Sashe 72
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayanta ta juya ta jingina a jikin ƙofar bayan ta rufe idanunta tana sauke ajiyar zuciyar tsalllake rijiya da baya, yanzu abin da ya rage sai ta bari idan ya ɗan jima da fita sai ta fito ta lallaɓa ta koma falon ƙasa.
A haka ta lallaɓo ta fito tana sauri sai da ta leƙa daga jikin ƙofar ta ga tana hango step ɗin na benen alamar Ibrahim ya fita sannan ta buɗe ƙofar a hankali ta fito kamar wanda aka jefo Jidda haka Aliya ta hango ta gashi ta riga ta fito daga ɗakin har ta rufe ƙofae babu damar ta koma hakan zai sa Jiddar ta ji ƙaran ƙofa da hanzari Aliya ta ji gefen jikin bangon da yake gefe ta laɓe, haka Jidda ta hayo tana sanye da wata doguwar riga mai tattara a hannun wacce gabaɗaya rigar kamar an halitta ta a jikinta yadda ta kama jikinta dole kowane namiji mai lafiya ya kalleta ba zai iya ɗauke idanunsa ba sannan dole sai wani abu ya ɗarsar masa a zuciya, tana riƙe da fulas ɗin tuwon don dama na miyar ne ta kai da plate da cokulan.
Addu,a take a zuciyarta kada Allah ya sa Jiddar ta waiwayo bayanta don tana juyowa za ta ganta sai dai Jidda da hankalinta yake a gaba bata waiwayo ba ta wuce tana takunta ta nutsuwa wanda gabaɗaya rigar da ta kamata duk takun da za ta yi sassan jikinta suna rausayawa. Tana tura ƙofar ta rufe ta nufi inda ya cire kayansa ya ajiye ta shiga linkewa za ta saka a kayan wanki don ita al,adarta ce kaya ko na wanki ne saj ta linkeshi.
Aliya tana shirin kama gabanta ta sauka ƙasa sai kawai ta ji ƙaran takalmi ana hayowa sama, idanu ta zaro da sauri ta lallaɓa ta tura ƙofar ɗaya ɗakin a hankali ba tare da ƙofar ta yi ƙara ba ta shige ta rufo gabaɗaya ta haɗa gumi tana leƙowa ta hango Ibrahim yana hayowa, duk ta haɗe gumi na tsurewar da ta yi,. ta ji lokacin da ya tura ƙofar ɗakin Jim kaɗan ta ji an sake buɗewa sai ta fara jin maganarsa yana cewa
"Ba jimawa zan yi ba ina ɗakko saƙon zan dawo na yi tunanin ma a mota na bar shi amma da na duba ban gani ba na san yana office"
Sai ta ji Jidda cikin wata sassanyar murya mai tafiyar da nutsuwar miji tana cewa
"Yanzu wannan tuwon da ka sa na maka haka zai yi ta jiranka" Ta faɗa ta karashe tana wani yin kamar ƙaramar yarinya ta ji lokacin da ya ce
"Kin san dai wannan tuwo dole ne ma in ce ai har É—umame zaki min da safe ko Jiddana?" Ya faÉ—a cikin sigar wasa da lallashi. Wani daÉ—i a cika ran Aliya jin yana batun cin tuwon sai kuma ta ji Jidda ta ce
"To ni dai karka daÉ—e ka ji" Ya kalle ta yana dariya ya ce
"Idan na daÉ—e tsallan kwaÉ—o za ki saka ni" Tana kumbura baki ta ce
"Kuka zan yi" Hannunsa ya saka a bakinsa yana ɗorawa a kan laɓɓansa guda biyu ya ce
"Karki yi min kuka da wannan idanun naki in ba haka ba zan rama da tsakiyar dare" Da hannu biyu ta rufe fuskarta tana jin yadda koyaushe son Ibrahim yake ƙaruwa a zuxiyarta saboda ya iya tafikar da mace ya san kalamai da ayyukan da zai yi mace ta so shi tabbas Ibrahim ya iya koyawa mace yadda za ta so shi.
Aliya duk da bata ganinsu amma tana jin yadda tattaunawar tasu take gudana haka nan kuma ranta yana ƙuna da abin da suke faɗa, sai dai ta sa duk ihu ne bayan hari, sannan saura ƙiris tarayya da alaƙarsu ta zama tarihi babu abin da ya fi faranta mata irin da ta ji ya ce sai ya ci tuwon nan har da ɗumame da safe ai kuwa ta san shikenan burinta ya cika!.
