Sashe 20
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wallahi yanzu ma jikinsa zafi kuma kashin fa ya sake yi kar ya ci ƙarfinsa don All... Bata ƙarasa ba ta ji ƙaran aman Kalifan dama haka yake jinyar haƙori kashi da amai ga zazzaɓi kansa zafi.
Bedroom ɗin ta nufa, tana zuwa duk ya kelaya amai haka ta ɗane kayan shimfiɗar ta goge masa bakin gabaɗaya har jikinsa ya yi sanyi alamar abin ya fara ci ƙarfinsa.
Tana fitowa falon ta ga Nasir ya kara waya a kunne, Nasir kuwa mahaifiyarsa yake kira. A can gidan su Nasir mahaifiyarsa ce Hajiya Mariya wacce suke kira da Hajiya suna zaune ita da yaranta ƙannen Nasir ɗin guda biyu Husna da Hibba karyawa suke dankalin turawa ne da wainar ƙwai sai shayi mai kauri da kuma farfesun kifi suna ci suna hira wayar Hajiya ta yi ƙara ɗagawa ta yi ta ce
"Hello Nasir" Nasir ya ce
"Hajiya ina kwana" Amsa masa ta yi tana faÉ—in ga abincinsa ya amsa mata da gashi nan zuwa sai ya ce
"Kalifa ne yake kashin haƙori da amai da zazzaɓi shi ne Sadiya ta ce za ta kai shi asibiti"
A harzuƙe Hajiya ta fara faɗa tana cewa
"Wai Nasir sau nawa zan faɗa maka cewa wasu matan munfukai ne, suna faɗar jinyar ƴaƴansu ne kawai don su tatsi kuɗin miji, wato ta ɗauka kai sokon namiji ne to ahir ɗinta wallahi wani kashin haƙori ne za a kaiwa likita to likita ya bashi mai, sau nawa zan faɗa maka laulayin haƙori ba ya jin magani, shi ne za a wahalar da kai a yaudare ka ai wallahi ɗana ya fi ƙarfin mace ta ci kuɗinsa rabu da ita naira ɗari ta isa ta biya buƙata zan bada maganin a kai mata" Sosai ya ji wani daɗi a ransa yana son yadda mahaifiyarsa take taya shi tattalin kuɗinsa, ya gama wayar lokacin ta dawo falon ya kalle ta a wani wulaƙance ya ce
"Hajiya ta ce za ta bada maganin a kawo" Sai da ta kai zuciyarta nesa sannan ta ce
"To"
Store ya je ya ɗakko shinkafa da wake daidai wanda yake bayarwa a dafa ya kawo ya bata ya juya ko sallama bai mata ba ya fice ya banko ƙofar gidan. Shiru ta yi tana ta tunanin rayuwarta a ce kai baka da wata kima ko daraja a wajen miji bare ƴan uwansa ɗanka bashi da wata daraja yanzu a ce ɗansa bashi da lafiya amma ya hana a kai shi asibiti sai mahaifiyarsa ce za ta ce masa za ta bada maganin, kwanciya ta yi a kusa da Kalifa tana ta tunani.
Zuwa can ta tashi ta fita ta fara wankin banɗaki tana cikin yi ta fara jin ƙaran wayarta, kafin ta zo har kiran ya katse wani ya shigo, tana ta tunanin ko lafiya sai ta ga sunan Babanta gabanta ne ya faɗi ta fara tunanin Allah sa alkairi ne.
Jiki sanyi ƙalau ta ɗaga wayar ta gaishe shi ya amsa tana jin muryarsa raɗau babu alamun damuwa hakan ne ya bata tabbacin babu wata damuwa ko matsala.
Baba Ya ce
"Sadiya kiranki na yi in ce ki tayani godiya wajen mijinki kai Allah sakawa Nasir da alheri" Shiru Sadiya ta yi sai dai bata bayyanawa Baba mamakinta ba ta ce
"Godiyar mai Baba?"
Baba ya ce
"Ka ji yaron arziƙi ashe ma bai faɗa miki ba, shi ya sa fa ake so in mutum zai yi alheri ya yi tsakani da Allah ba sai wani ya sani ba, shi ya sa aka ce hannun hagu kar ya san na dama ya miƙa" Sadiya ta ce
"Haka ne Baba"
Baba ya ce
"Wallahi Sadiya wayata na ji tana ta ƙara ina dubawa na ga mijinki ne bawan Allahn nan na gaishe shi" Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tsayawa Sadiya jin Baba ya ce wai shi ya gaishe shi ba ma Nasir ɗin ne ya gaishe da Baban ba.
