Sashe 80
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wane gurbi kuma Malam ai gurbi ina ga an riga an cike in dai a zuciyarka ne" Sanin halinta ya sa ya ce
"In ji wane shegen?"
Ta ce
"Ah to ka tuntuɓa dai amma na san babu gurbin zama a zuciyarka"
Tunaninsa ko ta fara sakkowa ne da vayanin nasa dama tunaninsa bai wuce ta ringa masa lafiyayyan abinci ba hakan ya sa ya ce
",Wallhi tsaf mace za ta saye zucuyata in dai ta harkar abinci ne, ai ki dafa shimkafa miya ta ji nama wallahi kin kasa kin sayar a zuciyata" Da dariya ta bushe ta ce
"To ni yanzu an ce maka neman wajen zama nake, to ai ko ni kake kawo mini abincin da naman gurbin zama zan baka w tawa zuciyar" Jin furucinta ya gane nasa furucin bai samu shiga ba hakan ya sa ya saka ƙafa ya haure kwanon miyar ta tu tsure a wajen ya shiga ƙwalawa Hafsa kira ta fito ya ce
"Ki duba idan akwai mai da yaji ki mini kwaÉ—o da tuwon nan in samu in kashe yunwar cikina wanna uwar taki bata neman albarkar gidan aure, a ce maggi mace ba za ta saya ta saka a miya ba"
Har ta juya za ta tafi ta juyo ta ce
"Kai daniya hatsi ko masara kake badawa wataran ma ka ce hatsi ya di tsada ka auna ka kai kasuwa ka siyar ka ɗauke canjin saman ka saka a aljihunka sai ka auno masarar ka kawo, mace za ta bada kuɗin surfe ta biya na niƙa sannan ta saya kayan miya ta maka miyar haba ai wannan macen ko banki ce ita ka gama daƙushe ta" Jin haka ya miƙe yake masifa yana faɗin ya rasa lokacin da suka fara daina tsoronsa har kowa yana da bakin mayar masa da martani!.
Bayan kwana biyu sai ya tsiro da wani abu wani daga yau ya daina basu hatsi ko masarar tuwon ma don ya ga neman ake a kassara shi tun da har yanzu ƴaƴan babu wata wacce ta fito da miji hakan ya sa ya ce iyayansu mata ne suka ɗaure musu tsantsa, don haka sai dai su suke ciyar da su amma shi dai kam ya daina bada ko ƙwayar hatsi.
Tun daga ranar ya ƙara haɓaka kayan store ɗinsa daga ya ji wani ya matsu zai sayar da hatsi haka zai je ya saye ya zo ta libga a store iyalinsa ko oho, watarana ya je yana ciniki da wani maƙocinsa daga yamma sai mutumin yake cewa ai buhun hatsi da zai sayar iyalansa zai aunawa masara sun ce sun gaji da cin tuwon hatsi, shi ya sa ya ɗakko buhu ɗaya daga ciki zai musu canji tun da shinkafa iya ta rana ce kaɗai ake yi. Buɗar bakin Baba ya ce taɓ amma kai wahalalle ne ai ni nan na gama gane idan ka biyewa iyali sai sun ga ka yi gawa don komaj naka sai ya ƙare saboda kullum sai an ce ka kawo abinci. Shi kuma yake faɗa masa cewa ai wannan nauyi ne da Allah ya ɗorawa mutum ko bai sauke ba sai Allah ya tambaye shi, amma Baba bai ji ba haka ya saya ya je a jibge shi kuma mutumin ya siyowa iyalansa buhun masarar don ya faranta musu.
A washe garin ranar da ya sayar sai Allah ya buÉ—a masa ta hanyar da bai zata ba.
Store ɗin Baba ya cika da shinkafa da hatsi dawa da masara, ko masakar tsinke babu, amma nauyin iyali an ƙi a sauke, kullum haka za suke zaune cikin yunwa ƴaƴan sai dai kowa ya je ya yi buga buga masu roƙon samari su roƙa, masu bada mutuncin su a basu kuɗi su bayar wanda kuma za su ɗauka ma ba a basu ba a wani waje sai su ɗauka don duk su saukewa kansu nauyin haƙƙin da ba nasu ba, haka matan ma wata sai ta kwanta da yunwa idan bata da kuɗi yanzu dai kowa shi yake ciyar da kansa.