Tana jin yana mata sallama har yana cewa da dare za su je su gaishe da Mummy duk don ya farwntawa Jiddan tun da ya san tana ƙaunar Mummy ita ma Mummy tana ƙaunarta. Tana jin ƙaran saukarsa daga benen sannan ta ji lokacin da Jidda ta koma ɗakin ta rufo. Aliya tana maƙale a ɗakin a jikin ƙofa kamar wata ƙadangaruwa, sai da aka ɗan jima ta tabbatar yanzu Ibrahim ya bar falon ƙasa wato ya fita kafin ma ta gama wani tunani ta jiyo ƙaran buɗe get ɗin gidan haka ya bata tabbacin ya fita ma.
Yanzu ne take so ta shammaci Jidda ta fito ta yi saurin sauka ƙasa tun da ta tabbatar yanzu Jidda ta san bata falon thn da ta fito ta ga bata ganta ba, saboda haka dole ta tanadi hujjar da za ta kare kanta da ita duk da wannan ba matsalarta ba ce a halin yanzu matsalarta ta fi karkata ga sauka daga saman wannan kafin asirinta ya tonu. Juyawa ta yi tana kallon ɗakin da take ciki tana ƙiyastawa a ranta yanzu haka Jidda gyaran ɗaki take ta san kuwa abu ne mawuyaci ta kasa shigowa ɗakin da Aliyar take ta gyara.
A zuciyarta ta ce
"Uwar shegiyar tsaftar jaraba, dama wannan bata dace da ƴan aiki ba ni ce na fi dacewa a kawowa ƴan aiki wannan kalar ma,aikata ce ba kalar hutu ba ma,aikatan ma ƴan wanke-wanke' Ta faɗa tana jan ƙaramin tsaki.
Cikin sanɗa ta buɗe ƙofar a hankali ta mayar ta rufe ta fara lallaɓawa tana takawa a hankali sai da ta je tsakiyar benen kawai ta ji ta yi wa ƙafarta masauki a cikin lema, kafin ta tantance sai ji ta yi suuuuuu ta yi wata uwar sufer da ta ganta zaune jaɓar tana gangarawa bata yi masauki ba sai a step na ƙarashe jin ƙaran buɗe ƙofa a sama ya sa ko hutawa bata yi daga gangarowar ba ta tashi da sassarfa ta tashi jin ƙugunta ya riƙe ta miƙa hannu ta riƙe tsantsa tana takawa dakyar da sauro ta yi tsakiyar falon Saude da take haɗa kayan wanke wanke a kicin tana ganin abin da yake faruwa a idonta ta shiga dariya marar sauti har da riƙe ciki.
Aliya kuma sai ta shiga sauri-sauri gudu-gudu ta yi hanyar ɗakin da yake kusa da wanda Jidda ta shiga yin wanka, tana wani cangala ƙafa kamar kwaɗo, don tafiyar kamar tsalle haka take tana shigewa ɗakin ta rufo. Saude kuwa har lokacin tana ta dariya duk da bata san dalilin da ya kai Aliya saman ba amma kuma dai ta san ba wani abin kirki ba ne tun da babu yadda za a yi take sauri tana son guduwa alamun bata so a ganta duk da faɗuwar da ta hanga ta yi daga saman benen amma ko fatsarwa bata yi da jin ciwon ta tashi tana tafiya kamar wata sabuwar yar shayi tana tale ƙafa tana riƙe ƙugu ga wani ɗan tsalle da take tana cangala ƙafa.
Akiya tana shiga ɗaki kawai sai ta kwanta a ƙasa sa,arta ɗaya ma kafet ɗin ɗaki da yake da laushi sosai, birgima take tana ambaton wayyo a hankali ji take kamar ta yi ihu amma babu hali don gwiwar hannunta ma da ta bugu ciwo take mata. Haka ta daure ta shiga banɗaki ta wanke ƙafa sai fuskarta ta fito sai da ta ɗan ji jikin nata ya ɗan koma daidai ta buɗe ƙofar ta fito tana ƙoƙarin gyara ɗankwalin kanta. Jidda kuma tana ɗakin bayan ta ɗan ƙara ɗame gadon duk da shimfiɗar bata waji ɓaci ba. Dama cikin zannuwan gadon da Mummy ta aiko mata ranar nan ne wanda ta ce a wajen MAMAN AFRAH marubuciya ta saya domin babu abin da bata sayarwa, guda huɗu ta bata zanjuwan gadon da mai haɗe da labulaye da mai bargo sai mai filo huɗu dukka na ɗinkawa ne sai kuma wani lumtsumeme shi kuma na kamfani ne. Sun yi kyau sosai don da ta kira Mummy tana mata godiya sai ta ce za ta bata lambar MAMAN AFRAR ko za ta saya wani abu saboda kayanta suna da inganci tana siyar da labulaye zannuwan gado, takalman yara da manya, kayannyara ɗinkakku da na kamfani mayafai atamfofi lace abaya hijabai tutaren wuta, magungunan mata maganin sanyi, kayan sanyi, kayan kicin da sauransu.