Baba ya ci gaba da faÉ—in
"Kawai bayan ya amsa gaisuwata sai ya ce Baba ka tuwo akawun lamba, bai jira na ƙara magana ba ya yanke kiran, ni kuwa ban yi bori da sanyin jiki ba na kwashe lambobin akawun ɗina na tura masa, ina turawa na kira shi ban san lokacin da na ce ranka ya daɗe na tura ba" A take hawaye suka fara sartu a fuskarta wai Baban ne ya cewa sirikinsa ransa ya daɗe saboda kawai ya ji maganar kuɗi wannan wace irin zubar da kima ce.
Baba ya ce
"Da to ya amsa min ya kashe ana jimawa sai ka dubu ɗai-ɗari dubu na dukan dubu har dubu goma ya ce in ɗauki dubu biyar in ba tsohuwarki dubu biyar, na rinƙa masa godiya, yanzu dai na bata dubu uku ni na ɗauki bakwai shi ne na kira ki kema ki tayani gode masa, yaron arziƙi ai ke da shi sai mutuwa ce za ta raba"
Sadiya a zuciyarta ta ce
',In sha Allah ba zan mutu a gidan Nasir ba ina saka ran wataran zan fita daga wanna rayuwar marar Æ´anci rayuwa marar galihu, rayuwa marar daraja' A fili kuma ta ce
"Amma na ji daɗi Allah saka masa da alkairi kuma in ya dawo zan yi ta gode masa tare da yaba masa" Haka Baba ya mata sallama cike da jin daɗi. Tana ajiye wayar za ta juya wani kiran ya shigo, ta ɗauka Baban ne amma tana dubawa sai ta ga Mama ɗauka ta yi bayan sun gaisa ta ɗauka Mamar za ta tambaye ta yaya aka ƙare jiya da ta dawo ko dai wani abu makamancin haka, ko ma dai ta tambaye ta damuwarta kamar yadda ta je mata da ƙorafin jiya ko ba komai sai ta lallashe ta ta tausasa mata yadda za ta rage mata raɗaɗi a matsayinta na uwa amma sai ta shiga faɗa mata alkairin da Nasir ɗin ya musu tana ta msta godiya da musu fatan haɗin kawunansu, haka dai Sadiyar take bata amsa cikin ƙarfin hali daga ƙarshe suka yi sallama.
Tana kashe wayar ta koma ta zauna daɓas tana tunanin kenan dai Nasir ya ƙara ƙirƙirar wata hanyar toshe duk wata ɓaraka, ita tana gidan yana musguna mata ko kuɗin kai ɗanta asibiti bai bata ba gashi a can kuma yana bajinta wato zai wanke laifinsa ko da ta je musu da magana ba za suke amincewa ba, tun da suna masa kallon mutumin kirki wannan alama ce ta sun zaɓi farincikin ɗan wani a kan farin cikin nasu ƴar!.
*JIDDA*
Ranar da aka kawo kayan saka ranar Aliya da yamma, guɗa ƙawayen Umma suka cika gida da shi Umma tamkar za ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, saboda ganin kowacce a wajen ana kawo mata kayan saka rana sallayoyi dabino, kuɗi, wasu ma kuɗin ake kai musu amma sai gashi Aliya har da ƙaramar akwati wannan dalilin ya sa maƙota suke ta zuzuta abin har kan Mama da Aliya ya fashe. Da dare bayan an watse Aliya sai gwada takalman take tana wani bada faɗi a tsakar gida lokacin Abba baya nan yana waje tare da baƙi sai murna Aliya take tana cewa
"Umma na wuce raini a unguwa, na kere sa'a wallahi Kasim yana matuƙar sona, ya kankaro min mutunci a wajen ƙawaye irin wannan takalma kala goma atamfofi kala biyu da turaruka ina ga in aka ga lefe ai ina jin ƴan baƙin ciki sai sun zauce" Ta faɗa tana ɗaga murya.
