Sashe 98
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Malama tun da ba da ke ake ba ki yi shiru mana kuma ai zuwa da kai ya fi saƙo sannan gani ya kori ji shi da idanunsa suka ga abin da ya faru tamabayar mai zai yi"
Nasir shu takaicinsa É—aya ma da suka saka ya fito da kuma a jikinsa ko wanka bai gama ba, shi ua rasa wannan wace irin rayuwa cw kuma wace irin cakwakiya ce a ce kullum sai sun zo nan za su dafa abin da za su ci hakan ya sa ya ce
"Meenal mai ya sa kika musu ihun ɓarayi?"
Meenal duk da ta ji haushin tambayar ganjn kamar ma ita yake son É—orawa laifi sai ta É—ago masa ledar ta ce
"Dankali Hibba ta sata suka saka aljihu shi ne Allah ya toni asiri su na gani"
Hibba sai ta ji duk kunya ta kamata shi kuma sai ya ma rasa abin cewa sai Husna ta ce
"Yaya dankalin ne fa takr bamu kaɗan ba ya isarmu kullum sai dai mu yi kashi kamat wasu mararsa galihu, shi ne muka ƙara yawan dankalin da muka soya muka kwasa yadda zai ishemu" Ya ɗanyi shiru ya ce
"Kuma sai ku ɗauka bakwa cewa ta ƙara muju wanda take baku ba ya isa"
Hibba ta ce
"Ka ga fa É—an wanda take bayarwa bai fi cikin mutum É—aya ba"
Ganin dankali ransa ya ɓaci kamar wanda aka roƙa ganin yana neman yarda da maganrsu Mrenal ta ce
"Ƙarya suke munafukai ne wallahi a kicin suke tsayawa su cin iya cinsu sai su kai ɗan kaɗan gida, amma ya za a yi na zuba musu wannan" ,Gabaɗaya ma sai ya rasa maganst wa zai ɗauka su kuma su Hibba suna mamakin sharrin da take ƙullawa da kuma tsabar iya kissa.
ÆŠan jim kawai ya yi ya ce
"Bani dankalin na ledar" Miƙa masa Meenal ta yi sai ya miƙawa Husna ya ce
"Gashi nan ku juye a cikin wannan É—in ku je ku tafi gida"
Meenal ta doka uban tsallw tana masifa da kumfar bakin ya goyi bayan ƴan uwansa ta kama ledar hannun Husna ta riƙe ta ce babu wanda ya isa ya fita da dankalin daga gidan tun sa ita ba ta basu ba.
Nasir ya ce
"Wato ni da nake da ikon a kan abincin ban isa na gindaya magana ba sai kin yi jayayya ko?" Ta yi raurau da ido na kissa ta ce
"Shikenan ni bani da kima da daraja a idanunka ka saka ƙannenka za au rainani, Husna ta ɗaga hannu ta mareni amma babu wani mataki da ka ɗauka sannan har naushina ta yi fa, ai da ƴar gwal aka taɓa Sadiya da tuni kana tada jijiyoin wuya, kuma wallahi bashi suka ci indai ni ce wanda ya ci tuwo da ni miya ya sha mu zuba ni da su ɗan halak ka fasa!."
Nasir ya ce
"Mari ne kin yi an rama, to ya kuke so in yi da raina, kuma wallahi idan kika sake wani abu ya biyo baya ni da ke ne sannan ki saka mata ledar wannan su tafi"
Jin haka sai ta ƙara harzuƙa ta saki ledar tare da ɗaga hannu za ta wankawa Husna mari Husna ta yi saurin durƙushewa Meenal ta mari iska, shi kuma hakan ya yi daidia da hannunsa da ya miƙa ya cafe hannun Meenal. Baki sake take kallonsa tana tunanin wanna wace irin baƙar rana ce, lallai zama bai ganta ba dole ta tashi ta ƙwatarwa kanta ƴanci don ba za ta yarda ta zauna ba a haka a ce ana mulkarta ba wannan rayuwar ta tsarawa kanta ba. Yana riƙe da hannunta yake faɗin
"Idan kika sake kika mare ta wallahi daga yau na soke zuwansu miki girkin safe, yaran suna yi kansu da ƙafarsu amma kina raina musu" Jin ya faɗi haka ta gane zai aikata tun da ta ga take*tkensa ita kuma ta fi so a ce yanzu aka fara wasa wato idan har suka daina zuwa aiki komai zai canja domin za su tashi daga mulkarsu da takr sannan ba za ta ci gaba da samun damarmakin da yake fatan samu ba wanda za ta ambula musu ƙasa a ido su d uwarsu.