Kullum da asuba sai ya je ya buɗe store ɗin kafi ya tafi masallaci, ya ga komai lafiya domin yanzu kwaɗon da yake datsewa ba ya buɗuwa da kowane mukulli sannan idan ya dawo daga masallaci ma a store ɗin zai yada zango yana kallonsu yana murmushin jin daɗi yana ganin arziƙi gashin hanci ne, sai dai ya manta da karin maganar bar ganin ka tara ka kiyayi mai nema.
Yau ya kama litinin yana zaune da azzahar yana ganin waccen ta jiƙa garin kwaki, wancan ta shigo da awara kowa da abin da yake, shi kuma yana zaune da a ce wani zai miƙo masa da karma zai yi.
Mama Habiba ce ta zo ta ce
"Mallam don Allah ka bamu hatsi a yi tuwon nan, wallahi jiya ma da yunwa na kwanta kasancewar bani da kuɗi da safe ma ban karya ba ga rana ta yi yanzu, wallahi... Kafin ta kai aya ya katse ta yana masifa yana faɗin ko ƙwayar hatsi ba zai bayar ba, tashi ta yi jikinta babu ƙwari ta kama hanyar ɗakinta, kamar daga sama kamar almara sai Baba ya fara hango hayaƙi yana fitowa daga jikin ƙofar store ɗinsa kafin ƙiftawar ido gabaɗaya store ɗin ya kama da wuta sosai gobara ta kama..
SADIYA
Har suka shige tana tsaye bakinta a sake, tana jin ana cewa maza suna juyawa uwayen gidansu baya idan suka samu wasu matan ma,ana idan suka ƙara aure duk da ba duka aka taru aka zama ɗaya ba, amma daj kam abin na Nasir ya fara wuce gona da iri, domin ta lura shi babu ruwansa ma da wani adalci in ba rashin adalci ba da rashin sanin muhimmancin matarsa uwar gidansa ta yaya za a yi a ce wai ita ce za ta ɗauke kayanta a mata kicin na langa langa saboda ita bata da ƴanci sannan bata da wani galihu a cikin gidan.
Duk da ta san idan ɓera da sata to daddawa ma da warinta, ma,ana idan har da laifin Nasir wajen mayar da ita ba komai ba a cikin gidansa to da laifin iyayanta musamman mahaifinta, da shi babu ruwansa da ƴanci ko kwanciyar hankalin ƴarsa a gidan aure shi kawai burinsa a riƙe masa ƴarsa a ɗauki ɗawainiyarta, kowane namiji kuwa ya ga babu wanda ya damu da kai hasalima iyayan so suke a ɗauke musu nauyinka dole sai yadda ka gani don wulaƙanci an saya maka shi kwando -kwando.
Abin takaicin ma shi ne mahaifiyarta duk da ta san mahaifiyarta bata isa da Baba ba amma dai ya dace a ce ita a matsayjnta na mace tana tausaya mata da sauraron halin da take ciki, ba wai ta yi watsi da damuwarta ba in ta zo za ta faɗa ta ƙi saurarenta, kuma rashin amayar da damuwar ne yake ƙara daskarar mata da damuwa a zuxuyarta, gashi saboda cikin da take ɗauke da shi ba ta son take saka damuwa a ranta sai dai shi faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi.
Kicin ɗin ta shiga Kalifa yana buye da ita ta shiga kicin ɗin, jin ƙafarta ta ƙara riƙe mata sai ta samu waje ta zauna a kan kujerar katako irin ta mata ta tsakar gida, tana zama kawai da takaici ya cika mata zuciya bata san lokacin da hawaye ya zubo mata ba,bata ankara ba sai ta ji hannun Kalifa a kumatunta tana share mata ya ce
"Momma ki daina kuka" Ya faɗa cikin muryarsa ta yara sai lokacin ta ankara da abin da take da sauri ta saka hannu ta ƙarasa goge hawayen, domin ko kaɗan bata son Kalifa yake ganin zubar hawayensa idan ya tashi da haka lokaxin da ya yi wayo zai iya fahomtar abin da ya saka ta zubar hawaye a baya. Abu na gaba idan har yaro yana ganin hawayen mahaifiyarsa koyaushe yau da gobe zai sa ya ɗauka su hawayen ba wani damuwa ba ne idan ana zubar da su, hakan zai zamana ya saba gani nan gaba ko da a ce ya girma idan zai ga hawayen mahaifiyarsa hakan ba zai zama damuwa a garesa ba wanda zai sa ya ji wani iri domin ya saba gani, idan har yara suna ganin hawayen zai zamana basa ɗaukan kukan uwa da muhimmanci, basa ɗaukan zubar hawayen mahaifiyrsu a bakin komai.