Tana cikin gyarawar ne ta ji rigif alamar faɗuwar wani abu dalilin da ya sa ta fito kenan sai dai abin mamakin tun daga can saman take waige -waige har ta zo ƙasa bata ga alamar komai ba, sai dai ta ji ta taka lema da bata san ya aka yi hakan ta faru ba. Tana zuwa tsakiyar falon hakan ya yi daidai da zuwan Aliya ma sai kawai Jidda ta kalle ta ta ce
"Wai ina kika shige ne ni wallahi na ɗauka ma fita wajen kika yi ko saƙo aka kawo miki" Tambayar nan ta sake saka Saude a shakku don yanzu ta ƙara tabbayarwa Jidda bata san da zuwan Aliya sama ba, hakan ya sa ta fara hasashen dama ko sho dalilin da ya saka ta taho a gaggauce har tana faɗowa daga matakalar, don dama ita ta taho daga ƙofar da take sada ta da falon Jidda idan aka taho daga ɓangaren su na ƴan aiki lokacin sa ta yi wa falon tsinke ta hangi wulgin Aliya ta yi sama to duk tunaninta Jidda ma tana saman, sai bayan tana kicin kuma ta ga fitowar Jidda daga ɗaki ita ma ta zo ta nufi saman, don ta ji lokacin da Jidda take cewa Aliya ina ta yi kuma. Dama ita Saude tana zargin Aliya da wani abu na rashin gaskiya don yanayin da ta ganta ranar nan a kicin ma rashin gaskiya ne ɓaro ɓaro iya nazari da tunaninnta tana ganin tsantsar tsana da kuma ƙyashi a idanun Aliya da take yi wa Jidda.
A haka ta lallaɓo ta fito tana sauri sai da ta leƙa daga jikin ƙofar ta ga tana hango step ɗin na benen alamar Ibrahim ya fita sannan ta buɗe ƙofar a hankali ta fito kamar wanda aka jefo Jidda haka Aliya ta hango ta gashi ta riga ta fito daga ɗakin har ta rufe ƙofae babu damar ta koma hakan zai sa Jiddar ta ji ƙaran ƙofa da hanzari Aliya ta ji gefen jikin bangon da yake gefe ta laɓe, haka Jidda ta hayo tana sanye da wata doguwar riga mai tattara a hannun wacce gabaɗaya rigar kamar an halitta ta a jikinta yadda ta kama jikinta dole kowane namiji mai lafiya ya kalleta ba zai iya ɗauke idanunsa ba sannan dole sai wani abu ya ɗarsar masa a zuciya, tana riƙe da fulas ɗin tuwon don dama na miyar ne ta kai da plate da cokulan.
Addu,a take a zuciyarta kada Allah ya sa Jiddar ta waiwayo bayanta don tana juyowa za ta ganta sai dai Jidda da hankalinta yake a gaba bata waiwayo ba ta wuce tana takunta ta nutsuwa wanda gabaɗaya rigar da ta kamata duk takun da za ta yi sassan jikinta suna rausayawa. Tana tura ƙofar ta rufe ta nufi inda ya cire kayansa ya ajiye ta shiga linkewa za ta saka a kayan wanki don ita al,adarta ce kaya ko na wanki ne saj ta linkeshi.
