Sashe 97
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wallahi ke dai bari Lubabatu na ji mutuwar bawan Allahn nan, duniya ba matabbata ba, watarana mu ma haka tamu mutuwar za ta risƙemu" Wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sauke jin babu wani batu bayan na mutuwa hakan ya sa ta zage suka ci gaba da jajantawa. Ko da dare ya yi ta zo kwanciya sai tsoro ya mamaye mata zuciya daga ta rufe ido sai take ganin kamar gawar za ta zo mata haka ta kwana idanu a buɗe don ba ta so ta rufe idanun sai take hangar gawar kamar ta zo gidan, haka ta kwana a firgice.
Da safe sa ciwon cikin ƙarya ta tashi amma tana ta nuna za ta tafi sutura Abba ya ce tun da ba ta da lafiya ta zauna, daɗi ya cika ranta don ita ba ta so ma ta je suturar gawar da ba ta da tabbacin ta mutu. Ko da Abba ya tafi suturar ya dawo haka ta ce
"Oh duniya ba tabbas har an binne shi ko, rayuwa kenan, yanzu mutum an jima gawa rayuwa kenan, duniya kenan yau kana tafiya a saman ƙasa watarana kuma kana ƙarƙashin ƙasa"
Abba ya ce
"Bari ke dai ai muna rayuwa ba mu san rana da lokacin mutuwarmu ba bare yanzu da ake yawan mutuwar nan ta bagatatan mutuwar fuju,a yanzu za ka rabu da mutum an jima ka ji an ce babu shi" Umma dai ba ta ji amsar tambayarta ba hakan ya sa ta ce
"Wallahi kuwa Allah sarki marigayi Malam Kalla su tasu ta ƙare saura tamu tun da sun shiga kabari"
Abba ya ce
"Kai ina tsoron mutuwa ranar da zan ganni ga ni ga mala,ika, ranar da za a saka ni a kabari ranar da zan ganni a cikin kabari, ya Allah ka rabamu da duhu da azabar kabari da nauyin ƙasa"
Umma ta takarkare ta ce
"Amin" Amma duk ranta ya ɓaci ita so take ya ce an binne shi don tana tsoron ya faɗi abin da ya faru tun da tana ganin bai mutu ba. Har ta yi shiru sai ta ce
"Ko ba a yi suturar ba ne"
Abba ya ce
"Haba ke kuwa sutura ta nawa kuma tuni ma da an dawo mai zai dawo da ni gida in ba a kai shi makwancinsa ba, dama dawowa na yi idan na karya sai na koma idan na ɗan jima wajen karɓar makokin sai na dawo na shirya na tafi kasuwa"
Umma ta ce
"Haka ne" Ta faɗa tana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya.
Aliya kuwa tun da ta ji bayanin da Umma ta mata ta gane cewa Abba ne ya dawo, Umma tana datse kiran wayar ta ajiye kawai take kuka wiwi don rashin cikar burinta kuma tana tunanin yadda za a samu wani kuÉ—in aikin.
Ko da Kasim ya dawo sai da ya fahimci ta sauya amma sai ta nuna masa kanta ne yake ciwo shi kansa haushinsa take ji ta gaji da sakar masa fuskar da take ta gaji da nuna masa tana zaune da shi ne da zuciya ɗaya, bai san cewa da wata manufa take zaune ba burinta yana cika zaman gidansa ya ƙara don ta fi ƙardin zaman aure da talaka, talakan ma mata -maza. Ko wayar ta da ya gani sabuwar ta nuna masa Jidda ce ta saya mata duk da ta fahimci bai ji daɗi ba amma haka ta make abinta tun da ta san shi dai koyaushe cikin fafutukar na abin da za a rufawa kai asiri yake ita ba ta taɓa hango masa zai taka matakin masu arziƙi ba duk da an ce arziƙi kashi ne amma ita ba ta hango arziƙi a tare da wannan mata mazan ba gani take a haka zai ƙare ita kuma ta fi ƙarfin zama da shi yadda take kyakkawa ajin farko da gidan daula ta dace, gidan daular ma ba kowane iri ba.