Baki ta dantse da haƙori ta ce.
"Ai abin bai kai haka ba, sannan karka manta ba fa ni kaɗai suke yi wa bautar ba har da kai sannan har da kansu da kuma mahaifiyarsu, kuma ai a ganina harshe da haƙori ma ana saɓawa a ci gaba da zama"
Bai tanka mata ba don ya matsu ya je ya ƙarawa wankansa Sadiya kuwa dama tuni ya kama gabanta, kallon su Hibba ya yi ya ce su yi tafiyarsu, sai dai Meenal ta ci alwashin rama abin da aka mata.
Ko da suka tafi a hanya suna ta maganar abin da ya faru, suna zuwa gida suka rattabawa Hajiya abin da ya faru tsabar haushi da takaici ta yi ta tsinewa Meenal har da uwarta ma. Sai dai da ta ji cewa Husna ta wanka wa Meenal mari sai ta ji da dama dama wai kibiya a ido amma dai tabbas ta lura yarinya ƙarama tana juya su, sannan ko da su
Hbbar suka ba ta labarin cewa Nasir ya shiga É—akin Sadiya har ma yana mata faran faran sai ta nuna jin haushi har da cewa a yi dai mu gani in tusa tana hura wuta!.
Meenal sai da ƙawarta ta zo gidanta washe gari sanann ta ari wayarta ta saka ta kira alajin ta da ya mata alƙwarin kuɗi don haka sai ta masa ƙorafin abin da ɓarayi suka yi na ƙwace kuɗi da kuma wayarsu. Ko da ya ji hakan sai ya ce idan zai yiwu ta zo su haɗu yau a hotel ta karɓi sabuwar waya dadal a kwali. Don haka tare suka fita da ƙawarta Safiyya ganin Nasir ba ya nan ya tafi kasuwa, sai da ta gama sheƙe ayarta ta dawo gidan amma kafin ma lokacin dawowarsa ya yi ta dawo, tana dawowa ta saka sabuwar wayarta a caji da sim ɗinta wani da take da shi a ajiye kafin ta yi welcome back na wancan.
Rashin ishashan kuɗi ya hana ta zuwa su koma wajen boka, ita da Momi sai dai hatta wayar ta faɗawa Nasir Momi ce ta siya mata don ba ta bari ya san ma an mata satar waya ba. Ganin yanzu adalci yana neman wanzuwa a gidan hakan ya sa ta ci alwashin tarwatsa duk wani abu da yake alaƙa da farincikin Sadiya a cikin gidan, don yanzu babu laifi suna samun kulawa ita da Kalifa saɓanin baya da ake nuna musu watiyar launin fata.
Ƙaryar da Meenal ta tsiro shi ne ta ringa zazzaɓin ƙarya ta amai, ko da ya ce ta je asibiti ta ce ba ta son zuwa Safiyya ta kawo mata tsinkena gwajin ciki da ake yi da fitsari wato PT wanda wata ƙawarsu ta auna tana da ciki domin kuwa ya nuna layi biyu ɓaro -ɓato. Shi ta yaudari Nasir da shi ta faɗa masa tana da ciki, abin mamaki sai ya ɗora rai a kan cikin yake ba ta kulawa tun da yanzu yana ƙoƙarin daidaita adalci. Meenal ta ci alwashin sai ta nunawa Sadiya ita ba kowa ba ce a wajen Nasir kamar yadda take a baya.
Babban abin da Meenal da Safiyya suka shirya shi ne daƙile duk wata soyayya da kulawa da Sadiyar take samu ba ta kowacce hanya ba sai ta hanya guda ɗaya wacce suke ganin idan har abin da suka shirya ya tafi daidai to tabbas Sadiya za ta tsinci talatar ta a laraba!.
