Sashe 53
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tana zuwa falon ta sauke Kalifa ta ɗora a kan kujera ta fara shirin gyara gidan, sallamar wata yarinya da ta zo siyan manja ya sa ta fito daga ɗakin ta je ta bata ta dawo, tsintsiya ta ɗakko bayan ta kunna gawayi don yin tuwon dare. Fitowarsa daga ɗaki yana buɗaɗa ƙamshi ita shaddar ma kanta aabuwa ce dal yau ya fara sakawa hatta hula da agogon duk sabbi ne yadda kayan ya masa kyau tamkar ranar ɗaurin aure kamar abin arziƙi ya ce
"Sadiya baki tambaye ni ina mota ta ba" Murmushin ƙarfin hali ta yi ta ce
"Na ga bata waje to tunanina ko ka ba wani ne É—ani" Ta faÉ—a cikin zolaya. Washe baki ya yi ya ce
"Kamar kin sani kuwa ai Meenal ce suka karɓa aro ita da ƙawarta za a koyawa Meenal ɗin mota" Ɗan jim ta yi tana tunanin ba ya ma gudun matsala sai ta ce
"Ma sha Allah, Allah ya tsare ya sa a koya a sa'a" Da amib ya amsa yana saka takalmi ya fita a daidai lokacin kuma suka ji ƙaran tsayuwar motar ya waiwayo yana cewa
"Kin ji Æ´an halak suna dawo" Ita dai bata amsa masa ba ganin ya zama wani sauna a kan mace duk don ya ga bata nuna damuwa a kan lamuransa shi ya sa har yake faÉ—a mata komai ya zo bakinsa yana ganin ba za ta ji ciwo ba.
Yana fita ya rufo ƙofar Sadiya ta cire takalmi ta yi saɗaf-saɗaf ta je zauren ta shiga leƙawa daga wata ƙaranar tulla da take jikin ƙofar, tana ganin lokacin da suka fito daga motar wata farar budurwa wacce fuskarta har wani jaja take saboda bikicin ita ce ta fito daga mazaunin direba ita kuma Meenal ɗin daga mazaunan mai zamana banza. Suna ta dariya shi kuma ya harɗe hannu a ƙirji yana ta kallonsu, Meenal ta zunɓura baki tana magana cikin ɓaci ta ce
"Ka ga ko, ta kusa jefa maka ni a kwata" Ƙawar tana dariya ta ce
"Ka ji ni da mata za ta min sharri wai ni ce ma zan jefa ta a kwata to ita ce ta kusa jefa mu a wata ƙatuwar kwata, ɗazu ma kaɗan ta kaɗe wani tsoho" Gabaɗaya aka yi dariya, kafin ita ƙawar ta shiga baya ita kuma Meenal ta shiga gaba shi kuma ya shiga ya tada motar da yake a jiki ta bar mukullin, haka suka bar layin duk abin da suke a kan idanun Sadiya sai da suka tafi ta juyo ta dawo cikin gidan ta fara aikin gabanta.
Yau saura sati ɗaya biki Nasir duk ya mayar da hankaki kwacakwam kan lamarin bikinsa sai hidima yake daga shi har su Hajiya da ƙannensa tamkar dai wannan ne karon farko da zai taɓa aure. Duk da Hajiyar ta faɗawa Sadiya cewa su a wurinsu wannan ne auren fari da Nasir ɗin zai yi, kuma wannan ne auren da suke gani za su yi biki na kece raini, maganganu maarar sa kai da ƙafa dai Sadiya ta ji su sai dai tana toshe kunnuwanta ta yi kamar ba ta ji ba, saboda Hajiya ita tana ikirarin biki biyu za ta yi wato ɓangaren amarya da na ango abin ta tuwona maina.
Tun da aka zo aka yi jere ake ta kulle ƙofofin ɓangaren amarya, sannan duk wanda zai shigo gidan cikin nuna halin ko in kuka yake ga Sadiya hatta gogan yanzu ta rasa kansa da ƙafarsa babu wani abu da yake shiga tsakaninsu ba ya cin abincin gidan kwata-kwata sannan idan ya fita ma wani lokacin sai dare. Ita yanzu ko ya zo ma baya yake juya mata a kan gadon, domin ta lura gabaɗaya zumuɗin son kasancewa da sabuwar amarya yake ɗibansa, komai ya mayar da shi ga amarya, ana saura kwana biyu ɗaurin aure ya haɗa kayayyakinsa ya kwashe rabi da kwata ya kai ɗakin amarya, duk wasu abubuwa na amfaninsa to ya mayar ɗakin amarya, tamkar dai cewa aka yi ita Sadiyar ba matarsa ba ce duk da ayyukansa ya nuna cewa da alamar hakan amma dai ita ta bashi lokaci.
