Sashe 88
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nasir ya sha masifa a wajen Meenal don tana faɗin ya zaɓi da Sadiya a kanta. Ranar a kan gado ya kwana shi kaɗai ita kuma a ƙasa don kawai ta nuna masa tana fushi, ta ɗauka zai saka a cire nepar washe gari sai ta ga ɗiff bai yi maganar ba ma hakan ya sa ta saka a ranta dole ta je gida domin ta kaiwa Momi kuɗi a je a yi aiki a kansa wato ya dawo sai abin da ta ce masa.
Sadiya kuwa a daren ta haɗa mango juice da zoɓo ta saka a frezer ɗinta. Tana ta addu,ar Allah ya ɗota ta a kansu, tun da ta ga dole sai tana kataɓus wajen ƴancinta tun da babu mai bin bayanta ya ƙwatar mata haƙƙinta daga gidansu har gjdansu Nasir ɗin.
Tuni kasuwar kayan sanyi ta dawo, bayan kwana biyu aka sake kafe sunayen ƴan tallafi Allah da ikonsa sunan Sadiya ya sake fitowa amma wannan karon ban da Noor dama an ce wasu hsr sau uku ma sunan su yana fitowa haka ta je ta karɓo kuɗin nan, tana ta al,ajabi duk da ba a mamaki da lamarin ubangiji ga shi dai ta yi asara amma da yake Allah maji roƙo ne ya mayar mata a lokaci ƙanƙani, sai ta sauya wajen ajiya kawai ya zamana ƙananan kuɗi take ajiyewa a gida, su manyan kuɗin kawai sai ta ba almajirinta ya je pos ta rubuta masa acc no ta a je a tura mata, ya zamana ba ta ma ajiye cash ɗin bare a ɗauke.
Meenal kuwa wuni ta tambaya zuwa gidansu, ta haɗa kan kuɗin wajen Sadiya wanda ta sata, da na wajen Nasir da take masa sata yadda ba zai gane ba, ko ya ce zai sauke ta a gida sai ta ce masa ya je za ta hau napep. Waya suka yi da wani Alhajinta cikin wanda suke holewarsu kafin ta yi aure sannan suna shirmensu a waya ma, haka suka haɗu a hotel ya kama musu ɗaki suka sheƙe ayarsu, ya mata alƙawarin za ta ji alert mai nauyi domin a lokacin wai bankinsa ya samu matsala kuma ba shi da cash.
A ƙofar gidansu ya sauke ta, dama ta yi wa Momi waya haka suka fito Momi ta tare musu wani mai napep, su biyu ne a ciki mai napep da kuma wani a gefensa a zaune, Momi ta kwatanta musu inda za su kaisu, don sosai sai an fita ma daga gari wani ɗan ɗauye ne haka suka yi ciniki, sai suka yanka musu kuɗi da yawa Mominta dage tana neman ragi buɗar bakin Meenal tana dariya ta ce
"Momi akwai kuɗi fa, kuɗi ba matsala ba ne kawai mu je ai biyan buƙata kawai ake so, ai tun da Nasir har ya fifita wanann ƙazamar matar tasa marar aji sai ya gwamamce kiɗa da karatu"
Momi ta ce
",Yaushe ta zama ƙazama bayan na ji ana cewa tsaftar masifa gare ta"
Meenal ta ce
",A,a kawai na faÉ—a ne"
Haka suka ci gaba da tafiya suna tafiya su Meenal da Hajiya suna ta tattauna zancen kuÉ—in da yake a jakar.
Momi ta ce
,"Wallahi gwara da kika raba shegiya da kuÉ—in ai da sannu zaman gidan zai gagare ta,"
Meenal ta ce
"Ai bokan nan ko nawa ya buƙata zan basho, dama akwai ma wani alƙawarin kuɗi da aka mini" Sun saki baki suna ta zuba, basa lura da cewa basu san su waye masu napep ɗin ba, kawai mutane in suka shuga napep ko motar haya sai su saki baki suna ta zance, wani ma sirrinsa zai ke faɗa abubuwa dai barkatai ba a takatsantsan.