Murmushi ta yi tw ce
"Ba kuka ba ne yaji ne ya shiga idanuna" Ta faɗa tana kama hannuwansa biyu ta riƙe tana dariya, shi ma dariyar ya yi ya ce
"Yaji ne Momma?" Ta ce
"Eh" Daga haka ta yunƙura ta tashi tsaye don sai da ta dafa ƙasa ma ta tashi. Kayanta na kicin ɗin ta shiga haɗawa domin hanyar lafiya a bi ta da shekara domin idan da ita kaɗai ce matar Nasir yanzu sun zama su biyu in har ta yi wani abu da zai yi sanadin Nasir ta kaita gida, to ta san Baba haƙuri wataƙila har sai ya durƙusa wannan kuma abin kunya ne a gareta kishiya ta san waye mahaifinta mene ne matsayinta a gidansu duk da ta san waccen kaita gidan da ya yi har sai da Nasir ɗin ya ba Meenal haƙuri.
Haka ta ringa fito da kayan Kalifa ma yana ɗakko ƙananan abubuwa har suka kwashe tass. A waje guda suka tattara lokacin Nasir ya fito daga ɗaki Meenal tana biye da shi, haka Meenal ta wuce ta gabanshi ta nufi kicin ta riƙe da plate mai ɗauke da kofuna kicin ɗin ta je ta ajiye tare da rufo kicin ɗin ta juya ta kalli Sadiya ta ce
"Ko ke fa" Tana faÉ—ar hakan ta zo ta tsaya gabansa tana masa magana cikin kwarkwasa amma Sadiya sai ta ba bango ajiyarsu kamar ma bata san da zaman su a wajen ba.
"In ji wane shegen?"
Ta ce
"Ah to ka tuntuɓa dai amma na san babu gurbin zama a zuciyarka"
Tunaninsa ko ta fara sakkowa ne da vayanin nasa dama tunaninsa bai wuce ta ringa masa lafiyayyan abinci ba hakan ya sa ya ce
",Wallhi tsaf mace za ta saye zucuyata in dai ta harkar abinci ne, ai ki dafa shimkafa miya ta ji nama wallahi kin kasa kin sayar a zuciyata" Da dariya ta bushe ta ce
"To ni yanzu an ce maka neman wajen zama nake, to ai ko ni kake kawo mini abincin da naman gurbin zama zan baka w tawa zuciyar" Jin furucinta ya gane nasa furucin bai samu shiga ba hakan ya sa ya saka ƙafa ya haure kwanon miyar ta tu tsure a wajen ya shiga ƙwalawa Hafsa kira ta fito ya ce
"Ki duba idan akwai mai da yaji ki mini kwaÉ—o da tuwon nan in samu in kashe yunwar cikina wanna uwar taki bata neman albarkar gidan aure, a ce maggi mace ba za ta saya ta saka a miya ba"
Har ta juya za ta tafi ta juyo ta ce
"Kai daniya hatsi ko masara kake badawa wataran ma ka ce hatsi ya di tsada ka auna ka kai kasuwa ka siyar ka ɗauke canjin saman ka saka a aljihunka sai ka auno masarar ka kawo, mace za ta bada kuɗin surfe ta biya na niƙa sannan ta saya kayan miya ta maka miyar haba ai wannan macen ko banki ce ita ka gama daƙushe ta" Jin haka ya miƙe yake masifa yana faɗin ya rasa lokacin da suka fara daina tsoronsa har kowa yana da bakin mayar masa da martani!.
