← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 112 OF 146

Sashe 112

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

✍️

*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*

83&84.
Zaune nake ina duba kayan gyara da na siya a wajen Surayya Halin yau. Domin lokacin haihuwar twins a wajen ta Yaya Ummi ta siya mini kayan da suka gyara ni matuka da gaske har Baban 2 ya dinga tambabar ni na haife su kuwa?.
Tsumin kwakwa ya tayar mini da kwadayinsa da na jima ina yi. Domin dad'i gare shi. Na dauka na sha. Na tashi na je kicin na dauko gwangwanin Madara ta ruwa na fasa. Domin tunda Tijjani ya fara samun sukuni kullum sai na sha gwangwanin Madara. Ban da sauran abubuwan da suke inganta lafiyar jiki.
Na fasa na juye a kofi. Na dawo falo na bude robar koren maganin da na tabbatar da kyaunsa. Na zuba na juya na shanye. Ina hasasho subadin da zan sha yau a wajensa.
Na tattara sauran na kulle dan kada na yi over dose.
Na dauki waya na k'ira shi. Ya amsa na ce "ka taho ne?"
"Eh kina son wani abu ne?"
"Ka taho mini da dabino ko kwakwa ".
Da azama ya ce "Done my little, ban ji hayaniyar 2 ba". Na ce "gasu nan barci suka yi".
Ya ce "Da yammacin nan? Tashe su dan Allah. Bazan yarda da daddare su tisamu a gaba su hana ni hutawa ba".
Na kyalkyale da dariya. Domin nasan nufinsa.
Na mayar da robar y'aya'n gadali domin sai gobe zan ci tunda bani da kwakwa ko dabino a hannuna.

*Akwai kayan Chad masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*. Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntubi marubuciyar Halin yau dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa*.
*08032773332*.

Sosai muke zamana lafiya da taka tsantsan kan abin da zai janyo mana rikici. Na fahimci yajin da na yi, ya sake sawa Tijjani tsoron mu yi fada. Duk da hakan kuma wani loakcin zai fitittke ya yi mini sababin na raina shi, ko akan abu kad'an sai ya tsiri fishi yana fad'in "Tunda Babah ta bani lasisin na dinga yi masa yaji shi ke nan nake yi masa abin da nake so. Dan na ga ba shi da yadda zai yi. Idan yana irin wannan fishin, wani zubin ya bani dariya. Wani lokacin ya bani mamaki. Idan na so sai na rarrashe shi tunda shi haka yake kamar su Hanif wajen son a ritata shi, a tarairaye shi. Wanii lokacin kuwa na share shi, na fi shi fishi. Idan ya lura da hakan sai ya yi maza ya hadiye nasa fishin ya hau lallaba ni.

*Shekara daya a gaba*

Kwanci tashi tagwaye suka yi shekaru uku. Haka muke gurgura rayuwa yadda ta zo. Wataran fari, wataran baki. Zuwa lokacin sosai harkokokin Bulkachuwa suka sake mike wa. Ni kaina ina siyar da dankalin turawa da su karas da atile a cikin gida. Ba kuma k'aramin alheri nake samu ba. Tunda shine yake siyo mini babu maganar kudin kawowa. Idan na siyar na cire riba na ba shi kudin sai ya sake siyo mini wasu. A hakan har na tara jarina ba tare da na zuba wani kudin ba. Dan haka na ware kudinsa na ba shi, tare da yi masa bayanin yadda kudaden suka haihu dan haka zan cigaba da yi da nawa. Yana bude baki sai ce wa ya yi wadananan din ma naki ne. Kin tuna bashin da kika yi ta ranta mini a lokacin da bani da shi?". Na girgiza lai na ce " A a tsakanina da kai babu bashi Baban 2. Ba ka dauke ni yadda na dauke ba Wallahi." Da azama ya ce "Na gode, na yarda babu bashi. To na ba ki kyauta.
Na murmusa na ce "Ka dai biya ni kawai. Shike nan na gode, Allah ya kara budi da lafiya." Ya amsa da "Ameen maman 2."
Ya kanne mini ido tare da ce wa "Na kosa a yiwa su twins Gambo fa".
Na yi dariya na mike na bar shi dan yanzu sai ya fara tsokana ta akan abubuwan da na yi ta yi masa a baya.
Muna cikin haka babu zato sai ga shi ya zo mini da takardar da take nuni na samu gurbin karatu a kwalejin ilimi ta jihar Bauchi.
Ban yi murna ba, domin tun filazal na fi son na yi kasuwanci. Na kuma fahimci Ubangiji ya sanya mini nasibi a cikin juya kudi. To akan me zan damu kaina sai na yi karatun da babu garantin zan ci moriyarsa tunda kullum kasar sake lalace wa take yi. Aikin gwamnati siyar da shi ake yi da makuden kudade, sai kana da hanya ma da ka samu a siyar maka d'in.
Bai yi fishi ba, ya zauna ya dinga zayyano mini tasirin ilimi a wajen mace ba dan ta yi aiki ta samu kudi ba ne kawai. Ilimin mace da gogewarta na taimaka mata k'warai wajen bawa yara tarbiya da sanin yadda zata yi cudanya da mutane daban daban. Ya sanyaya murya ya ce "Ki daure ki sawa zuciyar ki soyayyar karatun nan Asiya dan sai kin yi shi. Fata na ke yi ko na mutu a ce ke din kina da wata madagora da zaki rik'e mini y'aya'na. Duk duniya ke nake da tabbacin ba zaki gaza da hidimarsu ba. Daure ki bani hadin kai mana".
Na dinga kuka domin idan yana irin wannan maganganun gabadaya kidime wa nake yi. Shi kuma baya fasa fada mini lokaci zuwa lokaci, tamkar mai son na yi haddarsu. Tare muka fara makaranta da su Hanif. Domin Nursery da take cikin college din ya snaya su. Da kansa yake kai mu. Sai ya wuce garin da zai je. Bama koma wa gida sai na gama daukar darussa.
Komawa ta makaranta sai ta jawo takaddama mai yawa a cikin gidan Marina. Domin a tarihin gidan ni ce na kammala sakandire har na fara ta gaba da ita da kuma aurena. Dada ta dinga sababin ya rungumi BAK'AR TA'ADAR arna masu barin matansu suna cud'anya da mazaje kullum da sunan neman ilimi. Babu kishi babu komai. Alhalin ma'aiki ya ce wanda baya kishin iyalin sa babu shi babu jin kamshin aljanna.
Yanzu gabadaya gidan Marina ni na tsole ido. Rufin asirin da muke ciki ya na matukar mintsinin ahalin gidan.
Bana damuwa tunda ba a garin nake ba. Wani abin ma har a yi yamididinsa a gama bana ji bare raina ya baci a banza.
Chapter 112 · 0% Book details