Sashe 77
Uwa Ko Ukuba Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Gama kushe dakin Mom tayi sannan tayi shiru tana kallon Asmeey dake kneeling agabanta kanta akasa jikinta na rawa uppan bata ceba, jakanta Mom tabude taciro wani abu a black leather tamika mata tace “stand up and take this hide it inda babu wanda zai gani” tashi Asmeey tayi jikinta na rawa ta karba tawuce wajen wardrobe tabude ta boye ledan a karkadhin kayanta sannan tadawo tasake kneeling agaban Mom, Mom takalleta ji take kaman tasa kafafunta ta murje wuyanta ta mutu amman tadaure, yanda takara kyau abin namata ciwo but ta daure da kyar tace “stand up and carry your hijab” mikewa Asmeey tayi tawuce wajen wardrobe tadauko hijabinta gabanta na faduwa, Mom tace “sakashi” sakawa tayi, Mom tanuna mata kofa tace “wuce mutafi auren yakare!” Bugawa kirjin Asmeey yayi sosai dan kallon Mom tayi, dudda gabanta na mahaukacin faduwa amman ta daure ta dake jin Mom nacemata auren yakare tace “ina z……” kwata kwata maganan ya makale mata awuya sabida kallon da Mom ta mata, strictly Mom tace “are you questioning me Asmeey? Koko gezo idanuna ke miki? Koko ciwon kunne yasa naji kaman kin tambayeni ina zaki?” Girgizamata kai tayi tana kuka tace “Y….a yace…..kar…..kar….na…..na……fiii……” Mom tadaga murya tace “ni kike gayama Yaya yace karki fita? Ni Asama’u?” Mamaki yawani kalan cinye Mom ganin Asmeey kaman tarage shakkan ta dan wlh ada Asmeey bata isa tace mata wane kaza ko kaza ba, Mom ta buga kirji tace “nadaukeki acikina! For 9months! Na raineki! Na haifoki! Nature you kawowa this day, Asmeey ni mahaifiyarki kike cema ina zan kaiki? That tababben yaron nan yace karki fita”? Girgizama Mom kai tayi tana kuka wani tsoro na tarwatsa mata zuciya, Mom tace “okay sabida kinyi aure kin zauna awannan wulakantaccen dakin karo karo dawani gantalallan yaro da iyayensa ke ciyarwa har yau! Tufatarwa har yau! Basa makwanci har yau shine kike kike tambayana ina zankaiki kehh! Tufiakwa!” Kasa Asmeey tafarayi tana dukawa cus Mom tafara maganganun nan saitaji rayuwanta na hargitsewa Mom tazo wajen, batai wata wata ba ta daga kafanta da takalminta ke kai mai tudu tawani daki kan Asmeey tace “na kasheki na kashe banza wulakantacciya!” Jikake kummm goshin Asmeey da kanta gabaki daya sun daku da katakon gadosu, gindin tundun takalmin Mom yasa goshinta ya fashe saiga jini wajen na kulu lokaci daya sai kawai Mom ta duko takalleta yanda kan Asmeey ke kasa tana kuka ta rakube da gado kaman marainiya, Mom takai yatsanta takama habanta tadago da fuskanta tace “kalleni nan!” Kallonta Asmeey tayi jikinta na tsuma na kuka tana makyarkyata bamata iya kallon Mom sosai tsabagen tsoranta kaman wata doddanniya haka Asmeey ke ganin Mom, cikin wani irin murya Mom tace “tsakanina dake is biyayya Asma’u sabida ke diyata ce, duk randa kikace bazakini ba bakida ragowan amfani a duniyan nan!” Mom ta nuna mata wardrobe tace “kinga ledan chan maganin bera ne aciki full sachet! Idan you refuse to come with me you choose here kinyi choosing mijinki bakida ragowan amfani aduniya makesure kin dauki maganin chan kin ci inaso naji sanarwan mutuwanki da gaggawa shiyafima rayuwata alkhairi naga kin mutu!”Mom tai maganan batare data daga murya ba Asmeey tawani irin kallonta tana nishi tanaji kaman ma mutuwan na zuwan mata yanzu, Mom tace “since you are torn between Mahaifinki, ni, dakuma mijinki, idan baki bini ba nima na jaye permission na barinki kicigaba da numfashi aduniya your live belongs to me Asmeey! Menace?” Bakın Asmeey nawani kalan bari batama iya maganan da kyau sabida yanda Mom tarike mata habba tace “my life belongs to you Mom!” Wani kalan kallo Mom tamata ido cikin ido tace “na tsaneki Asma’u! Na tsaneki! Ke Allah ya halakaki mutuwan ma banso kiyi ta sauki! Nakawo Fawaz nace shinakeso ki aura ki zabi mahaukaci! Arayuwanki kap ni uwarki niyakamata kibi zabinta not zabin mahaifinki or this jobless boy! I made you Asmeey! You become human in my tummy, and u come to this world through my vagina so kawani yaro mahaifiya ke da iko dashi not uba saisa Annabi ya ambato uwa sau uku kafin uba!” Wani irin ijiyan zuciya Asmeey take tana kallon Mom kallon wat is left again? Rayuwanta yagama yawo? Mom tasaki kumatunta tamike tawuce “tashi mutafi” wlh kasa motsi Asmeey tayi