki a dalilin yadda kukan Yabi ya buge shi.
Ya leka kofar Dada dan ya bata man zafin da ya siyo mata sai kawai ya ga Tijjani da Nasiba a gefen bisihiyar zogale suna zance. Dada na daki abin ta. Duk da ba yau ya saba ganinsu ba, amma yau din sai da zuciyarsa ta buga da tsananin gaske.
Ya amsa gaisuwarsu cikin k'arfin hali. Ya shiga wajen Dada ya fito, ya fita.
Ya zauna kan tabarma amma zufa ta rufe shi. Ya dinga jin wani iri. Duk yadda ya so jurewa kasa wa ya yi. Yana tambayar kansa yanzu Tijjani yana da rigar da za'a bashi aure ke nan?.
Ya tuna irin kukan da Yabi ta kira ta yi masa dazu, ya san kuka ne na neman agaji, kuka ne mai harshen damo. Daren ranar ya yi masa tsawo ainun.
Washagari ana idar da sallar asuba ya ce Salisu ya raka shi Bauchi.
Tamkar jifa haka Yabi ta gansu. Zuciyarta ta karye. Domin ta hango rauni da wata irin soyayyar ta a kan fuskar mahaifinta.
Tare da Tijjani suka musu iso zuwa falo.
Yana amsa gaisuwarsu ya yi gyaran murya ya ce "Zuwa na yi takanas dan na fad'a miki ce wa ki yi hakuri ki zauna a dakin ki. Ki kuma sauke dukkan hakkina da kika san Ubangiji ya dora miki. Daga nan har zuwa lokacin da Allah ya kaddara muku zaman kada ki yarda ki zalunce shi. Kada kuma ki fito babu izininsa. Aure da kike ga ni darajar sa ta wuce duk zaton mai zato. Sai dai bisa adalcin Ubangiji ya kewaye shi da dokoki da kuma sharudda daban daban. Bai barmu kara zube ba. Ina rokon ki, ki k'ara hak'uri a cikin wannan tsukun da ake son kaimu k'asa da bak'inciki mai tsanani. Idan har kika yarda kika yi hak'uri, ni kuma na miki alkawarin zan jaddada damar da shari'a ta baki na zabin cigaba da zaman ko akasin hakan matukar zalunci da cin fuska ya shigo gidan auren ki".
Cikin kuka da rawar murya na ce "To Babanmu".
Ina fad'in haka ya mik'e tare da ce wa "Allah ya yi miki albarka. Ya fice bai ko bi takan tagwaye da suke ta rige rigen gaishe shi ba. Yaya Salisu ne kawai ya amsa musu tare da ciro ledar alawowi a aljihunsa ya damka kowa tasa ledar.
K'warai Tijjani ya muzanta da yadda suka fice basu bi takansa ba. Ya bi bayansu. Ba jimawa ya shigo ya zauna. Ya ce "Baban Marina ya canja, ya yi bangaranci. To wai a kaina aka fara k'arin aure ne da za'a mini wulakanci irin haka?"
*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633