Sashe 84
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Meenal ganin Sadiya ta danganta da maganar yanke wuta don da kuɗinta ma Naair ya ƙi ya saka a amayar mata jawai donnya nuna bata da kima da muhimmanci, sannan bata da wani galihu a wajensa, bai san darajarta ba, ganin ta mayar da hankali a kan sauran kasuwancinta na cikin gidan tana damƙar cikinikinta, kuma sai ta ga kullum tamkar ƙara buɗe mata hanyoyin samu ake don jama,a haka suke turruruwa wajen saye mata jayan tamkar kyauta take rabawa, don sai ma ta fara zargin ko dai wajen malamai ta je ta nemi kasuwa wato ko da maganin kasuwa take amfani shi ya sa take samun ciniki..
Abin da bata sani va shi ne Sadiya babu abin da ta riƙe sai addu,a idan ta yi sallah tana ɗaga hannu ta faɗawa ubangiji damuwarta sannan ta roƙe shi ya kawo mata kasuwa me albarka ya ƙara kawo mata masu sayen kayanta ta ko ina, hatta bashi da sauran masu kasuwanci suke kuka da shi idan an karɓi kayansu bashi ba a biyansu ko a basu rabi a hana rabi wata ma ta cinye kenan, to Sadiya babu mai riƙe mata kuɗi kuma addu,a ce makamin saboda tana faɗawa ubangiji ya raba ta da ƴan bashi duk wani wanda zai cinye mata kuɗinta Allah ya nesanta ta da shi.
Yau ya kama Laraba Sadiya ta tambayi Naair zuwa gidan Kaka dubiya saboda Kaka tana zazzaɓi danyake jiya ta faɗa masa da ta ganshi a tsakar gida kuma ya amince, don har yau Nasir bai shiga ɗakinta da sunan tana da baki ko matsayinta na matarsa ba ita bata ma taɓa jin ƙarin aure irin wannan ba a duk da tana ji a labari ana cewa wata idan aka mata kishiya mijin yana neman ta bashi kwananta ya ƙarawa amarya wani ya siya wani kuma ya ƙwata ta ƙarfi, kwanaki ta ji labarin matar da ta ce tun da mijinta ya yi aure shekara uku bai kusance ta ba, kai ɗakinta ma sai ya ga dama zai shiga kuma ba ya yin sama da minti goma zai fita, ashe dai ita ma al,amarin yana zuwa kanta rayuwa kenan.
Yana tafiya kasuwa ta shirya ta shirya Kalifa ta tattara kayan sana,arta ta saka a kicin ta janyo kicin ɗin ta kulle haka ma falonta. Meenal da bata san Sadiya ta tambayi Nasir fita ba sai ganinsu ta yi da shirin fita Sasiyar tana sanye da atamda glitter da ta saya a wajen maman afrah an mata ɗinkin ya yi kyau sai hinabi mai ƙasan net wanda yake pink ya yi daidai da wata ƙananun fulawowi pink da suke jikin atamfar sai takalmin ta marar tudu. Ta yi kyau sosai ga Kalifan ma sanye da riga da wando ƴan kanti sun yi kyau da ɗan takalminsa sosai suka fito abinsu sai kawai ta ji ƙyashi cewa wannan fa da kuɗin sana,a Sadiyar ta saya tun da ta san cewa Nasir ba zai saya musu ba. A zuciyarta ta ce
'Wannan matar matuƙar tana sana,a za ta fara haɗa kafaɗa da ni tabbas amma zan yi maganin abin' Ko kallo bata ishi Sadiya ba ta kama hannun Kalifa suka fice daga gidan sai ƙaran rufowar ƙofar gidan ta ji.
