Sashe 101
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Za a ita ganowa ta hanyar fingerprint (Yatsun hannu) Idan Meenal ce ta taɓa hular za a gano idan kuma hannun Sadiya ne a jiki shi ma duk za a gano, kenan ta hanyar gano hannun jikin hular ne za a bambance tun da yanzu filon da aka yi amfani duk yataunmu suna jiki"
Momi ta ce
"Ikon Allah"
Ya ci gaba da faÉ—in
" Za a iya gano cewa Meenal ce ta ajiye hular a É—akin Sadiya ta hanyoyi biyu da suka shafi DNA da binciken yatsun hannu (fingerprint)
Fingerprint Analysi idan Meenal ta taɓahular da hannunta kai tsaye, za a iya samu yatsun hannunta a jikin hular
masu bincike za su ɗauki hular, su fitar da fingerprints da ke jiki, su kwatanta da na Meenal. idan yatsunta sun bayyana, to shikenan hujja ce kai tsaye cewa ta taɓa ko ta bar hular a can.
DNA Analysis idan akwai gashin kanta a cikin hular (ko 'yan ƙwayoyin fata), za a iya fitar da DNA
Sannan a gwada da nata idan ya dace, to lallai ita ce ta bar hular wannan hanya ce mafi ƙarfi wajen tabbatar da asalin mai abu musamman idan babu fingerprints., Idan kuɓa Sadiya ce ta taɓa ma duk za a gano" Su duka sun tsorata da furucinsa sai dai Momi da ta san duniya ta lalace ana iya siyan komai da kuɗi wato tana iya sayen gaskiya da kuɗi ma amma kuma furucin da ya yi yanzu ya tarwatsa ƴaƴan hanjin su dukansu.
Yana tabbatarwa da faÉ—in
"Ba zan ba kaina wahala a kan wannan ba sai da sharaɗi wallahi wallahi kowacece aka gano ita ce da laifi sai na yanke duka igiyoyon aurena a kanta, ina nufin idan har aka yi bincike duk wacce ita ce da laifin sai na sawwaqe mata aurena, zan raba alaƙar aurena da ita saki ɗai-ɗai ha uku!"
Gaban Sadiya ya fi na kowa bugawa duk ta san tana da gaskiya, amma yanzu gaskiya ta yi ƙaranci a duniyar nan ,don tana tunanin idan har aka tauye mata haƙƙi tabbas ita ce za ta samu takardar sakin ina za ta je da wannan tsohon cikin bare ta san halin Baba.
BABA
Tun yana jiran taimakon mutanen unguwa har ya cire rai kasancewar babu wamda ya ɗakko ko naira biyar bare a ɗakko ko da ƙwayar hatsi ko shinkafa a bashi haka ya sha baƙaƙen maganganun a kan cewa duniya ta lalace yanzu mutane ba sa taimakawa, bai san cewa kowa ya san abubuwan da yake yi wa iyalinsa ba na tauyewa domin yanzu an daina kiwon dabba an koma kiwon mutum. Haka ya ci gaba da fafutukarsa ta zuwa kasuwa dama kuma yana da kuɗi kawai dai rashin wadatar zuci ne sai dai kuma tun da wannn gobara ta faru sai lamuram gidan suka sake caɓewa ba ya bada ko kwabo iyakarsa idan an tambaye shi abinci sai ya cw shi da tsautsayin gobara ya faɗawa ina ya ganshi, sai dai su bari har wata damuna ta zo idan ya yi shuka ya samu sannan zai ci gaba da basu abinci ko da kuwa iya na dare ne.
Yanzu kowa ya zage dantse yana nema da masu sana,a da kuma masu bada kansu a basu kuɗi shi dai burinsa ya aurar da su ya huta, duk da yanzu ya mayar da hankali ne ga nasa sabin auren da yake son ya yi, don ya ɗora rai a kan sai ya auri namiji. Babu wanda ya san Baba yana neman aure wata yarinya ce ya samu budurwa mai rawar kai kuma idanunta a buɗe suke tas. Tun da ya ƙyalla idanu ya ga yarinyar ya ɗora rai a kanta ba komai ya fi tafiya da shi ba irin farar fatarta da ta sha mayukan bilicin sannan uwa uba kaf gidansu maza ne ita kaɗai ce mace, wannan ya sa yake ganin zai samu irin haihiwa tun da an ce ana gadon haihuwa, sannan ko mahaifiyar yarinyar ma su biyu ne mata a gidansu ƴan uwan mahaifiyar tata maza har goma, sannan ita ƴar uwar mahaifiyar tata ma kaf ƴaƴanta maza ne ba ta taɓa haihuwar mace ba wannan ya sa Baba ganin kakarsa ta yanke saƙa.