Umma ta ce
"Aliya kin yi sa'ar miji, mijin nunawa sa'a mijin bugar ƙirji ki nuna a ko jna saboda duk namijin da aka ce miki zai iya bugun ƙirji ya faranta miki to tabbas yana da kyakkyawan buri idan ya samu maƙudan kuɗi ina ga sai kyautar miliyoyi" Suka kwashe da dariya duk abin da suke Jidda tana ji don ita tun da aka kawo kayan da aka buɗe a gaban mutane ta gani bata sake gani ba, don ko bayan mutane sun watse da ta je ta fara ɗaga takalman Umma ta ce
"Jidda kar ki ƙara ɗaga kayan nan, wato kina ɗagawa zuciyarki tana ƙuna ko? Abu ne da ba za ki taɓa samu ba, wataƙila ma mijin naki ya ƙoƙarta ko dubu talatin ne kuɗin lefen da na saka ranar har ma sadaki tabbas aurenki bashi da maraba da sadaka Jidda" Lokacin d Umma ta mata wannan furucin ta ji ciwo amma kuma tuno yadda take jin Ibrahim a ranta da zuciyarta sai take gani ko babu ko kwabo za ta aure shi ta zauna da shi tsakani da Allah, kuma za ta masa matuƙar biyayya har ƙarshen numfashinta!.
A fili kuma sai ta tashi siyam-siyam ta nufi ɗaki tana jin babu daɗi a lan abin da Ummar ta mata ko don ba ita ta haife ta ba, amma ita Jidda a zuciyarta daɗi da farinciki take na kayan da aka kawowa Aliya kuma bata jin ƙyashi ko baƙinciki kuma bata wani tunani a kan cewa tana jin tana son wani abu makamancin abin da aka kawowa Aliyar bare ma ita kamar yadda Ummar ta faɗa ta san ma hakan ne tun da a yadda take kallon Ibrahim bata taɓa zaton zai ce da aure yake son ta ba, tunaninta bai shirya auren ba duk da baka san tanadin mutum ba amma ita bata da buri a haka take son kayanta.
Abba yana wajen yake ganin matan jefi-jefi suna zuwa suna gani tare da yin Allah sanya alkairi. Abba bayan baƙin sun tafi ya jima zaune yana ta jimami da mamaki sai dai ya san ba a mamaki da jimami da lamarin ubangiji hakan ya sa ya rasa ma wa zai tunkara da wannan magana, jin wai ashe ɗan gidan Alhaji Sule ne ya zai auri Jidda, mutumin da babu inda za a ambaci sunansa a kasa gane shi babban mutum mai dukiya da ya yi shura, lallai Allah, Allah ne yana yin yadda ya so a lokacin da ya so, yana ba wanda ya so sanda ya so Wayo ko dabara ba ya ba mutum abu Allah kaɗai yake bayarwa, Allah shi yake bayarwa a gode masa ya ƙara!.
Bedroom ɗin ta nufa, tana zuwa duk ya kelaya amai haka ta ɗane kayan shimfiɗar ta goge masa bakin gabaɗaya har jikinsa ya yi sanyi alamar abin ya fara ci ƙarfinsa.
Tana fitowa falon ta ga Nasir ya kara waya a kunne, Nasir kuwa mahaifiyarsa yake kira. A can gidan su Nasir mahaifiyarsa ce Hajiya Mariya wacce suke kira da Hajiya suna zaune ita da yaranta ƙannen Nasir ɗin guda biyu Husna da Hibba karyawa suke dankalin turawa ne da wainar ƙwai sai shayi mai kauri da kuma farfesun kifi suna ci suna hira wayar Hajiya ta yi ƙara ɗagawa ta yi ta ce
"Hello Nasir" Nasir ya ce
"Hajiya ina kwana" Amsa masa ta yi tana faÉ—in ga abincinsa ya amsa mata da gashi nan zuwa sai ya ce
"Kalifa ne yake kashin haƙori da amai da zazzaɓi shi ne Sadiya ta ce za ta kai shi asibiti"
A harzuƙe Hajiya ta fara faɗa tana cewa
"Wai Nasir sau nawa zan faɗa maka cewa wasu matan munfukai ne, suna faɗar jinyar ƴaƴansu ne kawai don su tatsi kuɗin miji, wato ta ɗauka kai sokon namiji ne to ahir ɗinta wallahi wani kashin haƙori ne za a kaiwa likita to likita ya bashi mai, sau nawa zan faɗa maka laulayin haƙori ba ya jin magani, shi ne za a wahalar da kai a yaudare ka ai wallahi ɗana ya fi ƙarfin mace ta ci kuɗinsa rabu da ita naira ɗari ta isa ta biya buƙata zan bada maganin a kai mata" Sosai ya ji wani daɗi a ransa yana son yadda mahaifiyarsa take taya shi tattalin kuɗinsa, ya gama wayar lokacin ta dawo falon ya kalle ta a wani wulaƙance ya ce
"Hajiya ta ce za ta bada maganin a kawo" Sai da ta kai zuciyarta nesa sannan ta ce
"To"
Store ya je ya ɗakko shinkafa da wake daidai wanda yake bayarwa a dafa ya kawo ya bata ya juya ko sallama bai mata ba ya fice ya banko ƙofar gidan. Shiru ta yi tana ta tunanin rayuwarta a ce kai baka da wata kima ko daraja a wajen miji bare ƴan uwansa ɗanka bashi da wata daraja yanzu a ce ɗansa bashi da lafiya amma ya hana a kai shi asibiti sai mahaifiyarsa ce za ta ce masa za ta bada maganin, kwanciya ta yi a kusa da Kalifa tana ta tunani.