Yau ya kama asabar a yau ne suka gama shirin aiwatar da komai hakan ya sa Meenal sanya idanu a dukkan motsin Sadiya domin kawo ƙarshen zamanta a gidan, sannan yau ya kasance ranar girkin Sadiyar. Yau ko da ya fita da wuri ya dawo saboda sun shirya za su je duba baban wani abokinsu hakan ya sa ya yi wa Sadiya sallama ya tafi. Sadiya tana zaune a ɗakinta sai ta tashi ta shiga banɗaki ta bar Kalifa a ɗakin yana bacci. A lokacin ne kuma Nasir ya kira Meenal yana tambayerta ya jiki sannan ta faɗa masa tana son ya taho mata da jan apple. Sadiya tana fitowa daga banɗaki ta shige ɗaki ita kuma Safiyya ƙawar Meenal tana can ƙofar gidan Sadiyar ta maƙale a jikin wata katanga, sai kuma Nasir wanda yake dab da ƙarasowa gidan.
Sadiya a bakin gado ta zauna, zamanta ke da wuya kenan tana ɗan hakin tafiyar da ta yi sai kawai ta ji Meenal ta ƙwala wani gigitaccen ƙara, Sadiya gabanta ne ya yanke ya faɗi domin abin da ya fara zuwa zuciyarta shi ne ko dai mciji ne ya sari Meenal ɗin ko dai wani abu mai kama da haka domin ƙara ya yi kama da na mai neman ɗauki da gaggawa. Gabanta ne ya faɗi ta taso tana ɗan tura cikinta, sai kuwa ta ji ta sake ƙaran a karo na biyu, sai kuma kiran sunan Sadiyar ya biyo bayan ƙaran da ta saki, Sadiya a kiɗime ta fito daga ɗakinta da zuciyarta ɗaya domin zuwa ta taimaka mata tun da dai ta san tun da her Meenal ta kira sunanta to tabbas tana neman taimako.
Kiran sunan Sadiya take hakan ya sa Sadiyar nufar ɗakinta a kiɗime. A ƙofar gida Safiyya da take laɓe ta hango motar Nasir ta shawo kwana da sauri ta fito daga maɓoyarta ta fara tafiya tamkar yanzu ta zo layjn take tafiya, yana ƙarasowa tana ɗaga ƙafarta za ta shiga gidansa ya fito suna gaisawa a daidai nan ne suka ji wani irin ƙara da Meenal ta saki, har rige rige suke wajen shiga gidan don ganin abin da yake faruwa.
Nasir shu takaicinsa É—aya ma da suka saka ya fito da kuma a jikinsa ko wanka bai gama ba, shi ua rasa wannan wace irin rayuwa cw kuma wace irin cakwakiya ce a ce kullum sai sun zo nan za su dafa abin da za su ci hakan ya sa ya ce
"Meenal mai ya sa kika musu ihun ɓarayi?"
Meenal duk da ta ji haushin tambayar ganjn kamar ma ita yake son É—orawa laifi sai ta É—ago masa ledar ta ce
"Dankali Hibba ta sata suka saka aljihu shi ne Allah ya toni asiri su na gani"
Hibba sai ta ji duk kunya ta kamata shi kuma sai ya ma rasa abin cewa sai Husna ta ce
"Yaya dankalin ne fa takr bamu kaɗan ba ya isarmu kullum sai dai mu yi kashi kamat wasu mararsa galihu, shi ne muka ƙara yawan dankalin da muka soya muka kwasa yadda zai ishemu" Ya ɗanyi shiru ya ce
"Kuma sai ku ɗauka bakwa cewa ta ƙara muju wanda take baku ba ya isa"
Hibba ta ce
"Ka ga fa É—an wanda take bayarwa bai fi cikin mutum É—aya ba"
Ganin dankali ransa ya ɓaci kamar wanda aka roƙa ganin yana neman yarda da maganrsu Mrenal ta ce
"Ƙarya suke munafukai ne wallahi a kicin suke tsayawa su cin iya cinsu sai su kai ɗan kaɗan gida, amma ya za a yi na zuba musu wannan" ,Gabaɗaya ma sai ya rasa maganst wa zai ɗauka su kuma su Hibba suna mamakin sharrin da take ƙullawa da kuma tsabar iya kissa.
