Sashe 21
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na ce zai bari ne, domin ko Yaya Jabir ne autan maza na bar shi Nazira".
Ta ru'ko hannuna ta ce "Madallah da zuciyar Yabin Marina! Ni nasan zuciyarta ba zata cigaba da son wanda zata yi kuka a hannun ahalinsa ba, ba zata so wanda ubansa yake k'yamarmu ba, in sha Allah sai kin auri wanda ya fishi komai, aurensa da Maijidda kuma bama adawa. Sai kuma kuka ya goce mata, nima hawaye ya sake zubo mini, domin idan na ce bana sonsa ko abin bai dame ni ba na yi k'arya.
Amma zan nuna wa su Baban Tsakiya ni din yar halak ce ina kishin ubana, ina kuma kishin kaina.
Babban rufin asirin da Allah ya yi mini shine dama ina da Abdulrashid. Su biyun duk ina sonsu amma nafi son Yaya J.
Yafi daukar hankalina matu'ka da gaske sai dai zan iya rayuwa da Abdul ba tare da na takura ba.
Sai da muka yi kukanmu son ranmu sannan muka je gidan Yaya Salamatu, muka bata labarin halin da ake ciki.
A sanyaye ta ce "Babanmu ne basa so fa, gara miki ma hakan, Allah ya kawo miki mafi alheri me za'a yi ma da auren dangi irin namu ne?"
Mun jima sosai sannan muka tafi, bayan na bata labarin Malam Yunus da yake son Nazira.
Ta yi murna, ta yi farin-ciki, ta bamu dari biyar mu hau mashin. Bayan ta bawa Nazira kaya a leda ta kaiwa Mamansu.
Na koma gidan Yaya Salisu, su kuma suka wuce gida.
Kwanana shida da barin gida sai ga Yaya J a gidan Yaya Salisu.
A matu'kar birkice na ganshi.
Ya kasa mini magana, tsawon lokaci kafin ya ce "Me yasa haka Yabi?"
Ba walwala na ce "me yasa, me ke nan?"
Ya ce "na dauka ko baki ha'da komai da su Baban Tsakiya ba zasu ci darajata bare kuma iyayenki ne da zasu daura miki aure".
Na bata rai na ce "Bana ma bukatar su mini walittaka Jabir, domin komin kashin Babanmu da ake ga ni, Ubangiji ya azurta shi da yara mazan da zasu maye mana gurbin kowa.
Kai ko ba ni da yan'uwa maza a cikin gidan Wallahi Ammar da Bulkachuwa zasu iya daura mini aure duk da kasancewarsu ya'yan mata ne, amma idan har ya kasance sai ku to lah shakka zan iya saka hula na wakilci kaina ko kuma na samu alkali ko liman".
Jikinsa ya yi matu'kar yin laushi.
A sanyaye ya ce "Ni yanzu mene ne laifina a nan Yabi?'
Yana rufe baki na ce "Rashin biyayyar ka. Na tabbatar an fa'da maka ka kiyaye ni, domin ban cancanci ka aure ni ba, saboda mahaifina ba shi da daudar duniya".
Ya yi kasa da kansa ya ce "Ni da ke muke magana ki daina sako mini manyanmu domin wannan ba dabi'a ce mai kyau ba.
Na gallah masa harara na ce "Madallah"
Na tsuke bakina na yi gum.
Ya marairaice ya ce "Yabi kada ki bari a bada kofar da za'a yi mana farraku, ina son ki, ina kaunar kasance wa da ke, jikina na bani kamar ma na kusa barin duniyar nan, ki taushi zuciyarki kada ki zalunci wanda yake tsananin sonki Yabi. Ban miki komai ba, kada ki hukunta ni da laifin da bani na yi miki shi ba".
Jikina ya yi sanyi. Na kasa magana domin gaba'daya ya d'aure ni da jijiyoyin jikina. Zufar da take karyo masa ta sanya na sake jin sonsa na taso mini.