Duk wani burin Baba yana kan Badariyya wacce ta gama gano lagon Baba na son haihuwar namiji sannan ta gane tsantsar jahilcinsa da rashin godiyar Allah na ƴaƴa matan da ya bashi. Gabaɗaya sai take masa wayo da kuma kawo masa buƙatu shikenan duk da son kuɗin Baba amma haka yake kashe mata kuɗi musamman da yake ganin samari suna zuwa wajenta don ya ɗauke mata hankali daga kansu. Bai san cewa su samarin nata ƴan rage dare ba ne babu wani na aure sai an ce su fito sai a neme su a rasa yanzu shi kaɗai ne wanda take jalabtawa don shi ne na auren. Hatta wayar hannunta Baba ne ya saya shi ya gwammace ko nawa ne ya kashe tun da dai zai samu cikar burinsa na haihuwar ɗa namiji tun da yana ganin zai auri tsatson haihuwar maza.
Jarabawarsa a kan Badariyya shi ne soyayya gabaɗya sai ya ji yana ƙaunarta kamar ma a kanta ne ya ƙara tabbatar da mene ne so duk da kasancearta yarinya. Sai ya zamana tana juya shi kamar waina a tanda saboda soyayyar da yake mata hidima tamkar dai ba Malam Bala mai mammaƙo da son abin duniya ba. Babi wanda ya san wainar da Baba yake toyawa sai da ya zamana biki saura sati biyu sannan ya tara matan nasa ya sanar da su babu wacce ta yi wani baƙinciki kowa ta ce masa Allah kawo amarya lafiya, domin dama tun da suka ga ana gini sun san a rina wai an saci zanen mahaukaciya. Ƴaƴan gidan kuwa ya tara su yana gindaya musu sharuɗɗa kasancewar Badariyya ta gama faɗa masa abubuwan da take so da wanda ba ta so, haka yake ta kumfar baki ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba.
Ranar ɗaurin aure ya sha farar shaddarsa sai sheƙi take tana baza ƙamshin turarensa, Allah ne kaɗai ya san iya farincikin da yake ciki domin yana ganin kukansa ya ƙare nan da watanni tara cif yana da ɗa namiji mallakinsa. Sadiya ko da ta ji labarin auren Baban haushi da takaici ya baibaye ra son ta san saboda haihuwar namiji ya yi auren,, ita dai da farko ma ta ji haushin sakon Mama Habiba da ya yi amma yanzu daɗi take ji don ta san Mama Habiba albarkacin haƙurin da ta yi a gidansu to tabbas Allah zai musanya mata da mafi alkairi tun da ba wani wuce aure da haihuwa ta yi ba.
Ɗakin amarya ya sha jere da dare aka kawo amarya, ko da ƴan kawo amarya suka watse Baba ya je ya bankawa gidan sakata, ya shiga ɗakin amarya ya banke ƙofa ya shiga bedroom yana washe haƙora, amarya tana ɗan jin kunya haka ya ce su yi alwala su yi sallah, bayan sun yi sallar nafila Baba ya hau cire Babbar riga ya rataye, ya kalli amarya ya ce
"To amarya Bismillah" Ta masa kallon sheƙeƙe har sai da ya sha ruwan jikinsa ta ce
"Ban gane Bismillah ba, banga kayan maƙulashe ba" Ya ɗan yi jim yana kallonta ya ce
"Wane kaya kenan?"