maganganun Mom yasa taji kaman she’s brain dead sai hawaye dake sauka daga idanunta kawai, juyowa Mom tayi ganin Asmeey batai motsi ba mamaki na kashe Mom ganin Asmeey ta chanza tace “badake nake magana ba? Wuce muje someone need to see you!” Ko gezau Asmeey batayiba kaman ma bata hayyacinta, Mom batai wata wata ba tazo wajen ta duko ta daura mata mari dayasa Asmeey taji she’s not just brain dead yanzu she went blind Mom tai ihu da duka gidan ya amsa. “Wuce muje nace kin gama zama da mahaukaci ma kashe auren!” Daidai lokacin aka bude kofan dakin Mamie ta shigo idanunta kan Asmeey dake duke gaban gado tarakube kaman mussa ga jini nabin goshinta dayayi kululu kumatunta yayi jajir hannuwan Mom sun fito radau, dasauri Mom tai wajen Asmeey taduka tanakai hannunwanta tataba goshinta tace “Asmeey! Asmeey! Innalillahi! Asmeey!” Ko motsi Asmeey batayiba, Mom azuciye tace “Hamida tashi kibar wajen nan ko ranki yabaci yanzun nan, zan miki duk abinda yazo raina wallahi, you keep coming between me and my daughter ubanwa yataba coming between ke da yaranki”? Sakin Asmeey Mamie tayi ta taso batai wata wata ba tawani kalan tura Mom Mom ta bugu da kofa azuciye Mamie tace “bar gidan nan! Get out of my house!” Mom tayi wani dariyan keta ta nuna gidan tace “is this wat you call house? This useless 90s house? Yes I am going but da y’ata idan kin isa kihanani” Mamie nawani kalan kallon Mom tace “Salima bantaba ganin wata Uwa dana kalla naji araina cewa she don’t deserve to be a mother arayuwana ba saike! Salima kin dauka abin adone yara sudingajin tsoron iyayensu haka? This is not flex halin nan da dabi’an nan yasa duk na raina iliminki! Your education, qualifications is rubbish is utterly nonsense, kina part of human right activist yet you abuse this poor innocent girl kullum kullum! Koda agidan karuwanci, cikin shege, a turakan karuwai kika haifeta banjin you will be treating this poor child like a goat or jaka hakaba! What is her mistake? What is her sin? Me Asmeey tayi? Look at her! She is just an innocent little girl da all she wants is Mamanta tasota, just look at her face for once arayuwanki with love! Me Asmeey tamiki? What is her crime Salima? Metayi? Metayi? Metayi miki tell me why are you hurting Asmeey na? What did this bright young smart child did to you Salima menene gayamin?” Mamie tafashe da kuka dan yau takasa rike zuciyanta abin namata ciwo, tanunama Mom dake kallonta hannunta dakeda jinin Asmeey na goshinta Mamie nawani kalan kuka tace “look at blood na yarki? Salima wanda ta sanadinki yake zuba! Look at hannunta akarye ta sanadinki! Dubi jikinta duk kene Salima me Asmeey tamiki ehhhhhhh? Menene? Why this much hate for yarki dakika haifa da kanki, why why why do you want Asmeey dead? Sai kinga gawanta zaki huta? What did this poor girl do? Ki gayamin cus azaban yayi yawa, ina gujemiki alhaki fa! Wata rana zaki nadaman abubuwan dakikama yarinyar nan ki rubuta ki ijiye, Salima kiji tsoron Allah” lumshe idanu Mom tayi tabudesu takalli Mamie tace “kinga yanda kika hankadani na bugu da kofa na yafe miki sabida naga kin tsufa jikinki ya gajiya amman kika kara kuskuren tabani saina miki jina jini wallahi tallahi, y’a dai nina haifa ba ke ba ko, ko sokamata wuka nake ba ruwanki! Abarmin kayana! Ninayi wahalanta tun tana yar kunzugu, tashinmini agaba nadauki y’ata mubar gidan nan” tsayuwa Mamie ta gyara tace “idan kin fita da yarnan daga gidan nan saidai idan nafadi anan na mutu Salima!” Ijiye jaka Mom tayi akasa tace “hahaa inaga Asmeey bata gayamuku wacece mahaifiyarta ba, tashi Salima nace” Mamie tace “kome zakimin kimin yanda kika tsani yarnan zan gwada miki akwai wayanda zasu iya basu ranta just to protect her, Salima kasheni shine abinda zaisa ki dauki Asmeey, do your worst” wani irin yunkurowa Asmeey tayi tana layi kanta ya bugu, wani dummm yake mata but tanajin hayaniyan Mom da Mamie hakan yasa ahankali tace “Mamie karki fada da Mom sabida ni Mamie yakuri”maganan da Asmeey takeyi kadan kadan yasa Mamie tajuyo tana kallonta tana kokarin dukawa tama Asmeey magana Mom tawani pushing Mamie mercilessly Mamie tayi mummunan faduwa ta bugu ta desk da chair na Hamad laptop dinsa da desktop suka fado kanta tana kokarin tashi takasa tarufe idanu kaman ta mutu.
EPISODE 4️⃣3️⃣
EPISODE 4️⃣3️⃣