Kafin na yi magana sai kawai na tuno maganganun mahaifinsa a kaina, wai ni da nake matsayin y'arsa, yar dan-uwansa amma ya jefe ni da mafi munin kalma wai ina bin maza, ke nan karuwa ce?
Bayan ga hakan kuma ya ci mutuncin mahaifina wanda wansa ne.
Take na ji karshen jakanci ne na cigaba da mua'amalantar jininsa da sunan soyayya.
Mussaman da ya ce yana tausayin zuri'ar da d'ansu zai kwaso musu ni.
Na dago cikin karfin zuciya na ce "Jabir mu yi datse wannan soyayyar ka ji, na rantse maka tun jiya na shak'e ta, na kwashe mata karama.
Babanka ya tabbatar mini Maijidda ya za'ba maka, domin ita ce arzikin ubanta yayi daidai da shi, ban yi ba'kin ciki ba, domin kullum zabin Allah muke nema.
Alhamdulillah! Na karbi wannan kaddarar da hannu bibbyu, domin Ubangiji na bar wa al'amarin, ya yi mana za'bi da kansa.
Amma zan roke ka Yaya Jabir ka yi iya kokarinka wajen taka burki a ta'ba mutuncin Baban Marina da ahalinsa.
Ina jin tsoron kada wannan matsalar ta yi girman da ba zata gyaru ba.
Ina jin tsoron kada a wayi gari a ga gidan Marina ya zama sansanin yaki a tsakanin jini guda".
A matu'kar birkice ya ce "Allah kada ya kaddara mini ganin hakan Yabi! Ina fatan mutuwa ta riske ni kafin wannan lokacin"
Na girgiza kai na ce Shi kenan".
Ya marairaice ya ce "Na tsugunna miki Yabi Asiya?
Ki taimake ni, ki fahimce ni, idan kin kwantar da hankalinki ai za'a a samu sulhu ta sanadin aurenmu.
Sai mu kawo dai-daito, an yi abin da yafi haka muni, kuma an dawo an shirya, kada ki tsananta, ki yanke mini hukuncin da babu laifina. Allah da kansa baya kama mu da laifin iyayenmu ko na y'ay'anmu. Daure ki ji tausayina, na rantse idan kin bani ha'din kai ba abin da zai sa na bar ki komai za'a yi kuwa" .
Na girgiza kai na ce "Idan na yi hakan ba sonka nake da gaske ba.
A gaban iyayenmu Baban Tsakiya ya ce "Idan aka baka aurena Àllah ya isa.
Baya ga hakan kuma ya tsane ni, tsanar da ya danganta ni da karuwa ce ni, kuma ya ce na zage su, hakan ya janyo ubana ya kore ni saboda shi kullum yana sonsu, yana musu kyakkawan zato".
Daga haka kuma sai kuka ya subuce mini.
Bai hana ni yi ba, shima kuma idonsa ya ciko jijiyar kansa ta yi rud'u rud'u tabbacin yana cikin rud'u mai girma.
Da murya kuka na ce "Maijidda ta fini kyau, ta fini gata tunda Babanta mai ku'di ne, ta fini komai, ka karbi zabin iyayenka na tabbatar Ubangijin adalci zai juya maka al'amarint fiye da al'amarina, tunda ka yi biyayya.
Zan fa'da maka gaskiya ko zan yaudari kowa bazan yaudare ka ba. Kana da muhimmanci a rayuwata, da gaske ina ganin mutuncin ka.
Na roki arzikin ka rabu da ni, na riga na ha'kura da kai Wallahi, maganar soyayya kam ta kau".
Ya numfasa ya ce "Oh! Haka kaddara ta za'ba mini? Na so ace kin saurare ni, na so ace kin bani dama mun ha'da hannu da k'arfe mun yaki wannan *BAK'AR TA'ADAR* da take neman zame wa alummarmu tamkar wutar jeji.
Ina cikin zullumin yadda zumuncin yau ya koma tsakanin masu kumbar susa.
Ina cikin takaicin yadda aka jahilci d'an-uba.