Bayan kwana biyu sai ya tsiro da wani abu wani daga yau ya daina basu hatsi ko masarar tuwon ma don ya ga neman ake a kassara shi tun da har yanzu ƴaƴan babu wata wacce ta fito da miji hakan ya sa ya ce iyayansu mata ne suka ɗaure musu tsantsa, don haka sai dai su suke ciyar da su amma shi dai kam ya daina bada ko ƙwayar hatsi.
Tun daga ranar ya ƙara haɓaka kayan store ɗinsa daga ya ji wani ya matsu zai sayar da hatsi haka zai je ya saye ya zo ta libga a store iyalinsa ko oho, watarana ya je yana ciniki da wani maƙocinsa daga yamma sai mutumin yake cewa ai buhun hatsi da zai sayar iyalansa zai aunawa masara sun ce sun gaji da cin tuwon hatsi, shi ya sa ya ɗakko buhu ɗaya daga ciki zai musu canji tun da shinkafa iya ta rana ce kaɗai ake yi. Buɗar bakin Baba ya ce taɓ amma kai wahalalle ne ai ni nan na gama gane idan ka biyewa iyali sai sun ga ka yi gawa don komaj naka sai ya ƙare saboda kullum sai an ce ka kawo abinci. Shi kuma yake faɗa masa cewa ai wannan nauyi ne da Allah ya ɗorawa mutum ko bai sauke ba sai Allah ya tambaye shi, amma Baba bai ji ba haka ya saya ya je a jibge shi kuma mutumin ya siyowa iyalansa buhun masarar don ya faranta musu.
A washe garin ranar da ya sayar sai Allah ya buÉ—a masa ta hanyar da bai zata ba.
Store ɗin Baba ya cika da shinkafa da hatsi dawa da masara, ko masakar tsinke babu, amma nauyin iyali an ƙi a sauke, kullum haka za suke zaune cikin yunwa ƴaƴan sai dai kowa ya je ya yi buga buga masu roƙon samari su roƙa, masu bada mutuncin su a basu kuɗi su bayar wanda kuma za su ɗauka ma ba a basu ba a wani waje sai su ɗauka don duk su saukewa kansu nauyin haƙƙin da ba nasu ba, haka matan ma wata sai ta kwanta da yunwa idan bata da kuɗi yanzu dai kowa shi yake ciyar da kansa.
Kullum da asuba sai ya je ya buɗe store ɗin kafi ya tafi masallaci, ya ga komai lafiya domin yanzu kwaɗon da yake datsewa ba ya buɗuwa da kowane mukulli sannan idan ya dawo daga masallaci ma a store ɗin zai yada zango yana kallonsu yana murmushin jin daɗi yana ganin arziƙi gashin hanci ne, sai dai ya manta da karin maganar bar ganin ka tara ka kiyayi mai nema.
Yau ya kama litinin yana zaune da azzahar yana ganin waccen ta jiƙa garin kwaki, wancan ta shigo da awara kowa da abin da yake, shi kuma yana zaune da a ce wani zai miƙo masa da karma zai yi.
Mama Habiba ce ta zo ta ce
"Mallam don Allah ka bamu hatsi a yi tuwon nan, wallahi jiya ma da yunwa na kwanta kasancewar bani da kuɗi da safe ma ban karya ba ga rana ta yi yanzu, wallahi... Kafin ta kai aya ya katse ta yana masifa yana faɗin ko ƙwayar hatsi ba zai bayar ba, tashi ta yi jikinta babu ƙwari ta kama hanyar ɗakinta, kamar daga sama kamar almara sai Baba ya fara hango hayaƙi yana fitowa daga jikin ƙofar store ɗinsa kafin ƙiftawar ido gabaɗaya store ɗin ya kama da wuta sosai gobara ta kama..
SADIYA
Har suka shige tana tsaye bakinta a sake, tana jin ana cewa maza suna juyawa uwayen gidansu baya idan suka samu wasu matan ma,ana idan suka ƙara aure duk da ba duka aka taru aka zama ɗaya ba, amma daj kam abin na Nasir ya fara wuce gona da iri, domin ta lura shi babu ruwansa ma da wani adalci in ba rashin adalci ba da rashin sanin muhimmancin matarsa uwar gidansa ta yaya za a yi a ce wai ita ce za ta ɗauke kayanta a mata kicin na langa langa saboda ita bata da ƴanci sannan bata da wani galihu a cikin gidan.