Duk abin da suke masu napep É—in suna jin su, sannan suna ta yi wa juna magana da ido don sun gama shirya komai ba tare da su Meenal sun sani ba. Sai da suka yi nisa a tsakiyar daji gaba babu kowa haka ma baya sai kawai mai napep ta taka birki ya tsaya Momi ta ce
"Ya dai?"
Sai ya ce
"Mai ne ya ƙare shi ne zan zuba wani"
Meenal ta ce
"Don ma kana da akwai da yanzu a nan ina za a samu wani mai"
Mai napep ta ɓangaren Momi ɗayan da ya fito ta ɓangare Meenal dama majiya ƙarfi ne, hasali ma ba masu napep ba ne arowa suka yi a wajen abokinsu don su yi damfara sai kuma tsautsayi ya faɗa a kan su Momin.
Duka suka yi wa su Momin suka ƙwace jakar Meenal da wayoyin su, sai da suka musu lilis sannan suka shiga napep ɗin suka kwasa a guje, suka bar su yashe a nan tsakiyar hanyar tsakar daji, kowacce tana murƙususu don hatta bakinsu da hanci ya sha naushi, basu ma da ƙwarin gwiwar hadda ce lambar jikin napep ɗin!
Yau Sadiya kawai muka taɓo ina da uzuri ne.
MAMAN AFRAH
09025576222
https://chat.whatsapp.com/DDmSp3AUB7gJnJQLnau59V?mode=hqrt1
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 2ï¸âƒ£7ï¸âƒ£
UMMA
Da tsananin faɗuwar gaba take kallon ƙullin maganin guda biyu da bokanya ta bata, tana jin tsoron tunkarar sabuwar gawar tare da taraddadin kar ta je asirinta ya tonu domin tana ganin ta yaya za a ce daga ka fesar da magani ya bi iska kowa zai suma? Wannan lamari ne mai girma sai dai tun da ta yarda da aikin sihirin bokanya sai ta cire kokwanto a ciki tana rayawa a ranta wannan lokacin sai an samu nasara fiye da lokacin da aka faɗi babu nasara wanda Aliya ta yi aikin cokali, sannan wannan lokacin ba za ta yarda ta yi asarar kuɗin da aka biya na maganin ba.
Sai da ta sakko daga barandar ƙofar ɗakinta ta shiga tunanin ya za ta yi da Abba? Tun da dai ta san yana masallacin sai dai tuna sai an yi sallar isha yake dawowa hakan ya sa ta ji dama dama wai kibiya a ido. Fitowarta daga gida kenan ta tsaya tana kalle-kalle tun da dai ta san ita inda za ta je aiwatar da aikin nata aiki ne mai haɗari, sai dai dole ta yi takatsan tsan waje tafiya gidan Malam Kalla saboda yanzu dai ai maganin bai fara aiki ba tun da sai ta je ta fwsa maganin ne kowa zai suma sannan bakin kowa ya mutu komda wani ya gani bau mai tambya kamar yadda bokanya ta faɗa.
Ko da ta tafi tana jin tsoron yana ƙara mamaye ranta, sai dai mugun nufinta a kan Jidda na sai ta dawo ƙarƙashinsu sun ƙasƙantar sa ita, Ibrahim ɗin da ya zama gatanta sun maido da shi soyayyar Aliya ce take mulki a cikin zuciyarsa, hakan ya sa ta ji wani irin ƙarfin gwiwa a zuciyarrta ta ce
'Jidda dole ne ki ƙarƙanta! Dole ki zama abin tausayi kuma abin kwatance amma ba kwatance mai kyau ba sai dai kwatance na tausayawa, ko maƙiyinki sai ya tausaya muki Jidda, domin yanzu ƙiyayyar da nake miki ta linku ba zai taɓa iyuwa ba ke kina rayuwa a cikin daula ke da baki da wani gata ko galihu, baki da wani kyakkyawan asali ke asali mai munin ba babu shi, har ki fi ƴata samun gata da kulawa kina rayuwa a haɗaɗɗan gida mai cike da ƴan aiki ana miki hidima ana girmamaki, kina juya kan naira ta yadda kika so, kina ado da zinare hmmm wai ke ce har mijinki yake yi wa uban da ba shi ne silar dirowarki duniya ba kyautar mota, ni tawa ƴar tana can mijinta yana yawo ranar duniya tana ƙarewa a kansa a kasuwa, tabbas da sake!' Ta faɗa tana ƙara sauri don ganin ta aiwatar da abin da ta yi niyya domin maganar zucin da ta yi ya ƙara ingizata a kan aiwatarwar.