Ina matu'kar so a ce kin zama matata ta yadda zamu kawo cigaba ta fuskar zumunci a cikin zuri'armu ta hanyar mua'amalantar kowa da girmama wa.
Amma babu komai, mu ci gaba da addu'a Allah baya juyar da addu'ar masu kyakkawar manufa".
Ya saka hannu ya zaro hankicif ya fara goge zufar tashin hankali da take yanko masa, kalaman sa ba k'aramin sukurkuta ni suka yi ba.
Amma na yi jarumtar waske wa domin har cikin zuciyata nake jin ban cancanci na zama cikin ahalin Baban Tsakiya ba.
Ya kasa cewa tsawon lokaci sannan ya yi karfin halin cewa "Fatan alheri mai yawa gare ki Yabin J".
Sai ya dawo da sauri cikin rawar murya ya ce "Yanzu kin mini adalci idan kika jingina sunan ki da wani na?
Yanzu kin manta komai, bani da wata alfarma a wajen ki?"
Na yi kasa da kaina na ce "Alfarmomi masu yawa kuwa .
"Kai na fara so, kai kawai nake yiwa uzziri da sassauci bayan iyayena, sannan idan akwai wanda na yarda da son da yake mini to kuwa kai ne.
Sai dai ko kusa bazan yaudari kaina ba.
Iyaye girmansu yawa ne da su, Annabi (S.A.W) ya yi ta jan hakankalinmu akan mubi su.
Idan kuwa hakane zan gwada maka cikakkiyar soyayya ta hanyar dora ka akan turba sahihiya, iyayenka duka biyu basa son almarinka da ni.
Dan haka ka bar son zuciyarka, ka musu biyayya, na yi imani Ubangiji ba zai barka haka ba".
Daga haka na fashe da azababben kuka.
Jikinsa ya dinga kyarma ya ce "Na sani kina sona. Na roki arzikin, ki mini uzziri, kar ki ce mu rabu, mu bar wa Allah ya yi mana za'bi, mu yi addu'a mu ga ni. Jikina bai bani akwai namijin da zai aure mini ke alhalin ina numfashi a wannan duniyar ba".
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.
*BAKAR TA'ADA*
*NA*
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*
*(MRS M.I.NASHE)*
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*ALBISHIRINKU*
*MASOYAN LITTAFAN MARUBUCIYA HAFSAT C SODANGI*!
*DUBA DA YADDA KUKE KEWAR RUBUTUNTA YA SANYA TA YI SHIRIN SAKE DAWOWA DAN TA SAKE MUKU WANI RUBUTUN SABO DAL*
*AMMA KAFIN HAKAN TA DAWO MUKU DA TSOFAFFIN LITTAFAN TA ZUWA KAN WAYA, DAN KU SAKE BITA TARE DA NAZARIN KYAWAWAN SAKON DA TAKE NUFIN ISARWA GAREMU*.
*A YANZU HAKA LITTAFAI HUDU NE RIGIS*
*WAYYO DUNIYA 1-3*
*KYAUTATA 1-3*
*DAGA K'IN GASKIYA 1-3*
*MATA MASU DUNIYA 1-3*
*KO WANNE 1K NE AMMA AKWAI DISCOUNT IDAN ZA'A SIYA SAMA DA GUDA DAYA*
*MISALI GUDA BIYU-1500*
*GUDA UKU 2500*
*GUDA HUDU 3500*
*ZA'A TURA KUDIN TA ASUSUN MARUBUCIYAR KAMAR HAKA*
*0082739293, ACCESS BANK HAFSAT YUNUS ABDULLAHI*
*SAI A TURO MINI SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*SAI NA BADA LITTAFIN DA AKE SO*
*MADALLAH DA KARFAFA GUIWARKU*
*MADALLAH DA SOYAYYARKU GA RUBUTUNMU*
*AKWAI LITTAFANTA SAMA DA GUDA GOMA DA A YANZU SUKE SOFT COPIES, KAWAI KI TAMBAYI DUK WANDA KIKE NEMA A WAJENA CIKIN LITTAFANTA NA BAYA*.