Ta ce
"Ina kazar amarci sa sauran kayan sanyi?" Ya dafe kai ya ce
"Kash!. Ai kwata kwata na sha,afa wallahi garin saurin in zo wajenki na manta ana kawowa amarya wani kayan maƙulashe kuma laifin su malam Lurwanu ne da ba su tuna min ba" Tsaye ta miƙe tana cewa
"Ni Badariyya aka manta kazar amarcina sai ka ce wata amaryar kyankyaso"
Baba ya ce
"Haba an Badry nah ai kaji a gidan nan sai kin ture, ki yi haƙuri mantuwa ce kuma kowa ma yana yin mantuwa yanzu dai ki mini afuwa zuwa safiya sai in rama miki" Wani kallo ta masa ta ce
"Bari ka ji Bala" Da sauri ya kalle ta ganin yau babu É—an sunan soyayyar ma ta faÉ—i sunansa gatse-gatse cike sa rashin ta ido yarinyar da ya haife ta ta ci gaba da faÉ—in
"Ni Badariyya ƴar Mama ban san babu ba koɓai da nake so ake min ko ka manta ƙanwar maza ce ni, kowa ji yake da ni saboda ni kaɗai cw macw in za ka buɗe bakin aljihu ka buɗe" Wani yawu ya haɗiye yana fatan dai kar wannan yarinya da niyyar talauta shi ta zo ga shi kuma sonta yana ɗawainiya da shi. Haka ya lallaɓa ta ya saka babbar rigar ya fita ya buɗe gidan ya fice duk mutanen gidan suna jin fitarsa. Haka ya je wajwn mai kaji aka faɗa masa kuɗaɗensu, kamar ya yi kuka haka ya duba wata ta dubu biyar kamar tattabara saboda ƴar ƙarama ce, haka aka sako masa a leda ya ratsa ta siyo mata lemon roba guda ɗaya ya tafi.
Sai da suka zauna tana ƴar dariya ganin an kawo mata kaza ƙawayenta in sun zo gobe ai babu raini ana fito da kaza sai ta ga lemo ɗaya tana mamaki ta ce
"Babban yaro ya na ga haka kuma lemo ɗaya kamar ka roƙo ko dai alakoro aka saka maka?" Ya kalle ta yana washe baki don Allah kaɗai ya san daɗin da yake ji in ta ce masa Babban yaron nan sai ya ji ya koma yaro ɗanye sharaf yake jin kansa ɗaya da samari.
Yana kallon ta ya ce
"Ai da yake ni ba sha zan yi ba cikin ki dai ke kaÉ—ai ya ishe ki"
Ta ce
"A,a wannan ai sai a ce mini marowaciya baka san ƙawaye suna zuwa su ga ƙwaƙwaf washe garin kawo amarya ba, so kake ake cewa da saurayi na aura da sai na ture lemuka kuɓa bayan na san an ce ku manyan kun fi ba macw kulawa da nuna soyayya da bautata mata" Murmushin ƙarfin hali ya yi ya ce
"In dai lemo ne da safe zan siyo miki kafin su zo" Amincewa ta yi sai da ya buɗe ledar kaza ta ga ƙaramar kaza wani salati da ta kwasa sai da ya ji tamkar mutuwa aka sanar mata, yana kallonta ya ce
"Lafiya?"
Ta ce
Momi ta ce
"Ikon Allah"
Ya ci gaba da faÉ—in
" Za a iya gano cewa Meenal ce ta ajiye hular a É—akin Sadiya ta hanyoyi biyu da suka shafi DNA da binciken yatsun hannu (fingerprint)
Fingerprint Analysi idan Meenal ta taɓahular da hannunta kai tsaye, za a iya samu yatsun hannunta a jikin hular
masu bincike za su ɗauki hular, su fitar da fingerprints da ke jiki, su kwatanta da na Meenal. idan yatsunta sun bayyana, to shikenan hujja ce kai tsaye cewa ta taɓa ko ta bar hular a can.
DNA Analysis idan akwai gashin kanta a cikin hular (ko 'yan ƙwayoyin fata), za a iya fitar da DNA
Sannan a gwada da nata idan ya dace, to lallai ita ce ta bar hular wannan hanya ce mafi ƙarfi wajen tabbatar da asalin mai abu musamman idan babu fingerprints., Idan kuɓa Sadiya ce ta taɓa ma duk za a gano" Su duka sun tsorata da furucinsa sai dai Momi da ta san duniya ta lalace ana iya siyan komai da kuɗi wato tana iya sayen gaskiya da kuɗi ma amma kuma furucin da ya yi yanzu ya tarwatsa ƴaƴan hanjin su dukansu.
Yana tabbatarwa da faÉ—in
"Ba zan ba kaina wahala a kan wannan ba sai da sharaɗi wallahi wallahi kowacece aka gano ita ce da laifi sai na yanke duka igiyoyon aurena a kanta, ina nufin idan har aka yi bincike duk wacce ita ce da laifin sai na sawwaqe mata aurena, zan raba alaƙar aurena da ita saki ɗai-ɗai ha uku!"
Gaban Sadiya ya fi na kowa bugawa duk ta san tana da gaskiya, amma yanzu gaskiya ta yi ƙaranci a duniyar nan ,don tana tunanin idan har aka tauye mata haƙƙi tabbas ita ce za ta samu takardar sakin ina za ta je da wannan tsohon cikin bare ta san halin Baba.