Bayan nan suka ringa waya da Umma saboda tana tsoron ta je gidan su haɗu da Abba saboda ba ua son yawan zuwa gida babu dalili, shi yawo ba ya yi wa mace kyau a wajensa a ce yau tana can gobe tana can ko da budurwa ce kuwa bare matar aure, ya tsani fita babu dalili. Haka dai suka shirya suka je wajen bokanya don sanar da ita abin da ya faru. Ko da suka je bokanya ta ɗauka za su faɗi kyakkyawan labari amma sai ta ji saɓanin haka, mamaki ya kamata hakan ya sa ta yi wani surkulle ta ɗakko wani ganye tana karkaɗawa tana ambaton wani suna, zuwa can sai suka ji magana ta karaɗe ɗakin ana cewa
"Ya ke bokanya mai kike buƙata a aiwatar miki?" Bokanya ta ce
"Ina so sanin dalilin da ya sa gawar da za a sakawa maganin da na bayar ta motsa har ta riƙe wacce za ta yi aikin"
Mai maganar bisa muryar tsoro ya sheƙe da wata dariyar da har sai da su Umma suka razana sai da dariyar ta lafa ya ce
"Akwai wani abokin aikin ki boka Naladidi wanda sa,insa ta shiga tsakaninku a watan da ya wuce har ya ci alwashin sai ya ɓata miji duk wani aiki to shi ne yake kan bakansa, shi ne ya yi komai" Cike da rashin fahimta ta ce
"Mai ya yi"
Muryar ta ci gaba da cewa
"Ya aika aljani ɗan ƙundalo ya je ya ture Daddyn Ibrahim ɗin da kika yi wa asiri a cokali, shi ne aka kira Ibrahim ɗin aka sanar da shi a lokacin da zai ci abinci wannan dalilin ya sa bai ci abincin da cokalin ba bare har aikin ya ci, sannan shi ya aika aljani gidan gawar Malam Kalla, aljanin ya ɗauke gawar mamacin ya kwanta a wajen da aka ajiye mamacin bayan ya sauya kamanni irin na mamacin ai ba gawar ba ce aka yi ƙoƙarin sakawa maganin ba aljanin ne, da shi suka yi kokawar har sai da ya ga komai bai yi ba a aikin sannan ya koma ya sanar da bokan cewa ya cika aiki hakan ya sa ya ƙara cin alwashin duk aikin da za ki yi sai ya san yadda ya yi ya ɓata aikin bai yiwu ba" Tun da ya fara bayani jikin Umma yake karkarwa musamman idan ta tuna cewa wai da aljani ta yi fafutuka jiya ashe aljani ne ta ja hat zaure duk sai ta ji tsoro ya baibaye ta a ganinta har gwara gawa mutum ce a kan aljani. A neman duniya za ta je ta yi abin da aljannun ma za su ɗauke ta a banza.
Daga haka bokanya ta sallami aljanin da ya mata bayani don har wasu ayyukan da ta yi wa mitane aka samu akasi sai da ya faɗa mata dalili duk aikin bokan Naladidi ne. Tsaye ra miƙe rai a ɓace tana surutai da cin alwashi a kan bokan, nan ta ce idan su Umma sun samo kuɗi su dawo za ta musu maganin da ba a isa a saka hannu ba, don ta ce gabaɗaya wwaɗancan maganin da ta musu duk da an nuna matsalar rashin dacewar aikin daga gare ta ne amma ba za ta musu wani maganin ba sai sun sake biya shi ne Umma ta faɗa mata babu kuɗi sai ta ce su je in sun samo kuɗaɗe masu nauyi su dawo haka suka taho jiki babu ƙwari a hanya Umma ta ce
"Oh ni Lubabatu yanzu ashe da aljani na fafata, ashe É—auke gawar aka yi kenan da na tafi sai aljanin ya dawo da gawar kai jama,a lallai sai a bar aikin aljannu, ai ni dai na daddara da aikin matar nan"
Aliya ta ce
",Kenan Umma sai dai na haƙura sa cikar burin nawa?"