Ko naira biyar bai bata ba a matsayinta na uwar gida bare ta saka ran wani kayan da ake yi wa uwar gidan duk da malamai suna ganin hakan ba wajabci ba ne sai dai sun faɗa hakan kyautatawa ce sannan kowace rai tana son a kyautata mata amma Sadiya bata samu hakan ba. Ita ma ganin da kuɗinta hakan bai wani dame ta ba, tun gabatowar bikin a littafin maman afrah ruɓaɓɓiyar igiya ta ɗauki lambarta ta kira ta ta faɗa mata tana son atamfofi lokacin ana saura kwana biyar biki ne. Nana maman afrah ta ce ta mata magana ta whatsapp ta tura mata atamfa da les da takalmi da jaka, sai kayan Kalifa kala biyu ta bata acc no ta saka kuɗi sai ga mai napep ya kira ta a waya ya ta faɗa masa unguwar ya kawo mata, sun yi kyau sosai kamar yadda ta gansu a hoto haka suke shi ne ta bayar aka mata ɗinki. Sai aka mata buɗaɗɗe kasancewar tsufan da cikinta ya yi.
Ko bayan ya kwashe kayansa daga É—akin tana gyara masa drowersa ta ga ya ajiye wasu magunguna na maza hakan ya sa ta gane tanadin amarya ne murmushi ta yi abinta tana musu fatan wanyewa lafiya.
A ɓangaren amarya Meenal kuwa ta saya magungunan mata ciki kuwa har da wani na matsi mai suna gamgam wanda take fatan ma dawo mata da budurcinta ba tare da angon nata ya farga cewar ta yi fatali da mutuncin da ake fata da burin kowace mace ta kai gidan miji.
Yau za a kawo amarya bayan an yi gagarumin bikin kece raini kamar yadda Hajiya ta buƙata, Sadiya ma ta yi ɗan taro na maƙota da ƙwayenta, ta saka atamfarta poplin da ta ɗinka da yake ɗinkin doguwar riga ne sai ya mata cif abinta. Dirin tsayuwar motoci a ƙofar gidan ya ankarar da kowa ƙarasowar amarya, kasancewar akwai nepa, ife-ifen yara da guɗar manya ita ce ta karaɗe unguwar, sai yi suke suna maimaitawa Sadiya da ta fara jin faɗuwar gaba ta shiga ambaton hasbunallahu wa ni'imal wakil, ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagisu aslihli sha,ani kullahu wala takilni ila nafsi ɗarfata ain.
Haka suka shigo kamar da gayya suna ƙara guɗa, su kuma maƙoa suka shiga musu sannu da zuwa amma sai suke yi wa Sadiya da mutanenta kallon ƙasƙanci. Babu wansa ya ƙara tanka musu, suka nufi sashen amarya. Bayan kowa ya watse an yi wa Sadiya sallama tare da bata haƙuri hatta wasu saga cikin ƙannenta ma sun zo.
Zaune take a falo da kankana a gabanta wacce ta ɗakko daga frige lokacin Kalifa ya yi bacci, tana cikin sha ta ji tsayuwar mota jim kaɗan ta ji shigowar Nasir da abokansa suna sallama, ita ce ta amsa kasancewar part ɗinta ya fi kusa da ƙofae gidan. Sai dai da suka shigo babu wanda ya nufi inda take suka yi ɓangaren amarya. Zuwa can ta ji fitowarsu tana jin tashin muryoyin ƴanmata hakan ya bata tabbacin ƙawayen amarya ne. Bayan sun fita sai kuma ta ji dawowar Nasir shi kaɗai don ta ji lokacin da ya garƙama sakata a gidan, sannan kuma da safe da ta je gyara masa drower ta ga duk ya kwashe magungunnsa, hakan ya bata tabbacin za a kwashi amarci a daren yau!.
Shiru-shiru ko zai shigo ya mata sallama, ko kuma ya kawo mata ɗan abin taɓawa da wasu mazan suke siyowa har uwar gida, duk da bata saka rai ba amma bai kai mata komai ba, sannan bai kawo amarya ya haɗa su ba, wannan ya ƙara tabbatar mata za a yi wani zama a cikin gidan. Babu zato da tsammani sai jin ƙaran rufo ƙofar falon amarya ta yi.