Ta ru'ko hannuna ta ce "Madallah da zuciyar Yabin Marina! Ni nasan zuciyarta ba zata cigaba da son wanda zata yi kuka a hannun ahalinsa ba, ba zata so wanda ubansa yake k'yamarmu ba, in sha Allah sai kin auri wanda ya fishi komai, aurensa da Maijidda kuma bama adawa. Sai kuma kuka ya goce mata, nima hawaye ya sake zubo mini, domin idan na ce bana sonsa ko abin bai dame ni ba na yi k'arya.
Amma zan nuna wa su Baban Tsakiya ni din yar halak ce ina kishin ubana, ina kuma kishin kaina.
Babban rufin asirin da Allah ya yi mini shine dama ina da Abdulrashid. Su biyun duk ina sonsu amma nafi son Yaya J.
Yafi daukar hankalina matu'ka da gaske sai dai zan iya rayuwa da Abdul ba tare da na takura ba.
Sai da muka yi kukanmu son ranmu sannan muka je gidan Yaya Salamatu, muka bata labarin halin da ake ciki.
A sanyaye ta ce "Babanmu ne basa so fa, gara miki ma hakan, Allah ya kawo miki mafi alheri me za'a yi ma da auren dangi irin namu ne?"
Mun jima sosai sannan muka tafi, bayan na bata labarin Malam Yunus da yake son Nazira.
Ta yi murna, ta yi farin-ciki, ta bamu dari biyar mu hau mashin. Bayan ta bawa Nazira kaya a leda ta kaiwa Mamansu.
Na koma gidan Yaya Salisu, su kuma suka wuce gida.
Kwanana shida da barin gida sai ga Yaya J a gidan Yaya Salisu.
A matu'kar birkice na ganshi.
Ya kasa mini magana, tsawon lokaci kafin ya ce "Me yasa haka Yabi?"
Ba walwala na ce "me yasa, me ke nan?"
Ya ce "na dauka ko baki ha'da komai da su Baban Tsakiya ba zasu ci darajata bare kuma iyayenki ne da zasu daura miki aure".
Na bata rai na ce "Bana ma bukatar su mini walittaka Jabir, domin komin kashin Babanmu da ake ga ni, Ubangiji ya azurta shi da yara mazan da zasu maye mana gurbin kowa.
Kai ko ba ni da yan'uwa maza a cikin gidan Wallahi Ammar da Bulkachuwa zasu iya daura mini aure duk da kasancewarsu ya'yan mata ne, amma idan har ya kasance sai ku to lah shakka zan iya saka hula na wakilci kaina ko kuma na samu alkali ko liman".
Jikinsa ya yi matu'kar yin laushi.
A sanyaye ya ce "Ni yanzu mene ne laifina a nan Yabi?'
Yana rufe baki na ce "Rashin biyayyar ka. Na tabbatar an fa'da maka ka kiyaye ni, domin ban cancanci ka aure ni ba, saboda mahaifina ba shi da daudar duniya".
Ya yi kasa da kansa ya ce "Ni da ke muke magana ki daina sako mini manyanmu domin wannan ba dabi'a ce mai kyau ba.
Na gallah masa harara na ce "Madallah"
Na tsuke bakina na yi gum.
Ya marairaice ya ce "Yabi kada ki bari a bada kofar da za'a yi mana farraku, ina son ki, ina kaunar kasance wa da ke, jikina na bani kamar ma na kusa barin duniyar nan, ki taushi zuciyarki kada ki zalunci wanda yake tsananin sonki Yabi. Ban miki komai ba, kada ki hukunta ni da laifin da bani na yi miki shi ba".
Jikina ya yi sanyi. Na kasa magana domin gaba'daya ya d'aure ni da jijiyoyin jikina. Zufar da take karyo masa ta sanya na sake jin sonsa na taso mini.
Kafin na yi magana sai kawai na tuno maganganun mahaifinsa a kaina, wai ni da nake matsayin y'arsa, yar dan-uwansa amma ya jefe ni da mafi munin kalma wai ina bin maza, ke nan karuwa ce?