Umma tw ce
"Sai dai idan an samu kuɗin mu tuntuɓi wani wajen don wallahi ba zan ke zuwa muna danbarwa da aljannu ba wataran ma su ji haushi su ɗauke i su kaini matattararsu, tun da ni da naci in ce sai na yi aikin ko na gawar ma ba nacewa na yi ba kin ga da akwai tsautsyi sai aljanin ya ɗaukeni, amma ni dai tun da bokanya tana da abokin adawa suna faɗa mu cire kanmu daga zuwa wajenta"
MEENAL
Kafin ta sauke hannunta Husna ta ɗaga nata hannun ta kifa mata marin duk da abin ya zo mata a bazata amma sai ta dake ta dafe kunci da hannu tana rushewa da kuka, zuwan Nasir sai ya kasa fahimtar mene ne tun da ya ga an yi kuma Meenal ya ga an mara sai dai marin da Husna ta yi wa Meenal a kan idanunsa da na Sadiya, sai dai ita Sadiya kasancewar a gaba take ta ga marin da Meenal ɗin ta zabgawa Hibba. Meenal kunci ta dafe da hannu ɗaya ɗayan tana riƙe da ledar dankalin amma kuma yana dafe a cikinta.Tana rayawa a ranta cewa Husna ta taɓo gidan rina din sai ta mata sharrin da ba za ta fitar da kanta ba tun da har ta iya saka hannu ta mare ta, Nasir kuma yana mamakin faruwar abin don ya san dai ya ji an ambaci ɓarayi kuma ya fito ya ga saɓanin abin da kunnuwansa suka ji. Don haka bai tambayai ba a si ba sai ya ce
"Husna mene ne hakan? Matata kike mari a cikin gidana?" Husna da Hibba sun buÉ—e baki za su yi magana sai Meenal ta ce
"Darling wai fa kawai don na ce ihu ɓarayi shi ne ta naushe ni a ciki kuma ta mareni, dama tun ranar nan suke cewa ban isa in haihu a gidan nan ba tun da dai har na saka kake sakawa suna zuwa suna mini aiki" Baki suka saki jin wata kissar da ta musu sannan a yanayin yadda suka ga ya nuna a fuskarsa kamar dai ya yarda da maganganunta, sai dai kafin ya yi magana sai Sadiya ta ce
"Ya kamata ka fara tambayar abin da ya faru kafin ka ɗorawa ɓangare ɗaya laifi ka fara yin bincike domun tabbatar da abin da idanunka ba su gani ba karka yanke hukunci da abin da idanunka suka gani...
Tun kafin ta kai aya Meenal ta ce
Da safe sa ciwon cikin ƙarya ta tashi amma tana ta nuna za ta tafi sutura Abba ya ce tun da ba ta da lafiya ta zauna, daɗi ya cika ranta don ita ba ta so ma ta je suturar gawar da ba ta da tabbacin ta mutu. Ko da Abba ya tafi suturar ya dawo haka ta ce
"Oh duniya ba tabbas har an binne shi ko, rayuwa kenan, yanzu mutum an jima gawa rayuwa kenan, duniya kenan yau kana tafiya a saman ƙasa watarana kuma kana ƙarƙashin ƙasa"
Abba ya ce
"Bari ke dai ai muna rayuwa ba mu san rana da lokacin mutuwarmu ba bare yanzu da ake yawan mutuwar nan ta bagatatan mutuwar fuju,a yanzu za ka rabu da mutum an jima ka ji an ce babu shi" Umma dai ba ta ji amsar tambayarta ba hakan ya sa ta ce
"Wallahi kuwa Allah sarki marigayi Malam Kalla su tasu ta ƙare saura tamu tun da sun shiga kabari"
Abba ya ce
"Kai ina tsoron mutuwa ranar da zan ganni ga ni ga mala,ika, ranar da za a saka ni a kabari ranar da zan ganni a cikin kabari, ya Allah ka rabamu da duhu da azabar kabari da nauyin ƙasa"
Umma ta takarkare ta ce
"Amin" Amma duk ranta ya ɓaci ita so take ya ce an binne shi don tana tsoron ya faɗi abin da ya faru tun da tana ganin bai mutu ba. Har ta yi shiru sai ta ce
"Ko ba a yi suturar ba ne"
Abba ya ce
"Haba ke kuwa sutura ta nawa kuma tuni ma da an dawo mai zai dawo da ni gida in ba a kai shi makwancinsa ba, dama dawowa na yi idan na karya sai na koma idan na ɗan jima wajen karɓar makokin sai na dawo na shirya na tafi kasuwa"
Umma ta ce
"Haka ne" Ta faɗa tana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya.