*Ga link nan wansa yakemson shiga adashen kayan sallah ya shiga zubi duk sati 3k idan ka gama zubi sai ka karɓi kayan da ka zaɓa, in kin san ba yi za ki yi ba karki shiga min grp*
Ko a shiga grp ko min magana ta wtsapp
MAMAN AFRAH
09025576222
[11/15, 12:55 PM] ðŸ˜: *RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 1ï¸âƒ£8ï¸âƒ£
AMARYA MEENAL
"Sadiya baki tambaye ni ina mota ta ba" Murmushin ƙarfin hali ta yi ta ce
"Na ga bata waje to tunanina ko ka ba wani ne É—ani" Ta faÉ—a cikin zolaya. Washe baki ya yi ya ce
"Kamar kin sani kuwa ai Meenal ce suka karɓa aro ita da ƙawarta za a koyawa Meenal ɗin mota" Ɗan jim ta yi tana tunanin ba ya ma gudun matsala sai ta ce
"Ma sha Allah, Allah ya tsare ya sa a koya a sa'a" Da amib ya amsa yana saka takalmi ya fita a daidai lokacin kuma suka ji ƙaran tsayuwar motar ya waiwayo yana cewa
"Kin ji Æ´an halak suna dawo" Ita dai bata amsa masa ba ganin ya zama wani sauna a kan mace duk don ya ga bata nuna damuwa a kan lamuransa shi ya sa har yake faÉ—a mata komai ya zo bakinsa yana ganin ba za ta ji ciwo ba.
Yana fita ya rufo ƙofar Sadiya ta cire takalmi ta yi saɗaf-saɗaf ta je zauren ta shiga leƙawa daga wata ƙaranar tulla da take jikin ƙofar, tana ganin lokacin da suka fito daga motar wata farar budurwa wacce fuskarta har wani jaja take saboda bikicin ita ce ta fito daga mazaunin direba ita kuma Meenal ɗin daga mazaunan mai zamana banza. Suna ta dariya shi kuma ya harɗe hannu a ƙirji yana ta kallonsu, Meenal ta zunɓura baki tana magana cikin ɓaci ta ce
"Ka ga ko, ta kusa jefa maka ni a kwata" Ƙawar tana dariya ta ce
"Ka ji ni da mata za ta min sharri wai ni ce ma zan jefa ta a kwata to ita ce ta kusa jefa mu a wata ƙatuwar kwata, ɗazu ma kaɗan ta kaɗe wani tsoho" Gabaɗaya aka yi dariya, kafin ita ƙawar ta shiga baya ita kuma Meenal ta shiga gaba shi kuma ya shiga ya tada motar da yake a jiki ta bar mukullin, haka suka bar layin duk abin da suke a kan idanun Sadiya sai da suka tafi ta juyo ta dawo cikin gidan ta fara aikin gabanta.
Yau saura sati ɗaya biki Nasir duk ya mayar da hankaki kwacakwam kan lamarin bikinsa sai hidima yake daga shi har su Hajiya da ƙannensa tamkar dai wannan ne karon farko da zai taɓa aure. Duk da Hajiyar ta faɗawa Sadiya cewa su a wurinsu wannan ne auren fari da Nasir ɗin zai yi, kuma wannan ne auren da suke gani za su yi biki na kece raini, maganganu maarar sa kai da ƙafa dai Sadiya ta ji su sai dai tana toshe kunnuwanta ta yi kamar ba ta ji ba, saboda Hajiya ita tana ikirarin biki biyu za ta yi wato ɓangaren amarya da na ango abin ta tuwona maina.
Tun da aka zo aka yi jere ake ta kulle ƙofofin ɓangaren amarya, sannan duk wanda zai shigo gidan cikin nuna halin ko in kuka yake ga Sadiya hatta gogan yanzu ta rasa kansa da ƙafarsa babu wani abu da yake shiga tsakaninsu ba ya cin abincin gidan kwata-kwata sannan idan ya fita ma wani lokacin sai dare. Ita yanzu ko ya zo ma baya yake juya mata a kan gadon, domin ta lura gabaɗaya zumuɗin son kasancewa da sabuwar amarya yake ɗibansa, komai ya mayar da shi ga amarya, ana saura kwana biyu ɗaurin aure ya haɗa kayayyakinsa ya kwashe rabi da kwata ya kai ɗakin amarya, duk wasu abubuwa na amfaninsa to ya mayar ɗakin amarya, tamkar dai cewa aka yi ita Sadiyar ba matarsa ba ce duk da ayyukansa ya nuna cewa da alamar hakan amma dai ita ta bashi lokaci.