Duk da ta san idan ɓera da sata to daddawa ma da warinta, ma,ana idan har da laifin Nasir wajen mayar da ita ba komai ba a cikin gidansa to da laifin iyayanta musamman mahaifinta, da shi babu ruwansa da ƴanci ko kwanciyar hankalin ƴarsa a gidan aure shi kawai burinsa a riƙe masa ƴarsa a ɗauki ɗawainiyarta, kowane namiji kuwa ya ga babu wanda ya damu da kai hasalima iyayan so suke a ɗauke musu nauyinka dole sai yadda ka gani don wulaƙanci an saya maka shi kwando -kwando.
Abin takaicin ma shi ne mahaifiyarta duk da ta san mahaifiyarta bata isa da Baba ba amma dai ya dace a ce ita a matsayjnta na mace tana tausaya mata da sauraron halin da take ciki, ba wai ta yi watsi da damuwarta ba in ta zo za ta faɗa ta ƙi saurarenta, kuma rashin amayar da damuwar ne yake ƙara daskarar mata da damuwa a zuxuyarta, gashi saboda cikin da take ɗauke da shi ba ta son take saka damuwa a ranta sai dai shi faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi.
Kicin ɗin ta shiga Kalifa yana buye da ita ta shiga kicin ɗin, jin ƙafarta ta ƙara riƙe mata sai ta samu waje ta zauna a kan kujerar katako irin ta mata ta tsakar gida, tana zama kawai da takaici ya cika mata zuciya bata san lokacin da hawaye ya zubo mata ba,bata ankara ba sai ta ji hannun Kalifa a kumatunta tana share mata ya ce
"Momma ki daina kuka" Ya faɗa cikin muryarsa ta yara sai lokacin ta ankara da abin da take da sauri ta saka hannu ta ƙarasa goge hawayen, domin ko kaɗan bata son Kalifa yake ganin zubar hawayensa idan ya tashi da haka lokaxin da ya yi wayo zai iya fahomtar abin da ya saka ta zubar hawaye a baya. Abu na gaba idan har yaro yana ganin hawayen mahaifiyarsa koyaushe yau da gobe zai sa ya ɗauka su hawayen ba wani damuwa ba ne idan ana zubar da su, hakan zai zamana ya saba gani nan gaba ko da a ce ya girma idan zai ga hawayen mahaifiyarsa hakan ba zai zama damuwa a garesa ba wanda zai sa ya ji wani iri domin ya saba gani, idan har yara suna ganin hawayen zai zamana basa ɗaukan kukan uwa da muhimmanci, basa ɗaukan zubar hawayen mahaifiyrsu a bakin komai.
Murmushi ta yi tw ce
"Ba kuka ba ne yaji ne ya shiga idanuna" Ta faɗa tana kama hannuwansa biyu ta riƙe tana dariya, shi ma dariyar ya yi ya ce
"Yaji ne Momma?" Ta ce
"Eh" Daga haka ta yunƙura ta tashi tsaye don sai da ta dafa ƙasa ma ta tashi. Kayanta na kicin ɗin ta shiga haɗawa domin hanyar lafiya a bi ta da shekara domin idan da ita kaɗai ce matar Nasir yanzu sun zama su biyu in har ta yi wani abu da zai yi sanadin Nasir ta kaita gida, to ta san Baba haƙuri wataƙila har sai ya durƙusa wannan kuma abin kunya ne a gareta kishiya ta san waye mahaifinta mene ne matsayinta a gidansu duk da ta san waccen kaita gidan da ya yi har sai da Nasir ɗin ya ba Meenal haƙuri.
Haka ta ringa fito da kayan Kalifa ma yana ɗakko ƙananan abubuwa har suka kwashe tass. A waje guda suka tattara lokacin Nasir ya fito daga ɗaki Meenal tana biye da shi, haka Meenal ta wuce ta gabanshi ta nufi kicin ta riƙe da plate mai ɗauke da kofuna kicin ɗin ta je ta ajiye tare da rufo kicin ɗin ta juya ta kalli Sadiya ta ce
"Ko ke fa" Tana faÉ—ar hakan ta zo ta tsaya gabansa tana masa magana cikin kwarkwasa amma Sadiya sai ta ba bango ajiyarsu kamar ma bata san da zaman su a wajen ba.