BABA
Tun yana jiran taimakon mutanen unguwa har ya cire rai kasancewar babu wamda ya ɗakko ko naira biyar bare a ɗakko ko da ƙwayar hatsi ko shinkafa a bashi haka ya sha baƙaƙen maganganun a kan cewa duniya ta lalace yanzu mutane ba sa taimakawa, bai san cewa kowa ya san abubuwan da yake yi wa iyalinsa ba na tauyewa domin yanzu an daina kiwon dabba an koma kiwon mutum. Haka ya ci gaba da fafutukarsa ta zuwa kasuwa dama kuma yana da kuɗi kawai dai rashin wadatar zuci ne sai dai kuma tun da wannn gobara ta faru sai lamuram gidan suka sake caɓewa ba ya bada ko kwabo iyakarsa idan an tambaye shi abinci sai ya cw shi da tsautsayin gobara ya faɗawa ina ya ganshi, sai dai su bari har wata damuna ta zo idan ya yi shuka ya samu sannan zai ci gaba da basu abinci ko da kuwa iya na dare ne.
Yanzu kowa ya zage dantse yana nema da masu sana,a da kuma masu bada kansu a basu kuɗi shi dai burinsa ya aurar da su ya huta, duk da yanzu ya mayar da hankali ne ga nasa sabin auren da yake son ya yi, don ya ɗora rai a kan sai ya auri namiji. Babu wanda ya san Baba yana neman aure wata yarinya ce ya samu budurwa mai rawar kai kuma idanunta a buɗe suke tas. Tun da ya ƙyalla idanu ya ga yarinyar ya ɗora rai a kanta ba komai ya fi tafiya da shi ba irin farar fatarta da ta sha mayukan bilicin sannan uwa uba kaf gidansu maza ne ita kaɗai ce mace, wannan ya sa yake ganin zai samu irin haihiwa tun da an ce ana gadon haihuwa, sannan ko mahaifiyar yarinyar ma su biyu ne mata a gidansu ƴan uwan mahaifiyar tata maza har goma, sannan ita ƴar uwar mahaifiyar tata ma kaf ƴaƴanta maza ne ba ta taɓa haihuwar mace ba wannan ya sa Baba ganin kakarsa ta yanke saƙa.
Duk wani burin Baba yana kan Badariyya wacce ta gama gano lagon Baba na son haihuwar namiji sannan ta gane tsantsar jahilcinsa da rashin godiyar Allah na ƴaƴa matan da ya bashi. Gabaɗaya sai take masa wayo da kuma kawo masa buƙatu shikenan duk da son kuɗin Baba amma haka yake kashe mata kuɗi musamman da yake ganin samari suna zuwa wajenta don ya ɗauke mata hankali daga kansu. Bai san cewa su samarin nata ƴan rage dare ba ne babu wani na aure sai an ce su fito sai a neme su a rasa yanzu shi kaɗai ne wanda take jalabtawa don shi ne na auren. Hatta wayar hannunta Baba ne ya saya shi ya gwammace ko nawa ne ya kashe tun da dai zai samu cikar burinsa na haihuwar ɗa namiji tun da yana ganin zai auri tsatson haihuwar maza.
Jarabawarsa a kan Badariyya shi ne soyayya gabaɗya sai ya ji yana ƙaunarta kamar ma a kanta ne ya ƙara tabbatar da mene ne so duk da kasancearta yarinya. Sai ya zamana tana juya shi kamar waina a tanda saboda soyayyar da yake mata hidima tamkar dai ba Malam Bala mai mammaƙo da son abin duniya ba. Babi wanda ya san wainar da Baba yake toyawa sai da ya zamana biki saura sati biyu sannan ya tara matan nasa ya sanar da su babu wacce ta yi wani baƙinciki kowa ta ce masa Allah kawo amarya lafiya, domin dama tun da suka ga ana gini sun san a rina wai an saci zanen mahaukaciya. Ƴaƴan gidan kuwa ya tara su yana gindaya musu sharuɗɗa kasancewar Badariyya ta gama faɗa masa abubuwan da take so da wanda ba ta so, haka yake ta kumfar baki ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba.