Aliya kuwa tun da ta ji bayanin da Umma ta mata ta gane cewa Abba ne ya dawo, Umma tana datse kiran wayar ta ajiye kawai take kuka wiwi don rashin cikar burinta kuma tana tunanin yadda za a samu wani kuÉ—in aikin.
Ko da Kasim ya dawo sai da ya fahimci ta sauya amma sai ta nuna masa kanta ne yake ciwo shi kansa haushinsa take ji ta gaji da sakar masa fuskar da take ta gaji da nuna masa tana zaune da shi ne da zuciya ɗaya, bai san cewa da wata manufa take zaune ba burinta yana cika zaman gidansa ya ƙara don ta fi ƙardin zaman aure da talaka, talakan ma mata -maza. Ko wayar ta da ya gani sabuwar ta nuna masa Jidda ce ta saya mata duk da ta fahimci bai ji daɗi ba amma haka ta make abinta tun da ta san shi dai koyaushe cikin fafutukar na abin da za a rufawa kai asiri yake ita ba ta taɓa hango masa zai taka matakin masu arziƙi ba duk da an ce arziƙi kashi ne amma ita ba ta hango arziƙi a tare da wannan mata mazan ba gani take a haka zai ƙare ita kuma ta fi ƙarfin zama da shi yadda take kyakkawa ajin farko da gidan daula ta dace, gidan daular ma ba kowane iri ba.
Bayan nan suka ringa waya da Umma saboda tana tsoron ta je gidan su haɗu da Abba saboda ba ua son yawan zuwa gida babu dalili, shi yawo ba ya yi wa mace kyau a wajensa a ce yau tana can gobe tana can ko da budurwa ce kuwa bare matar aure, ya tsani fita babu dalili. Haka dai suka shirya suka je wajen bokanya don sanar da ita abin da ya faru. Ko da suka je bokanya ta ɗauka za su faɗi kyakkyawan labari amma sai ta ji saɓanin haka, mamaki ya kamata hakan ya sa ta yi wani surkulle ta ɗakko wani ganye tana karkaɗawa tana ambaton wani suna, zuwa can sai suka ji magana ta karaɗe ɗakin ana cewa
"Ya ke bokanya mai kike buƙata a aiwatar miki?" Bokanya ta ce
"Ina so sanin dalilin da ya sa gawar da za a sakawa maganin da na bayar ta motsa har ta riƙe wacce za ta yi aikin"
Mai maganar bisa muryar tsoro ya sheƙe da wata dariyar da har sai da su Umma suka razana sai da dariyar ta lafa ya ce
"Akwai wani abokin aikin ki boka Naladidi wanda sa,insa ta shiga tsakaninku a watan da ya wuce har ya ci alwashin sai ya ɓata miji duk wani aiki to shi ne yake kan bakansa, shi ne ya yi komai" Cike da rashin fahimta ta ce
"Mai ya yi"
Muryar ta ci gaba da cewa
"Ya aika aljani ɗan ƙundalo ya je ya ture Daddyn Ibrahim ɗin da kika yi wa asiri a cokali, shi ne aka kira Ibrahim ɗin aka sanar da shi a lokacin da zai ci abinci wannan dalilin ya sa bai ci abincin da cokalin ba bare har aikin ya ci, sannan shi ya aika aljani gidan gawar Malam Kalla, aljanin ya ɗauke gawar mamacin ya kwanta a wajen da aka ajiye mamacin bayan ya sauya kamanni irin na mamacin ai ba gawar ba ce aka yi ƙoƙarin sakawa maganin ba aljanin ne, da shi suka yi kokawar har sai da ya ga komai bai yi ba a aikin sannan ya koma ya sanar da bokan cewa ya cika aiki hakan ya sa ya ƙara cin alwashin duk aikin da za ki yi sai ya san yadda ya yi ya ɓata aikin bai yiwu ba" Tun da ya fara bayani jikin Umma yake karkarwa musamman idan ta tuna cewa wai da aljani ta yi fafutuka jiya ashe aljani ne ta ja hat zaure duk sai ta ji tsoro ya baibaye ta a ganinta har gwara gawa mutum ce a kan aljani. A neman duniya za ta je ta yi abin da aljannun ma za su ɗauke ta a banza.