Ko naira biyar bai bata ba a matsayinta na uwar gida bare ta saka ran wani kayan da ake yi wa uwar gidan duk da malamai suna ganin hakan ba wajabci ba ne sai dai sun faɗa hakan kyautatawa ce sannan kowace rai tana son a kyautata mata amma Sadiya bata samu hakan ba. Ita ma ganin da kuɗinta hakan bai wani dame ta ba, tun gabatowar bikin a littafin maman afrah ruɓaɓɓiyar igiya ta ɗauki lambarta ta kira ta ta faɗa mata tana son atamfofi lokacin ana saura kwana biyar biki ne. Nana maman afrah ta ce ta mata magana ta whatsapp ta tura mata atamfa da les da takalmi da jaka, sai kayan Kalifa kala biyu ta bata acc no ta saka kuɗi sai ga mai napep ya kira ta a waya ya ta faɗa masa unguwar ya kawo mata, sun yi kyau sosai kamar yadda ta gansu a hoto haka suke shi ne ta bayar aka mata ɗinki. Sai aka mata buɗaɗɗe kasancewar tsufan da cikinta ya yi.
Ko bayan ya kwashe kayansa daga É—akin tana gyara masa drowersa ta ga ya ajiye wasu magunguna na maza hakan ya sa ta gane tanadin amarya ne murmushi ta yi abinta tana musu fatan wanyewa lafiya.
A ɓangaren amarya Meenal kuwa ta saya magungunan mata ciki kuwa har da wani na matsi mai suna gamgam wanda take fatan ma dawo mata da budurcinta ba tare da angon nata ya farga cewar ta yi fatali da mutuncin da ake fata da burin kowace mace ta kai gidan miji.
Yau za a kawo amarya bayan an yi gagarumin bikin kece raini kamar yadda Hajiya ta buƙata, Sadiya ma ta yi ɗan taro na maƙota da ƙwayenta, ta saka atamfarta poplin da ta ɗinka da yake ɗinkin doguwar riga ne sai ya mata cif abinta. Dirin tsayuwar motoci a ƙofar gidan ya ankarar da kowa ƙarasowar amarya, kasancewar akwai nepa, ife-ifen yara da guɗar manya ita ce ta karaɗe unguwar, sai yi suke suna maimaitawa Sadiya da ta fara jin faɗuwar gaba ta shiga ambaton hasbunallahu wa ni'imal wakil, ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagisu aslihli sha,ani kullahu wala takilni ila nafsi ɗarfata ain.
Haka suka shigo kamar da gayya suna ƙara guɗa, su kuma maƙoa suka shiga musu sannu da zuwa amma sai suke yi wa Sadiya da mutanenta kallon ƙasƙanci. Babu wansa ya ƙara tanka musu, suka nufi sashen amarya. Bayan kowa ya watse an yi wa Sadiya sallama tare da bata haƙuri hatta wasu saga cikin ƙannenta ma sun zo.
Zaune take a falo da kankana a gabanta wacce ta ɗakko daga frige lokacin Kalifa ya yi bacci, tana cikin sha ta ji tsayuwar mota jim kaɗan ta ji shigowar Nasir da abokansa suna sallama, ita ce ta amsa kasancewar part ɗinta ya fi kusa da ƙofae gidan. Sai dai da suka shigo babu wanda ya nufi inda take suka yi ɓangaren amarya. Zuwa can ta ji fitowarsu tana jin tashin muryoyin ƴanmata hakan ya bata tabbacin ƙawayen amarya ne. Bayan sun fita sai kuma ta ji dawowar Nasir shi kaɗai don ta ji lokacin da ya garƙama sakata a gidan, sannan kuma da safe da ta je gyara masa drower ta ga duk ya kwashe magungunnsa, hakan ya bata tabbacin za a kwashi amarci a daren yau!.
Shiru-shiru ko zai shigo ya mata sallama, ko kuma ya kawo mata ɗan abin taɓawa da wasu mazan suke siyowa har uwar gida, duk da bata saka rai ba amma bai kai mata komai ba, sannan bai kawo amarya ya haɗa su ba, wannan ya ƙara tabbatar mata za a yi wani zama a cikin gidan. Babu zato da tsammani sai jin ƙaran rufo ƙofar falon amarya ta yi.
*Ga link nan wansa yakemson shiga adashen kayan sallah ya shiga zubi duk sati 3k idan ka gama zubi sai ka karɓi kayan da ka zaɓa, in kin san ba yi za ki yi ba karki shiga min grp*
Ko a shiga grp ko min magana ta wtsapp
MAMAN AFRAH
09025576222
[11/15, 12:55 PM] ðŸ˜: *RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 1ï¸âƒ£8ï¸âƒ£
AMARYA MEENAL