Bayan ga hakan kuma ya ci mutuncin mahaifina wanda wansa ne.
Take na ji karshen jakanci ne na cigaba da mua'amalantar jininsa da sunan soyayya.
Mussaman da ya ce yana tausayin zuri'ar da d'ansu zai kwaso musu ni.
Na dago cikin karfin zuciya na ce "Jabir mu yi datse wannan soyayyar ka ji, na rantse maka tun jiya na shak'e ta, na kwashe mata karama.
Babanka ya tabbatar mini Maijidda ya za'ba maka, domin ita ce arzikin ubanta yayi daidai da shi, ban yi ba'kin ciki ba, domin kullum zabin Allah muke nema.
Alhamdulillah! Na karbi wannan kaddarar da hannu bibbyu, domin Ubangiji na bar wa al'amarin, ya yi mana za'bi da kansa.
Amma zan roke ka Yaya Jabir ka yi iya kokarinka wajen taka burki a ta'ba mutuncin Baban Marina da ahalinsa.
Ina jin tsoron kada wannan matsalar ta yi girman da ba zata gyaru ba.
Ina jin tsoron kada a wayi gari a ga gidan Marina ya zama sansanin yaki a tsakanin jini guda".
A matu'kar birkice ya ce "Allah kada ya kaddara mini ganin hakan Yabi! Ina fatan mutuwa ta riske ni kafin wannan lokacin"
Na girgiza kai na ce Shi kenan".
Ya marairaice ya ce "Na tsugunna miki Yabi Asiya?
Ki taimake ni, ki fahimce ni, idan kin kwantar da hankalinki ai za'a a samu sulhu ta sanadin aurenmu.
Sai mu kawo dai-daito, an yi abin da yafi haka muni, kuma an dawo an shirya, kada ki tsananta, ki yanke mini hukuncin da babu laifina. Allah da kansa baya kama mu da laifin iyayenmu ko na y'ay'anmu. Daure ki ji tausayina, na rantse idan kin bani ha'din kai ba abin da zai sa na bar ki komai za'a yi kuwa" .
Na girgiza kai na ce "Idan na yi hakan ba sonka nake da gaske ba.
A gaban iyayenmu Baban Tsakiya ya ce "Idan aka baka aurena Àllah ya isa.
Baya ga hakan kuma ya tsane ni, tsanar da ya danganta ni da karuwa ce ni, kuma ya ce na zage su, hakan ya janyo ubana ya kore ni saboda shi kullum yana sonsu, yana musu kyakkawan zato".
Daga haka kuma sai kuka ya subuce mini.
Bai hana ni yi ba, shima kuma idonsa ya ciko jijiyar kansa ta yi rud'u rud'u tabbacin yana cikin rud'u mai girma.
Da murya kuka na ce "Maijidda ta fini kyau, ta fini gata tunda Babanta mai ku'di ne, ta fini komai, ka karbi zabin iyayenka na tabbatar Ubangijin adalci zai juya maka al'amarint fiye da al'amarina, tunda ka yi biyayya.
Zan fa'da maka gaskiya ko zan yaudari kowa bazan yaudare ka ba. Kana da muhimmanci a rayuwata, da gaske ina ganin mutuncin ka.
Na roki arzikin ka rabu da ni, na riga na ha'kura da kai Wallahi, maganar soyayya kam ta kau".
Ya numfasa ya ce "Oh! Haka kaddara ta za'ba mini? Na so ace kin saurare ni, na so ace kin bani dama mun ha'da hannu da k'arfe mun yaki wannan *BAK'AR TA'ADAR* da take neman zame wa alummarmu tamkar wutar jeji.
Ina cikin zullumin yadda zumuncin yau ya koma tsakanin masu kumbar susa.
Ina cikin takaicin yadda aka jahilci d'an-uba.
Ina matu'kar so a ce kin zama matata ta yadda zamu kawo cigaba ta fuskar zumunci a cikin zuri'armu ta hanyar mua'amalantar kowa da girmama wa.