Zuwa can ta tashi ta fita ta fara wankin banɗaki tana cikin yi ta fara jin ƙaran wayarta, kafin ta zo har kiran ya katse wani ya shigo, tana ta tunanin ko lafiya sai ta ga sunan Babanta gabanta ne ya faɗi ta fara tunanin Allah sa alkairi ne.
Jiki sanyi ƙalau ta ɗaga wayar ta gaishe shi ya amsa tana jin muryarsa raɗau babu alamun damuwa hakan ne ya bata tabbacin babu wata damuwa ko matsala.
Baba Ya ce
"Sadiya kiranki na yi in ce ki tayani godiya wajen mijinki kai Allah sakawa Nasir da alheri" Shiru Sadiya ta yi sai dai bata bayyanawa Baba mamakinta ba ta ce
"Godiyar mai Baba?"
Baba ya ce
"Ka ji yaron arziƙi ashe ma bai faɗa miki ba, shi ya sa fa ake so in mutum zai yi alheri ya yi tsakani da Allah ba sai wani ya sani ba, shi ya sa aka ce hannun hagu kar ya san na dama ya miƙa" Sadiya ta ce
"Haka ne Baba"
Baba ya ce
"Wallahi Sadiya wayata na ji tana ta ƙara ina dubawa na ga mijinki ne bawan Allahn nan na gaishe shi" Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tsayawa Sadiya jin Baba ya ce wai shi ya gaishe shi ba ma Nasir ɗin ne ya gaishe da Baban ba.
Baba ya ci gaba da faÉ—in
"Kawai bayan ya amsa gaisuwata sai ya ce Baba ka tuwo akawun lamba, bai jira na ƙara magana ba ya yanke kiran, ni kuwa ban yi bori da sanyin jiki ba na kwashe lambobin akawun ɗina na tura masa, ina turawa na kira shi ban san lokacin da na ce ranka ya daɗe na tura ba" A take hawaye suka fara sartu a fuskarta wai Baban ne ya cewa sirikinsa ransa ya daɗe saboda kawai ya ji maganar kuɗi wannan wace irin zubar da kima ce.
Baba ya ce
"Da to ya amsa min ya kashe ana jimawa sai ka dubu ɗai-ɗari dubu na dukan dubu har dubu goma ya ce in ɗauki dubu biyar in ba tsohuwarki dubu biyar, na rinƙa masa godiya, yanzu dai na bata dubu uku ni na ɗauki bakwai shi ne na kira ki kema ki tayani gode masa, yaron arziƙi ai ke da shi sai mutuwa ce za ta raba"
Sadiya a zuciyarta ta ce
',In sha Allah ba zan mutu a gidan Nasir ba ina saka ran wataran zan fita daga wanna rayuwar marar Æ´anci rayuwa marar galihu, rayuwa marar daraja' A fili kuma ta ce
"Amma na ji daɗi Allah saka masa da alkairi kuma in ya dawo zan yi ta gode masa tare da yaba masa" Haka Baba ya mata sallama cike da jin daɗi. Tana ajiye wayar za ta juya wani kiran ya shigo, ta ɗauka Baban ne amma tana dubawa sai ta ga Mama ɗauka ta yi bayan sun gaisa ta ɗauka Mamar za ta tambaye ta yaya aka ƙare jiya da ta dawo ko dai wani abu makamancin haka, ko ma dai ta tambaye ta damuwarta kamar yadda ta je mata da ƙorafin jiya ko ba komai sai ta lallashe ta ta tausasa mata yadda za ta rage mata raɗaɗi a matsayinta na uwa amma sai ta shiga faɗa mata alkairin da Nasir ɗin ya musu tana ta msta godiya da musu fatan haɗin kawunansu, haka dai Sadiyar take bata amsa cikin ƙarfin hali daga ƙarshe suka yi sallama.