Tun da ta fito take cin karo da mutanr jifa jifa ana tafiya gidan, da alama jajanta mutuwar ne ko dai mutanen suna da alaƙa da mamacin wato ƴan uwa na kusa tun da dai an ce sutura sai gobe.
Ta kusa ƙarasawa gidan ta hangi su Abba su uku shi da ladan ɗin masallacin nasu da kuma liman sun nufi gidan rasuwar, da sauri ta faɗa gidan ta tsaya daga bayan ƙofar gidan a cikin zauren ta laɓe a jikin ƙofar tun da ta san maganin bai fara aiki ba Abba yana ganinta zai tambaye ta ba,asi duk da mutuwa ce a maƙota yana da kyau a yi haƙƙin maƙota don jajantawa amma sai ya san ai duk gaggawar asara ta jirayi samu, ma,ana duk saurin zuwan da take ta jira ya dawo daga masallacin ta tambaye shi.
Tana ganinsu suka shige, baki ta taɓe zuciyarta tana ingizata. Ƙullin maganin ta buɗe hannunta saboda ɗan duhun da ya fara ratsa duniya na magriba sai ra kasa tantance wanne ne na fesawa a cikin gidan wanne ne na sakawa a hancin gawar!.
Gudun kar ta yi ɓaran ɓarama ta fesa na hancin gawa su ƙi suma mutanen gidan sai ta yi saɗaf saɗaf ta fita dagan zauren, tana fita ta ga wata yarinya tana tafiya tana ƴar waƙa da fitila a hannunta, kiranta ta yi ta ce ta ara mara fitilar ta karma ta haska maganin ta bambance sai ta ba yarinyar fitilar ta juya cikin gidan.
Sadiya kuwa a daren ta haɗa mango juice da zoɓo ta saka a frezer ɗinta. Tana ta addu,ar Allah ya ɗota ta a kansu, tun da ta ga dole sai tana kataɓus wajen ƴancinta tun da babu mai bin bayanta ya ƙwatar mata haƙƙinta daga gidansu har gjdansu Nasir ɗin.
Tuni kasuwar kayan sanyi ta dawo, bayan kwana biyu aka sake kafe sunayen ƴan tallafi Allah da ikonsa sunan Sadiya ya sake fitowa amma wannan karon ban da Noor dama an ce wasu hsr sau uku ma sunan su yana fitowa haka ta je ta karɓo kuɗin nan, tana ta al,ajabi duk da ba a mamaki da lamarin ubangiji ga shi dai ta yi asara amma da yake Allah maji roƙo ne ya mayar mata a lokaci ƙanƙani, sai ta sauya wajen ajiya kawai ya zamana ƙananan kuɗi take ajiyewa a gida, su manyan kuɗin kawai sai ta ba almajirinta ya je pos ta rubuta masa acc no ta a je a tura mata, ya zamana ba ta ma ajiye cash ɗin bare a ɗauke.
Meenal kuwa wuni ta tambaya zuwa gidansu, ta haɗa kan kuɗin wajen Sadiya wanda ta sata, da na wajen Nasir da take masa sata yadda ba zai gane ba, ko ya ce zai sauke ta a gida sai ta ce masa ya je za ta hau napep. Waya suka yi da wani Alhajinta cikin wanda suke holewarsu kafin ta yi aure sannan suna shirmensu a waya ma, haka suka haɗu a hotel ya kama musu ɗaki suka sheƙe ayarsu, ya mata alƙawarin za ta ji alert mai nauyi domin a lokacin wai bankinsa ya samu matsala kuma ba shi da cash.