Amma babu komai, mu ci gaba da addu'a Allah baya juyar da addu'ar masu kyakkawar manufa".
Ya saka hannu ya zaro hankicif ya fara goge zufar tashin hankali da take yanko masa, kalaman sa ba k'aramin sukurkuta ni suka yi ba.
Amma na yi jarumtar waske wa domin har cikin zuciyata nake jin ban cancanci na zama cikin ahalin Baban Tsakiya ba.
Ya kasa cewa tsawon lokaci sannan ya yi karfin halin cewa "Fatan alheri mai yawa gare ki Yabin J".
Sai ya dawo da sauri cikin rawar murya ya ce "Yanzu kin mini adalci idan kika jingina sunan ki da wani na?
Yanzu kin manta komai, bani da wata alfarma a wajen ki?"
Na yi kasa da kaina na ce "Alfarmomi masu yawa kuwa .
"Kai na fara so, kai kawai nake yiwa uzziri da sassauci bayan iyayena, sannan idan akwai wanda na yarda da son da yake mini to kuwa kai ne.
Sai dai ko kusa bazan yaudari kaina ba.
Iyaye girmansu yawa ne da su, Annabi (S.A.W) ya yi ta jan hakankalinmu akan mubi su.
Idan kuwa hakane zan gwada maka cikakkiyar soyayya ta hanyar dora ka akan turba sahihiya, iyayenka duka biyu basa son almarinka da ni.
Dan haka ka bar son zuciyarka, ka musu biyayya, na yi imani Ubangiji ba zai barka haka ba".
Daga haka na fashe da azababben kuka.
Jikinsa ya dinga kyarma ya ce "Na sani kina sona. Na roki arzikin, ki mini uzziri, kar ki ce mu rabu, mu bar wa Allah ya yi mana za'bi, mu yi addu'a mu ga ni. Jikina bai bani akwai namijin da zai aure mini ke alhalin ina numfashi a wannan duniyar ba".
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*.
*BAKAR TA'ADA*
*NA*
*SURAYYA DAHIRU GWARAM*
*(MRS M.I.NASHE)*
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*ALBISHIRINKU*
*MASOYAN LITTAFAN MARUBUCIYA HAFSAT C SODANGI*!
*DUBA DA YADDA KUKE KEWAR RUBUTUNTA YA SANYA TA YI SHIRIN SAKE DAWOWA DAN TA SAKE MUKU WANI RUBUTUN SABO DAL*
*AMMA KAFIN HAKAN TA DAWO MUKU DA TSOFAFFIN LITTAFAN TA ZUWA KAN WAYA, DAN KU SAKE BITA TARE DA NAZARIN KYAWAWAN SAKON DA TAKE NUFIN ISARWA GAREMU*.
*A YANZU HAKA LITTAFAI HUDU NE RIGIS*
*WAYYO DUNIYA 1-3*
*KYAUTATA 1-3*
*DAGA K'IN GASKIYA 1-3*
*MATA MASU DUNIYA 1-3*
*KO WANNE 1K NE AMMA AKWAI DISCOUNT IDAN ZA'A SIYA SAMA DA GUDA DAYA*
*MISALI GUDA BIYU-1500*
*GUDA UKU 2500*
*GUDA HUDU 3500*
*ZA'A TURA KUDIN TA ASUSUN MARUBUCIYAR KAMAR HAKA*
*0082739293, ACCESS BANK HAFSAT YUNUS ABDULLAHI*
*SAI A TURO MINI SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*SAI NA BADA LITTAFIN DA AKE SO*
*MADALLAH DA KARFAFA GUIWARKU*
*MADALLAH DA SOYAYYARKU GA RUBUTUNMU*
*AKWAI LITTAFANTA SAMA DA GUDA GOMA DA A YANZU SUKE SOFT COPIES, KAWAI KI TAMBAYI DUK WANDA KIKE NEMA A WAJENA CIKIN LITTAFANTA NA BAYA*.