Tana kashe wayar ta koma ta zauna daɓas tana tunanin kenan dai Nasir ya ƙara ƙirƙirar wata hanyar toshe duk wata ɓaraka, ita tana gidan yana musguna mata ko kuɗin kai ɗanta asibiti bai bata ba gashi a can kuma yana bajinta wato zai wanke laifinsa ko da ta je musu da magana ba za suke amincewa ba, tun da suna masa kallon mutumin kirki wannan alama ce ta sun zaɓi farincikin ɗan wani a kan farin cikin nasu ƴar!.
*JIDDA*
Ranar da aka kawo kayan saka ranar Aliya da yamma, guɗa ƙawayen Umma suka cika gida da shi Umma tamkar za ta zuba ruwa a ƙasa ta sha, saboda ganin kowacce a wajen ana kawo mata kayan saka rana sallayoyi dabino, kuɗi, wasu ma kuɗin ake kai musu amma sai gashi Aliya har da ƙaramar akwati wannan dalilin ya sa maƙota suke ta zuzuta abin har kan Mama da Aliya ya fashe. Da dare bayan an watse Aliya sai gwada takalman take tana wani bada faɗi a tsakar gida lokacin Abba baya nan yana waje tare da baƙi sai murna Aliya take tana cewa
"Umma na wuce raini a unguwa, na kere sa'a wallahi Kasim yana matuƙar sona, ya kankaro min mutunci a wajen ƙawaye irin wannan takalma kala goma atamfofi kala biyu da turaruka ina ga in aka ga lefe ai ina jin ƴan baƙin ciki sai sun zauce" Ta faɗa tana ɗaga murya.
Umma ta ce
"Aliya kin yi sa'ar miji, mijin nunawa sa'a mijin bugar ƙirji ki nuna a ko jna saboda duk namijin da aka ce miki zai iya bugun ƙirji ya faranta miki to tabbas yana da kyakkyawan buri idan ya samu maƙudan kuɗi ina ga sai kyautar miliyoyi" Suka kwashe da dariya duk abin da suke Jidda tana ji don ita tun da aka kawo kayan da aka buɗe a gaban mutane ta gani bata sake gani ba, don ko bayan mutane sun watse da ta je ta fara ɗaga takalman Umma ta ce
"Jidda kar ki ƙara ɗaga kayan nan, wato kina ɗagawa zuciyarki tana ƙuna ko? Abu ne da ba za ki taɓa samu ba, wataƙila ma mijin naki ya ƙoƙarta ko dubu talatin ne kuɗin lefen da na saka ranar har ma sadaki tabbas aurenki bashi da maraba da sadaka Jidda" Lokacin d Umma ta mata wannan furucin ta ji ciwo amma kuma tuno yadda take jin Ibrahim a ranta da zuciyarta sai take gani ko babu ko kwabo za ta aure shi ta zauna da shi tsakani da Allah, kuma za ta masa matuƙar biyayya har ƙarshen numfashinta!.
A fili kuma sai ta tashi siyam-siyam ta nufi ɗaki tana jin babu daɗi a lan abin da Ummar ta mata ko don ba ita ta haife ta ba, amma ita Jidda a zuciyarta daɗi da farinciki take na kayan da aka kawowa Aliya kuma bata jin ƙyashi ko baƙinciki kuma bata wani tunani a kan cewa tana jin tana son wani abu makamancin abin da aka kawowa Aliyar bare ma ita kamar yadda Ummar ta faɗa ta san ma hakan ne tun da a yadda take kallon Ibrahim bata taɓa zaton zai ce da aure yake son ta ba, tunaninta bai shirya auren ba duk da baka san tanadin mutum ba amma ita bata da buri a haka take son kayanta.
Abba yana wajen yake ganin matan jefi-jefi suna zuwa suna gani tare da yin Allah sanya alkairi. Abba bayan baƙin sun tafi ya jima zaune yana ta jimami da mamaki sai dai ya san ba a mamaki da jimami da lamarin ubangiji hakan ya sa ya rasa ma wa zai tunkara da wannan magana, jin wai ashe ɗan gidan Alhaji Sule ne ya zai auri Jidda, mutumin da babu inda za a ambaci sunansa a kasa gane shi babban mutum mai dukiya da ya yi shura, lallai Allah, Allah ne yana yin yadda ya so a lokacin da ya so, yana ba wanda ya so sanda ya so Wayo ko dabara ba ya ba mutum abu Allah kaɗai yake bayarwa, Allah shi yake bayarwa a gode masa ya ƙara!.