← Book details Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 106

Sashe 46

Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Bari in jira a yi ishsha,i idan har bai dawo ba ki jira nawa hukuncin" Na'am ta yi da maganarsa bai yi wa kowa magana ba ya juya fuuu ya yi ɗakinsa. Juyawa ta yi za ta koma ɗakin Mama Habiba ganin Mama Sa'ade tana mata wata dariyar ƙeta, sai kuma ta ji Mama Talatu ta kira ta hakan ya sa ta jiya alkalar tafiyar tata zuwa ɗakin Mama Talatun. Tana zuwa ƙofar ɗakin Mamar ta juya ta shige ɗakin Sadiya ta mara mata baya, Kalifa kuma Mama Habiba ta tafi ɗakinta da shi, tana shiga Mamar bata wani damu da halin da take ciki ba ta ce

"Sadiya mai kika yi wa Nasir ya dawo da ke gida?" Sadiya ta amsa tambayar sa har ta gaji da amsawa kamar yadda ta ba Baba amsar cewa babu abin da ta masa haka ma ta ba Mama amsa. Amma Mama ta ringa bala'i tana faɗin akwai dai wata a ƙasa domin ai ruwa ba ya tsamu banza, sai dai duk rantse -rantsen da ta yi Mamar bata yard ba.

Zuwa can aka kira sallar ishsha,i ta fito ta wanke hannu ta sake wata alwalar, tana jin da za ta gifta ta gaban Mama Bilki tana mata habaici, wai sun zama ɗaya da sauran yaran gidan da ake yi wa gorin rashin samun miji Allah ya ƙara tun da yanzu ita ma ta dawo zaman zawarci. Bata ce komai ba illa iyaka ta wuce ta shige ɗakin Mama tun da dai yanzu abin ya haɗe mata biyu wato rana zafi inuwa kuma ƙuna. A tsanake ta yi sallar ta ta ringa kai kukan ta wajen ubangiji a cikin sujadarta don ta san shi kaɗai ne zai yi mata mafita ta alkairi kuma shi yake tafiyar da dukkan lamuranta. Baba tsabar damuwa da ɗorawa kai babu abin da ya ci don har da man shanu da ya siyo wanda ya ce zai ci tuwo amma tsabar rashin nutsuwa ko kallon kwanukan tuwon da aka ajiye masa bai yi ba.

Ana yin sallar ya shigo gidan, don tunaninsa ma da ya fito daga masallacin zai ga motar Nasir amma shiru maƙatau babu shi babu alamarsa. Kiran Sadiya shi ne sallamarsa, lokacin Sumy da sauran wanda basa nan duk sun dawo, kowa kunne ya kasa don ya ji mai Baban zai ce, Sadiya wacce ta amsa ta taso jiki yana rawa Sumy dama tun da ta shigo take faman yada maganar ganin Sadiya da dare don ta san dai ruwa ba ya tsami banza. Tana fitowa Baba ya ce

"Wuce mu tafi in mayar da ke É—akin ki" Cike da marairaicewa ta ce

"Baba ina jin fa zai dawo" Ta faɗa don ganin Baban bai mayar da ita domin a ganinta matsawar dai ya mayar da ita ba ƙaramin raini zai ƙara janyowa mata a wajen Nasir ba ta fi so ya dawo da kansa tun da a iya saninta bata masa komai ba, amma dai ya kamata da a saurara a ji ta bakinsa amma kamar zubar da kima ne namiji ya maido mace gida da kansa kuma a mayar da itw, sai dai shi Baban babu mai faɗa masa ya ji. Cike da hargowa ya ce

"Wane shegen ne ya ce miki zai dawo, da a ce zai dawo ai da tuni ya dawo amma har an yi ishsha babu shi babu labarinsa, dole ki koma ɗakinki shi ne mutuncina da kwanciyar hankalinki " Da to ta amsa masa ba don ranta ya so ba sai dai don babu yadda za ta yi, takalmi ta saka ita tsabar ɓacin rai ma ta manta da Kalifa da yake ɗakin Mama Habiba.

Maganar Baba ta katse mata hanzari da ya ce
"Ina Kalifan yake?" Fitowar Mama Habiba riƙe da Kalifan ne ya dakatar da Sadiya daga bashi amsa, shi ya karɓi Kalifan ya yi gaba Sadiyar tana biye da shi Mama Habiba tana bin ta da kallo cike da tausayawa. Suna fitowa ya tare wani mai napep tsayawa ya yi wani matashin saurayi ne wanda kansa yake rawa ya ƙure kiɗa sai rausaya kai yake haka suka shiga Baba ya faɗa masa inda zai kai su suka tasamma gidan Nasir.

ALIYA
Sai da ya yi da gaske wajen yaƙi da zuciyarsa ganin tsananin razanar da ya yj bata bayyana ba duk da ita Aliya ta fahimci ya tsorata, tana tunanin to da shi mene ne nufinsa da har zai yi tunanin ba za ta ga abin da yake ɗauke da shi ba, tun da dai aure ai zama ne na dindindin ba ya buƙatar ɓoye-ɓoye don duk abin da aka ɓoye watarana sai ya bayyana. Wani yawu ya haɗiye muƙut yana ɗan wayincewa ya ce

"Yau ban yi sallar asuba ba har gari ya yi haske" Ya faɗa har lokacin ba ya cikin nutsuwarsa wani kallon tsantsar tsana Aliya take binsa da shi ganin haka ya fara jan mazaunai har ya zo bakin gadon, yana zuwa ya sako ƙafafunsa ƙasa har lokacin sai jan zanin gadon yake yana rufe jikinsa tamkar dai wanda ba ya ƙaunar a ga ko da cinyarsa ne bare kuma wancan babban wuri da ya san ya adana sirrinsa a wajen wanda babu wamda ya san da hakan sai mutane ƙalilan.