Aliya tana shirin kama gabanta ta sauka ƙasa sai kawai ta ji ƙaran takalmi ana hayowa sama, idanu ta zaro da sauri ta lallaɓa ta tura ƙofar ɗaya ɗakin a hankali ba tare da ƙofar ta yi ƙara ba ta shige ta rufo gabaɗaya ta haɗa gumi tana leƙowa ta hango Ibrahim yana hayowa, duk ta haɗe gumi na tsurewar da ta yi,. ta ji lokacin da ya tura ƙofar ɗakin Jim kaɗan ta ji an sake buɗewa sai ta fara jin maganarsa yana cewa
"Ba jimawa zan yi ba ina ɗakko saƙon zan dawo na yi tunanin ma a mota na bar shi amma da na duba ban gani ba na san yana office"
Sai ta ji Jidda cikin wata sassanyar murya mai tafiyar da nutsuwar miji tana cewa
"Yanzu wannan tuwon da ka sa na maka haka zai yi ta jiranka" Ta faɗa ta karashe tana wani yin kamar ƙaramar yarinya ta ji lokacin da ya ce
"Kin san dai wannan tuwo dole ne ma in ce ai har É—umame zaki min da safe ko Jiddana?" Ya faÉ—a cikin sigar wasa da lallashi. Wani daÉ—i a cika ran Aliya jin yana batun cin tuwon sai kuma ta ji Jidda ta ce
"To ni dai karka daÉ—e ka ji" Ya kalle ta yana dariya ya ce
"Idan na daÉ—e tsallan kwaÉ—o za ki saka ni" Tana kumbura baki ta ce
"Kuka zan yi" Hannunsa ya saka a bakinsa yana ɗorawa a kan laɓɓansa guda biyu ya ce
"Karki yi min kuka da wannan idanun naki in ba haka ba zan rama da tsakiyar dare" Da hannu biyu ta rufe fuskarta tana jin yadda koyaushe son Ibrahim yake ƙaruwa a zuxiyarta saboda ya iya tafikar da mace ya san kalamai da ayyukan da zai yi mace ta so shi tabbas Ibrahim ya iya koyawa mace yadda za ta so shi.
Aliya duk da bata ganinsu amma tana jin yadda tattaunawar tasu take gudana haka nan kuma ranta yana ƙuna da abin da suke faɗa, sai dai ta sa duk ihu ne bayan hari, sannan saura ƙiris tarayya da alaƙarsu ta zama tarihi babu abin da ya fi faranta mata irin da ta ji ya ce sai ya ci tuwon nan har da ɗumame da safe ai kuwa ta san shikenan burinta ya cika!.
Tana jin yana mata sallama har yana cewa da dare za su je su gaishe da Mummy duk don ya farwntawa Jiddan tun da ya san tana ƙaunar Mummy ita ma Mummy tana ƙaunarta. Tana jin ƙaran saukarsa daga benen sannan ta ji lokacin da Jidda ta koma ɗakin ta rufo. Aliya tana maƙale a ɗakin a jikin ƙofa kamar wata ƙadangaruwa, sai da aka ɗan jima ta tabbatar yanzu Ibrahim ya bar falon ƙasa wato ya fita kafin ma ta gama wani tunani ta jiyo ƙaran buɗe get ɗin gidan haka ya bata tabbacin ya fita ma.
Yanzu ne take so ta shammaci Jidda ta fito ta yi saurin sauka ƙasa tun da ta tabbatar yanzu Jidda ta san bata falon thn da ta fito ta ga bata ganta ba, saboda haka dole ta tanadi hujjar da za ta kare kanta da ita duk da wannan ba matsalarta ba ce a halin yanzu matsalarta ta fi karkata ga sauka daga saman wannan kafin asirinta ya tonu. Juyawa ta yi tana kallon ɗakin da take ciki tana ƙiyastawa a ranta yanzu haka Jidda gyaran ɗaki take ta san kuwa abu ne mawuyaci ta kasa shigowa ɗakin da Aliyar take ta gyara.
A zuciyarta ta ce
"Uwar shegiyar tsaftar jaraba, dama wannan bata dace da ƴan aiki ba ni ce na fi dacewa a kawowa ƴan aiki wannan kalar ma,aikata ce ba kalar hutu ba ma,aikatan ma ƴan wanke-wanke' Ta faɗa tana jan ƙaramin tsaki.
Cikin sanɗa ta buɗe ƙofar a hankali ta mayar ta rufe ta fara lallaɓawa tana takawa a hankali sai da ta je tsakiyar benen kawai ta ji ta yi wa ƙafarta masauki a cikin lema, kafin ta tantance sai ji ta yi suuuuuu ta yi wata uwar sufer da ta ganta zaune jaɓar tana gangarawa bata yi masauki ba sai a step na ƙarashe jin ƙaran buɗe ƙofa a sama ya sa ko hutawa bata yi daga gangarowar ba ta tashi da sassarfa ta tashi jin ƙugunta ya riƙe ta miƙa hannu ta riƙe tsantsa tana takawa dakyar da sauro ta yi tsakiyar falon Saude da take haɗa kayan wanke wanke a kicin tana ganin abin da yake faruwa a idonta ta shiga dariya marar sauti har da riƙe ciki.