Daga haka bokanya ta sallami aljanin da ya mata bayani don har wasu ayyukan da ta yi wa mitane aka samu akasi sai da ya faɗa mata dalili duk aikin bokan Naladidi ne. Tsaye ra miƙe rai a ɓace tana surutai da cin alwashi a kan bokan, nan ta ce idan su Umma sun samo kuɗi su dawo za ta musu maganin da ba a isa a saka hannu ba, don ta ce gabaɗaya wwaɗancan maganin da ta musu duk da an nuna matsalar rashin dacewar aikin daga gare ta ne amma ba za ta musu wani maganin ba sai sun sake biya shi ne Umma ta faɗa mata babu kuɗi sai ta ce su je in sun samo kuɗaɗe masu nauyi su dawo haka suka taho jiki babu ƙwari a hanya Umma ta ce
"Oh ni Lubabatu yanzu ashe da aljani na fafata, ashe É—auke gawar aka yi kenan da na tafi sai aljanin ya dawo da gawar kai jama,a lallai sai a bar aikin aljannu, ai ni dai na daddara da aikin matar nan"
Aliya ta ce
",Kenan Umma sai dai na haƙura sa cikar burin nawa?"
Umma tw ce
"Sai dai idan an samu kuɗin mu tuntuɓi wani wajen don wallahi ba zan ke zuwa muna danbarwa da aljannu ba wataran ma su ji haushi su ɗauke i su kaini matattararsu, tun da ni da naci in ce sai na yi aikin ko na gawar ma ba nacewa na yi ba kin ga da akwai tsautsyi sai aljanin ya ɗaukeni, amma ni dai tun da bokanya tana da abokin adawa suna faɗa mu cire kanmu daga zuwa wajenta"
MEENAL
Kafin ta sauke hannunta Husna ta ɗaga nata hannun ta kifa mata marin duk da abin ya zo mata a bazata amma sai ta dake ta dafe kunci da hannu tana rushewa da kuka, zuwan Nasir sai ya kasa fahimtar mene ne tun da ya ga an yi kuma Meenal ya ga an mara sai dai marin da Husna ta yi wa Meenal a kan idanunsa da na Sadiya, sai dai ita Sadiya kasancewar a gaba take ta ga marin da Meenal ɗin ta zabgawa Hibba. Meenal kunci ta dafe da hannu ɗaya ɗayan tana riƙe da ledar dankalin amma kuma yana dafe a cikinta.Tana rayawa a ranta cewa Husna ta taɓo gidan rina din sai ta mata sharrin da ba za ta fitar da kanta ba tun da har ta iya saka hannu ta mare ta, Nasir kuma yana mamakin faruwar abin don ya san dai ya ji an ambaci ɓarayi kuma ya fito ya ga saɓanin abin da kunnuwansa suka ji. Don haka bai tambayai ba a si ba sai ya ce
"Husna mene ne hakan? Matata kike mari a cikin gidana?" Husna da Hibba sun buÉ—e baki za su yi magana sai Meenal ta ce
"Darling wai fa kawai don na ce ihu ɓarayi shi ne ta naushe ni a ciki kuma ta mareni, dama tun ranar nan suke cewa ban isa in haihu a gidan nan ba tun da dai har na saka kake sakawa suna zuwa suna mini aiki" Baki suka saki jin wata kissar da ta musu sannan a yanayin yadda suka ga ya nuna a fuskarsa kamar dai ya yarda da maganganunta, sai dai kafin ya yi magana sai Sadiya ta ce
"Ya kamata ka fara tambayar abin da ya faru kafin ka ɗorawa ɓangare ɗaya laifi ka fara yin bincike domun tabbatar da abin da idanunka ba su gani ba karka yanke hukunci da abin da idanunka suka gani...
Tun kafin ta kai aya Meenal ta ce