A ƙofar gidansu ya sauke ta, dama ta yi wa Momi waya haka suka fito Momi ta tare musu wani mai napep, su biyu ne a ciki mai napep da kuma wani a gefensa a zaune, Momi ta kwatanta musu inda za su kaisu, don sosai sai an fita ma daga gari wani ɗan ɗauye ne haka suka yi ciniki, sai suka yanka musu kuɗi da yawa Mominta dage tana neman ragi buɗar bakin Meenal tana dariya ta ce
"Momi akwai kuɗi fa, kuɗi ba matsala ba ne kawai mu je ai biyan buƙata kawai ake so, ai tun da Nasir har ya fifita wanann ƙazamar matar tasa marar aji sai ya gwamamce kiɗa da karatu"
Momi ta ce
",Yaushe ta zama ƙazama bayan na ji ana cewa tsaftar masifa gare ta"
Meenal ta ce
",A,a kawai na faÉ—a ne"
Haka suka ci gaba da tafiya suna tafiya su Meenal da Hajiya suna ta tattauna zancen kuÉ—in da yake a jakar.
Momi ta ce
,"Wallahi gwara da kika raba shegiya da kuÉ—in ai da sannu zaman gidan zai gagare ta,"
Meenal ta ce
"Ai bokan nan ko nawa ya buƙata zan basho, dama akwai ma wani alƙawarin kuɗi da aka mini" Sun saki baki suna ta zuba, basa lura da cewa basu san su waye masu napep ɗin ba, kawai mutane in suka shuga napep ko motar haya sai su saki baki suna ta zance, wani ma sirrinsa zai ke faɗa abubuwa dai barkatai ba a takatsantsan.
Duk abin da suke masu napep É—in suna jin su, sannan suna ta yi wa juna magana da ido don sun gama shirya komai ba tare da su Meenal sun sani ba. Sai da suka yi nisa a tsakiyar daji gaba babu kowa haka ma baya sai kawai mai napep ta taka birki ya tsaya Momi ta ce
"Ya dai?"
Sai ya ce
"Mai ne ya ƙare shi ne zan zuba wani"
Meenal ta ce
"Don ma kana da akwai da yanzu a nan ina za a samu wani mai"
Mai napep ta ɓangaren Momi ɗayan da ya fito ta ɓangare Meenal dama majiya ƙarfi ne, hasali ma ba masu napep ba ne arowa suka yi a wajen abokinsu don su yi damfara sai kuma tsautsayi ya faɗa a kan su Momin.
Duka suka yi wa su Momin suka ƙwace jakar Meenal da wayoyin su, sai da suka musu lilis sannan suka shiga napep ɗin suka kwasa a guje, suka bar su yashe a nan tsakiyar hanyar tsakar daji, kowacce tana murƙususu don hatta bakinsu da hanci ya sha naushi, basu ma da ƙwarin gwiwar hadda ce lambar jikin napep ɗin!
Yau Sadiya kawai muka taɓo ina da uzuri ne.
MAMAN AFRAH
09025576222
https://chat.whatsapp.com/DDmSp3AUB7gJnJQLnau59V?mode=hqrt1
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 2ï¸âƒ£7ï¸âƒ£
UMMA
Da tsananin faɗuwar gaba take kallon ƙullin maganin guda biyu da bokanya ta bata, tana jin tsoron tunkarar sabuwar gawar tare da taraddadin kar ta je asirinta ya tonu domin tana ganin ta yaya za a ce daga ka fesar da magani ya bi iska kowa zai suma? Wannan lamari ne mai girma sai dai tun da ta yarda da aikin sihirin bokanya sai ta cire kokwanto a ciki tana rayawa a ranta wannan lokacin sai an samu nasara fiye da lokacin da aka faɗi babu nasara wanda Aliya ta yi aikin cokali, sannan wannan lokacin ba za ta yarda ta yi asarar kuɗin da aka biya na maganin ba.