ÆŠan jim kawai ya yi ya ce
"Bani dankalin na ledar" Miƙa masa Meenal ta yi sai ya miƙawa Husna ya ce
"Gashi nan ku juye a cikin wannan É—in ku je ku tafi gida"
Meenal ta doka uban tsallw tana masifa da kumfar bakin ya goyi bayan ƴan uwansa ta kama ledar hannun Husna ta riƙe ta ce babu wanda ya isa ya fita da dankalin daga gidan tun sa ita ba ta basu ba.
Nasir ya ce
"Wato ni da nake da ikon a kan abincin ban isa na gindaya magana ba sai kin yi jayayya ko?" Ta yi raurau da ido na kissa ta ce
"Shikenan ni bani da kima da daraja a idanunka ka saka ƙannenka za au rainani, Husna ta ɗaga hannu ta mareni amma babu wani mataki da ka ɗauka sannan har naushina ta yi fa, ai da ƴar gwal aka taɓa Sadiya da tuni kana tada jijiyoin wuya, kuma wallahi bashi suka ci indai ni ce wanda ya ci tuwo da ni miya ya sha mu zuba ni da su ɗan halak ka fasa!."
Nasir ya ce
"Mari ne kin yi an rama, to ya kuke so in yi da raina, kuma wallahi idan kika sake wani abu ya biyo baya ni da ke ne sannan ki saka mata ledar wannan su tafi"
Jin haka sai ta ƙara harzuƙa ta saki ledar tare da ɗaga hannu za ta wankawa Husna mari Husna ta yi saurin durƙushewa Meenal ta mari iska, shi kuma hakan ya yi daidia da hannunsa da ya miƙa ya cafe hannun Meenal. Baki sake take kallonsa tana tunanin wanna wace irin baƙar rana ce, lallai zama bai ganta ba dole ta tashi ta ƙwatarwa kanta ƴanci don ba za ta yarda ta zauna ba a haka a ce ana mulkarta ba wannan rayuwar ta tsarawa kanta ba. Yana riƙe da hannunta yake faɗin
"Idan kika sake kika mare ta wallahi daga yau na soke zuwansu miki girkin safe, yaran suna yi kansu da ƙafarsu amma kina raina musu" Jin ya faɗi haka ta gane zai aikata tun da ta ga take*tkensa ita kuma ta fi so a ce yanzu aka fara wasa wato idan har suka daina zuwa aiki komai zai canja domin za su tashi daga mulkarsu da takr sannan ba za ta ci gaba da samun damarmakin da yake fatan samu ba wanda za ta ambula musu ƙasa a ido su d uwarsu.
Baki ta dantse da haƙori ta ce.
"Ai abin bai kai haka ba, sannan karka manta ba fa ni kaɗai suke yi wa bautar ba har da kai sannan har da kansu da kuma mahaifiyarsu, kuma ai a ganina harshe da haƙori ma ana saɓawa a ci gaba da zama"
Bai tanka mata ba don ya matsu ya je ya ƙarawa wankansa Sadiya kuwa dama tuni ya kama gabanta, kallon su Hibba ya yi ya ce su yi tafiyarsu, sai dai Meenal ta ci alwashin rama abin da aka mata.
Ko da suka tafi a hanya suna ta maganar abin da ya faru, suna zuwa gida suka rattabawa Hajiya abin da ya faru tsabar haushi da takaici ta yi ta tsinewa Meenal har da uwarta ma. Sai dai da ta ji cewa Husna ta wanka wa Meenal mari sai ta ji da dama dama wai kibiya a ido amma dai tabbas ta lura yarinya ƙarama tana juya su, sannan ko da su
Hbbar suka ba ta labarin cewa Nasir ya shiga É—akin Sadiya har ma yana mata faran faran sai ta nuna jin haushi har da cewa a yi dai mu gani in tusa tana hura wuta!.
Meenal sai da ƙawarta ta zo gidanta washe gari sanann ta ari wayarta ta saka ta kira alajin ta da ya mata alƙwarin kuɗi don haka sai ta masa ƙorafin abin da ɓarayi suka yi na ƙwace kuɗi da kuma wayarsu. Ko da ya ji hakan sai ya ce idan zai yiwu ta zo su haɗu yau a hotel ta karɓi sabuwar waya dadal a kwali. Don haka tare suka fita da ƙawarta Safiyya ganin Nasir ba ya nan ya tafi kasuwa, sai da ta gama sheƙe ayarta ta dawo gidan amma kafin ma lokacin dawowarsa ya yi ta dawo, tana dawowa ta saka sabuwar wayarta a caji da sim ɗinta wani da take da shi a ajiye kafin ta yi welcome back na wancan.