Ranar ɗaurin aure ya sha farar shaddarsa sai sheƙi take tana baza ƙamshin turarensa, Allah ne kaɗai ya san iya farincikin da yake ciki domin yana ganin kukansa ya ƙare nan da watanni tara cif yana da ɗa namiji mallakinsa. Sadiya ko da ta ji labarin auren Baban haushi da takaici ya baibaye ra son ta san saboda haihuwar namiji ya yi auren,, ita dai da farko ma ta ji haushin sakon Mama Habiba da ya yi amma yanzu daɗi take ji don ta san Mama Habiba albarkacin haƙurin da ta yi a gidansu to tabbas Allah zai musanya mata da mafi alkairi tun da ba wani wuce aure da haihuwa ta yi ba.
Ɗakin amarya ya sha jere da dare aka kawo amarya, ko da ƴan kawo amarya suka watse Baba ya je ya bankawa gidan sakata, ya shiga ɗakin amarya ya banke ƙofa ya shiga bedroom yana washe haƙora, amarya tana ɗan jin kunya haka ya ce su yi alwala su yi sallah, bayan sun yi sallar nafila Baba ya hau cire Babbar riga ya rataye, ya kalli amarya ya ce
"To amarya Bismillah" Ta masa kallon sheƙeƙe har sai da ya sha ruwan jikinsa ta ce
"Ban gane Bismillah ba, banga kayan maƙulashe ba" Ya ɗan yi jim yana kallonta ya ce
"Wane kaya kenan?"
Ta ce
"Ina kazar amarci sa sauran kayan sanyi?" Ya dafe kai ya ce
"Kash!. Ai kwata kwata na sha,afa wallahi garin saurin in zo wajenki na manta ana kawowa amarya wani kayan maƙulashe kuma laifin su malam Lurwanu ne da ba su tuna min ba" Tsaye ta miƙe tana cewa
"Ni Badariyya aka manta kazar amarcina sai ka ce wata amaryar kyankyaso"
Baba ya ce
"Haba an Badry nah ai kaji a gidan nan sai kin ture, ki yi haƙuri mantuwa ce kuma kowa ma yana yin mantuwa yanzu dai ki mini afuwa zuwa safiya sai in rama miki" Wani kallo ta masa ta ce
"Bari ka ji Bala" Da sauri ya kalle ta ganin yau babu É—an sunan soyayyar ma ta faÉ—i sunansa gatse-gatse cike sa rashin ta ido yarinyar da ya haife ta ta ci gaba da faÉ—in
"Ni Badariyya ƴar Mama ban san babu ba koɓai da nake so ake min ko ka manta ƙanwar maza ce ni, kowa ji yake da ni saboda ni kaɗai cw macw in za ka buɗe bakin aljihu ka buɗe" Wani yawu ya haɗiye yana fatan dai kar wannan yarinya da niyyar talauta shi ta zo ga shi kuma sonta yana ɗawainiya da shi. Haka ya lallaɓa ta ya saka babbar rigar ya fita ya buɗe gidan ya fice duk mutanen gidan suna jin fitarsa. Haka ya je wajwn mai kaji aka faɗa masa kuɗaɗensu, kamar ya yi kuka haka ya duba wata ta dubu biyar kamar tattabara saboda ƴar ƙarama ce, haka aka sako masa a leda ya ratsa ta siyo mata lemon roba guda ɗaya ya tafi.
Sai da suka zauna tana ƴar dariya ganin an kawo mata kaza ƙawayenta in sun zo gobe ai babu raini ana fito da kaza sai ta ga lemo ɗaya tana mamaki ta ce
"Babban yaro ya na ga haka kuma lemo ɗaya kamar ka roƙo ko dai alakoro aka saka maka?" Ya kalle ta yana washe baki don Allah kaɗai ya san daɗin da yake ji in ta ce masa Babban yaron nan sai ya ji ya koma yaro ɗanye sharaf yake jin kansa ɗaya da samari.
Yana kallon ta ya ce
"Ai da yake ni ba sha zan yi ba cikin ki dai ke kaÉ—ai ya ishe ki"
Ta ce
"A,a wannan ai sai a ce mini marowaciya baka san ƙawaye suna zuwa su ga ƙwaƙwaf washe garin kawo amarya ba, so kake ake cewa da saurayi na aura da sai na ture lemuka kuɓa bayan na san an ce ku manyan kun fi ba macw kulawa da nuna soyayya da bautata mata" Murmushin ƙarfin hali ya yi ya ce
"In dai lemo ne da safe zan siyo miki kafin su zo" Amincewa ta yi sai da ya buɗe ledar kaza ta ga ƙaramar kaza wani salati da ta kwasa sai da ya ji tamkar mutuwa aka sanar mata, yana kallonta ya ce
"Lafiya?"
Ta ce