Sai da ta sakko daga barandar ƙofar ɗakinta ta shiga tunanin ya za ta yi da Abba? Tun da dai ta san yana masallacin sai dai tuna sai an yi sallar isha yake dawowa hakan ya sa ta ji dama dama wai kibiya a ido. Fitowarta daga gida kenan ta tsaya tana kalle-kalle tun da dai ta san ita inda za ta je aiwatar da aikin nata aiki ne mai haɗari, sai dai dole ta yi takatsan tsan waje tafiya gidan Malam Kalla saboda yanzu dai ai maganin bai fara aiki ba tun da sai ta je ta fwsa maganin ne kowa zai suma sannan bakin kowa ya mutu komda wani ya gani bau mai tambya kamar yadda bokanya ta faɗa.
Ko da ta tafi tana jin tsoron yana ƙara mamaye ranta, sai dai mugun nufinta a kan Jidda na sai ta dawo ƙarƙashinsu sun ƙasƙantar sa ita, Ibrahim ɗin da ya zama gatanta sun maido da shi soyayyar Aliya ce take mulki a cikin zuciyarsa, hakan ya sa ta ji wani irin ƙarfin gwiwa a zuciyarrta ta ce
'Jidda dole ne ki ƙarƙanta! Dole ki zama abin tausayi kuma abin kwatance amma ba kwatance mai kyau ba sai dai kwatance na tausayawa, ko maƙiyinki sai ya tausaya muki Jidda, domin yanzu ƙiyayyar da nake miki ta linku ba zai taɓa iyuwa ba ke kina rayuwa a cikin daula ke da baki da wani gata ko galihu, baki da wani kyakkyawan asali ke asali mai munin ba babu shi, har ki fi ƴata samun gata da kulawa kina rayuwa a haɗaɗɗan gida mai cike da ƴan aiki ana miki hidima ana girmamaki, kina juya kan naira ta yadda kika so, kina ado da zinare hmmm wai ke ce har mijinki yake yi wa uban da ba shi ne silar dirowarki duniya ba kyautar mota, ni tawa ƴar tana can mijinta yana yawo ranar duniya tana ƙarewa a kansa a kasuwa, tabbas da sake!' Ta faɗa tana ƙara sauri don ganin ta aiwatar da abin da ta yi niyya domin maganar zucin da ta yi ya ƙara ingizata a kan aiwatarwar.
Tun da ta fito take cin karo da mutanr jifa jifa ana tafiya gidan, da alama jajanta mutuwar ne ko dai mutanen suna da alaƙa da mamacin wato ƴan uwa na kusa tun da dai an ce sutura sai gobe.
Ta kusa ƙarasawa gidan ta hangi su Abba su uku shi da ladan ɗin masallacin nasu da kuma liman sun nufi gidan rasuwar, da sauri ta faɗa gidan ta tsaya daga bayan ƙofar gidan a cikin zauren ta laɓe a jikin ƙofar tun da ta san maganin bai fara aiki ba Abba yana ganinta zai tambaye ta ba,asi duk da mutuwa ce a maƙota yana da kyau a yi haƙƙin maƙota don jajantawa amma sai ya san ai duk gaggawar asara ta jirayi samu, ma,ana duk saurin zuwan da take ta jira ya dawo daga masallacin ta tambaye shi.
Tana ganinsu suka shige, baki ta taɓe zuciyarta tana ingizata. Ƙullin maganin ta buɗe hannunta saboda ɗan duhun da ya fara ratsa duniya na magriba sai ra kasa tantance wanne ne na fesawa a cikin gidan wanne ne na sakawa a hancin gawar!.
Gudun kar ta yi ɓaran ɓarama ta fesa na hancin gawa su ƙi suma mutanen gidan sai ta yi saɗaf saɗaf ta fita dagan zauren, tana fita ta ga wata yarinya tana tafiya tana ƴar waƙa da fitila a hannunta, kiranta ta yi ta ce ta ara mara fitilar ta karma ta haska maganin ta bambance sai ta ba yarinyar fitilar ta juya cikin gidan.