Rashin ishashan kuɗi ya hana ta zuwa su koma wajen boka, ita da Momi sai dai hatta wayar ta faɗawa Nasir Momi ce ta siya mata don ba ta bari ya san ma an mata satar waya ba. Ganin yanzu adalci yana neman wanzuwa a gidan hakan ya sa ta ci alwashin tarwatsa duk wani abu da yake alaƙa da farincikin Sadiya a cikin gidan, don yanzu babu laifi suna samun kulawa ita da Kalifa saɓanin baya da ake nuna musu watiyar launin fata.
Ƙaryar da Meenal ta tsiro shi ne ta ringa zazzaɓin ƙarya ta amai, ko da ya ce ta je asibiti ta ce ba ta son zuwa Safiyya ta kawo mata tsinkena gwajin ciki da ake yi da fitsari wato PT wanda wata ƙawarsu ta auna tana da ciki domin kuwa ya nuna layi biyu ɓaro -ɓato. Shi ta yaudari Nasir da shi ta faɗa masa tana da ciki, abin mamaki sai ya ɗora rai a kan cikin yake ba ta kulawa tun da yanzu yana ƙoƙarin daidaita adalci. Meenal ta ci alwashin sai ta nunawa Sadiya ita ba kowa ba ce a wajen Nasir kamar yadda take a baya.
Babban abin da Meenal da Safiyya suka shirya shi ne daƙile duk wata soyayya da kulawa da Sadiyar take samu ba ta kowacce hanya ba sai ta hanya guda ɗaya wacce suke ganin idan har abin da suka shirya ya tafi daidai to tabbas Sadiya za ta tsinci talatar ta a laraba!.
Yau ya kama asabar a yau ne suka gama shirin aiwatar da komai hakan ya sa Meenal sanya idanu a dukkan motsin Sadiya domin kawo ƙarshen zamanta a gidan, sannan yau ya kasance ranar girkin Sadiyar. Yau ko da ya fita da wuri ya dawo saboda sun shirya za su je duba baban wani abokinsu hakan ya sa ya yi wa Sadiya sallama ya tafi. Sadiya tana zaune a ɗakinta sai ta tashi ta shiga banɗaki ta bar Kalifa a ɗakin yana bacci. A lokacin ne kuma Nasir ya kira Meenal yana tambayerta ya jiki sannan ta faɗa masa tana son ya taho mata da jan apple. Sadiya tana fitowa daga banɗaki ta shige ɗaki ita kuma Safiyya ƙawar Meenal tana can ƙofar gidan Sadiyar ta maƙale a jikin wata katanga, sai kuma Nasir wanda yake dab da ƙarasowa gidan.
Sadiya a bakin gado ta zauna, zamanta ke da wuya kenan tana ɗan hakin tafiyar da ta yi sai kawai ta ji Meenal ta ƙwala wani gigitaccen ƙara, Sadiya gabanta ne ya yanke ya faɗi domin abin da ya fara zuwa zuciyarta shi ne ko dai mciji ne ya sari Meenal ɗin ko dai wani abu mai kama da haka domin ƙara ya yi kama da na mai neman ɗauki da gaggawa. Gabanta ne ya faɗi ta taso tana ɗan tura cikinta, sai kuwa ta ji ta sake ƙaran a karo na biyu, sai kuma kiran sunan Sadiyar ya biyo bayan ƙaran da ta saki, Sadiya a kiɗime ta fito daga ɗakinta da zuciyarta ɗaya domin zuwa ta taimaka mata tun da dai ta san tun da her Meenal ta kira sunanta to tabbas tana neman taimako.
Kiran sunan Sadiya take hakan ya sa Sadiyar nufar ɗakinta a kiɗime. A ƙofar gida Safiyya da take laɓe ta hango motar Nasir ta shawo kwana da sauri ta fito daga maɓoyarta ta fara tafiya tamkar yanzu ta zo layjn take tafiya, yana ƙarasowa tana ɗaga ƙafarta za ta shiga gidansa ya fito suna gaisawa a daidai nan ne suka ji wani irin ƙara da Meenal ta saki, har rige rige suke wajen shiga gidan don ganin abin da yake faruwa.