Aliya kuma sai ta shiga sauri-sauri gudu-gudu ta yi hanyar ɗakin da yake kusa da wanda Jidda ta shiga yin wanka, tana wani cangala ƙafa kamar kwaɗo, don tafiyar kamar tsalle haka take tana shigewa ɗakin ta rufo. Saude kuwa har lokacin tana ta dariya duk da bata san dalilin da ya kai Aliya saman ba amma kuma dai ta san ba wani abin kirki ba ne tun da babu yadda za a yi take sauri tana son guduwa alamun bata so a ganta duk da faɗuwar da ta hanga ta yi daga saman benen amma ko fatsarwa bata yi da jin ciwon ta tashi tana tafiya kamar wata sabuwar yar shayi tana tale ƙafa tana riƙe ƙugu ga wani ɗan tsalle da take tana cangala ƙafa.
Akiya tana shiga ɗaki kawai sai ta kwanta a ƙasa sa,arta ɗaya ma kafet ɗin ɗaki da yake da laushi sosai, birgima take tana ambaton wayyo a hankali ji take kamar ta yi ihu amma babu hali don gwiwar hannunta ma da ta bugu ciwo take mata. Haka ta daure ta shiga banɗaki ta wanke ƙafa sai fuskarta ta fito sai da ta ɗan ji jikin nata ya ɗan koma daidai ta buɗe ƙofar ta fito tana ƙoƙarin gyara ɗankwalin kanta. Jidda kuma tana ɗakin bayan ta ɗan ƙara ɗame gadon duk da shimfiɗar bata waji ɓaci ba. Dama cikin zannuwan gadon da Mummy ta aiko mata ranar nan ne wanda ta ce a wajen MAMAN AFRAH marubuciya ta saya domin babu abin da bata sayarwa, guda huɗu ta bata zanjuwan gadon da mai haɗe da labulaye da mai bargo sai mai filo huɗu dukka na ɗinkawa ne sai kuma wani lumtsumeme shi kuma na kamfani ne. Sun yi kyau sosai don da ta kira Mummy tana mata godiya sai ta ce za ta bata lambar MAMAN AFRAR ko za ta saya wani abu saboda kayanta suna da inganci tana siyar da labulaye zannuwan gado, takalman yara da manya, kayannyara ɗinkakku da na kamfani mayafai atamfofi lace abaya hijabai tutaren wuta, magungunan mata maganin sanyi, kayan sanyi, kayan kicin da sauransu.
Tana cikin gyarawar ne ta ji rigif alamar faɗuwar wani abu dalilin da ya sa ta fito kenan sai dai abin mamakin tun daga can saman take waige -waige har ta zo ƙasa bata ga alamar komai ba, sai dai ta ji ta taka lema da bata san ya aka yi hakan ta faru ba. Tana zuwa tsakiyar falon hakan ya yi daidai da zuwan Aliya ma sai kawai Jidda ta kalle ta ta ce
"Wai ina kika shige ne ni wallahi na ɗauka ma fita wajen kika yi ko saƙo aka kawo miki" Tambayar nan ta sake saka Saude a shakku don yanzu ta ƙara tabbayarwa Jidda bata san da zuwan Aliya sama ba, hakan ya sa ta fara hasashen dama ko sho dalilin da ya saka ta taho a gaggauce har tana faɗowa daga matakalar, don dama ita ta taho daga ƙofar da take sada ta da falon Jidda idan aka taho daga ɓangaren su na ƴan aiki lokacin sa ta yi wa falon tsinke ta hangi wulgin Aliya ta yi sama to duk tunaninta Jidda ma tana saman, sai bayan tana kicin kuma ta ga fitowar Jidda daga ɗaki ita ma ta zo ta nufi saman, don ta ji lokacin da Jidda take cewa Aliya ina ta yi kuma. Dama ita Saude tana zargin Aliya da wani abu na rashin gaskiya don yanayin da ta ganta ranar nan a kicin ma rashin gaskiya ne ɓaro ɓaro iya nazari da tunaninnta tana ganin tsantsar tsana da kuma ƙyashi a idanun Aliya da take yi wa Jidda.