Tsaye ta tashi a kan ƙafafunsa da suke barazanar gaza ɗaukar gangar jikinsa sabosa ji yake kamar ba zai iya taka su a kan ƙasa ba bare har su kai shi zuwa wani waje. Gabaɗaya ya naɗo zanin gadon ya cire shi daga kan gadon, ya shiga ɗaura zani tamkar wata mace sai da ya ɗaura ya ji wani ɗan kwanciyar hankali ya saukar masa tamkar dai yana rayawa a ransa cewa Aliya bata ga komai ba tunanin hakan ne kaɗai yake ganin zai saukar masa da nutsuwar da har zai iya fuskantar ta.

Ya É—an sassauta murya ya ce

"Ki yi haƙuri Aliya na far miki ba tare da amincewarki ba wallahi kin san ba zan iya haƙuri ba, bare har na jure a daren farkon ki a gidana matsayinki na mallakina wani abu bai shiga tsakaninmu ba pls ina roƙon ki mini wannan afuwar!". Ya faɗa yana haɗa hannunsa wajen roƙon ta. Ji take tamkar ta samu mashi ko tsinin wuƙa ta raba ransa da gamgar jikinsa, tsantsar tsanarsa ta ninku a zuciyarta, ninkuwar da bata jin akwai ranar da farashin ta zai yi ƙasa.

Bai jira cewarta ba don ya ga ta zaɓi masa kallon tuhuma da tsana a kan ta furta masa kalamin da yake son ya ji ta faɗa ko ya san inda ya dosa. Ya ƙara kalallame murya ya ce

"Mu je ki gasa jikin ki kin ji Aliyata, mu yi wankan tsarki mu yi sallah lokaci yana ƙurewa" Kamae wanda za ta fasa ɗakin saboda ƙaraji haka ya ji tashin sautin maganarta tana faɗin

"Kasim ya isheka, ka riƙe wannan daɗin bakin da kake yi kai kanka ka san ni Aliya babu wani daɗin bakinka da zai yi tasiri ba, abu na farko da zan faɗa maka shi ne na tsane ka ba na ƙaunarka ka yaudare ne zan ma iya cewa ka damfare ni" Gabansa ne ya shiga dokawa da ƙarfi ya fara tunanin wace irin baƙar rana ce, shi dai ya san bacci take lokacin da ya gabatar da sunna bare ya ce ko abin da ya yi ne bai gamshe ta ba wato bata samu abij da take buƙata daga gareshi ba kasancewarsa na namiji ba.

Cike da fargaba ya ce
"Haba Aliya kar ki manta soyayya ce ta gina alaƙa ta da ke fa...

Hannu ta É—aga masa ta hanyar dakatar da shi ta ce

"Ya isa! Na ce ya isa haka, ni ba wasan kwaikwayo nake yi ba idan wasan kwaikwayo kake so za ka iya kunna su Adam zango da Ali Nuhu idan a ɓangaren mata ne kana iya kallon Momi Gombe, ni Aliya a gaskiya nake faɗa maka magana babu wasa a ciki na tsane ka ka yaudare ne Kasim ashe kai mata-maza ne???" Da sauri ya kalle ta har zanin gadon da ya nannaɗa a jikinsa yana neman suɓucewa da sauri ya riƙe ya ce

"Aliya ban ɓoye miki hakan ba sai don na ga ba wani nakasu ba ne hakan, tabbas an haife ni da baiwar mata -maza amma kuma an yi maganin wannan larurar tun ba yanzu ba wannan wajen ma da kika gani wajen ɓangaren matantakar ne da likitoci suka yi min aiki har suka ɗinke wajen, sannan wajen ai ya zama ma bashi da wani tasiri tun da ni namiji ne can ma na fi ƙarfi ta ɓangaren maza, za ki ga ma ko breast ɗina sak na maza ne bai fito irin na mace ba, kin san shi mata -maza ana samunsu da breast su girma sak na mace sannan al'aurarsu ma waje biyu ne ɓangaren mazantaka da kuma ɓangaren matantaka sai dai kowa da ɓangaren da ya fi ƙarfi" Ganin ta zuba masa ido tana sauraron abin da yake cewa sai hakan ya bashi tabbacin tamkar dai abubuwan da yake faɗa suna shigarta hakan ya da ya ɗora da faɗin.

"Idan har aka yi wa mata -maza aiki su ma za su rayu kamar kowane mutum wanda ba mata-maza ba, sannan suna haihuwa kamar kowa daɗin daɗawa ba a gadon haihuwar mata maza, wato a ce mata maza ya haifi wanda yake mata maza" Idanu ta runtse don idan tana jin kalmar mata -maza ji takr kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu, gashi ya karɓe ɗan budurcin da take alkintawa tana jin yadda ƙasanta yake mata zafi da raɗaɗi amma sanin jinsin Kasim ya daƙushe kowane ciwo da take ji, tabbas don ya shammace ta amma da bai isa ya karɓi budurcin nan ba

Lokacin da ta runtse idanunta babu abin da take hangowa sai Jidda kwance a lallausan gado, mai kyakkyawar shimfiɗa da zanin gado mai laushi, tana kwance a lallausar fatar Ibrahim. Hakan ya sa da ta buɗe idanun sai ta ga Kasim ya zama wani baƙiƙƙirin. Idanu ta ɗaga sai ta ga ashe ma wandonsa ya shimfiɗa a kan gadon ya gabatar da sunnar a ka don tana iya hangar abubuwa masu wuyar faɗuwa a jikin wandon.
Chapter 46 · 0% Book details