Ranta yana ta ƙuna ta koma ɗakinta. Can zuwan an jima ta ji ana ta buga gidan ta taso rai a ɓace ta zo ta ce
"Wai waye? Bashi ko tara za a damu mutane da buga ƙofa?" Muryar wani namiji ta ji yana tambayar mai gidan yana nan ta ce masa ba ya nan ta juya tana jan wani tsaki ta dawo gidan kamar an ce ta duba ƙasa a gabanta sai kawai ta ga mukullai, kallon mukullin take sosai tana son sanin mukullin mene ne don ta san ba na Nasir ba ne. A zuciyarta ta ce
"Sadiya" Kai ta shiga gyaɗawa alamar tabbayarwa ta tsugunna ta ɗauka tana duba mukullan a take wani tunani ya faɗo mata, da sauri ta koma ta sakawa ƙofar gidan sakata ta dawo da sauri mukulli ɗaya ta saka anjikin ƙofar ɗakin Sadiya sai ya shiga sai dai bai buɗe ba sai da ta sake gwada wani ya buɗe ƙofar wani tsalle ta yo da ihu a fili ta furta
"Tsuntsu daga sama gasasshe" Falon ta shigo wani ƙamashin freshner mai sanyin ƙamshi ya dakar mata hanci ko ina tsaf a gyare wajen freezer ta nufa ta buɗe tana taɓe baki sai ta ga babu komai a ciki an ma goge ta tass. Wani tsaki ta ja a fili ta ce
",Ba ke ce a gabana ba, bakya cikin target ɗina, tun da ke na gama da nake ɓangaren tun da an cire wutar nepar baki da sauran wani amfani sai zama a wajen" Ta faɗa tana jan murfin ta rufe freezer ta nufi cikin bedroom. Yadda gadon yake a ɗame shi ne abin ya bata mamaki sannan zanen gadon fari ne tass mai manyan flowers blue baki ta taɓe tana kallon kayan kan madubin.
A fili ta ce
"Yanzu zan yi abin da ya kawoni" Ta faɗa tana ajiye mukullin hannunta da yake da ta buɗe ƙofar da shi ta shiga, tana ajiyewa a zuciyarta ta ce
'Da zafi-zadi ake dukan ƙarfe, kuma da sanyin safiya ake kama fara, ba zan tsaya kallon ruwa kwaɗo ya mini ƙafa ba, in dai zaman kishi ne ni babu macen da za ta iya gagarawa da ni domin sai na mata kishi da kissa ƴar ƙasa yadda sai ta ji tsanar gidan mijin da kanta don sai na takurawa kishiya" Ta faɗa tare da buɗe drower Sadiya ta shiga bincike kayan kawai take watsowa ƙasa amma bata ga abin da take nema ba. Haka ta gama bincikenta ta mayar da su yadda suke tamksr bata taɓa su ba domin ta iya takunta.
Haka ta gama dubawa amma bata ga abin da take nema ba, ranta sai wuya yake saboda ta san tabbas yau wata dama ce da ta samu wacce ba lallai ta same ta ba. Ƙarƙashin gado ta shiga dubawa amma bata gani ba, tsaye ta tashi ta tsaya rana riƙe da tsantsa ta damƙe fatar bakinta da haƙorinta na sama. Duk cikin wani abu da take gani za a ɓiye abin da take nema ta duba amma bata gani ba, gadon ta taka ta duba saman drower nan ma babu sai da ta sakko ta lura da ƙaramar lokkar jikin bed side drower da sauri ta jufi can ta buɗe sama da ƙasa amma babu. Kasancewar biyu ne sai ta koma ɗaya gefen ta buɗe ta saman sai ta ga panties ɗin Kakifa ne a ciki wanda suke a laye, tsaki ta yi ta tuƙunɗuna su ta tura ta rufe lokar, tana janyo ta saman sai ta ga wata ƙaramar jaka pose taɓa jakar ta yi ai kuwa ta ji ɗan tudu da sauri
ta fito da jakar tana fatan a dace tana buɗewa kuwa ta ga abin da take nema wani murmushi mai bayyana haƙora ta yi ganin kuɗaɗen a ciki a laye suke kasancewar pose ɗin tana da ɗan girma, ƴan dubu dubu ne a laye sai ƴan ɗari biyar biyar sai ɗari bibiyu da ƴan ɗari ɗari. Ganin kuɗin cunkus sai abun ya bata mamaki a ƙiyasce tana tunanin kuɗin nan zai iya kusan kaiwa dubu ɗari. Fito dansu ta yi duka ta zige zip ɗin ta buɗe ɗaya gefen sai ta ga ƴan hamsin hamsin ne da sauran canjuna a ciki su kuma dai ba su fi dubu biyar ba fito dansu ta yi duka a fili ta furta
"Wai dama sana,ar cikin gida tana kawo kuɗi har haka? Lallai wannan ake cewa bar ganin ka tara ka kiyayi mai nema ashe har tana samun rufin asiri a sana,arta haka lallai na yi sake!" Ƙaran bugun ƙofar gida ne ya ankarar da ita vata san lokacin da ta tashi tsaye daga zaunen da take ba, ga kuɗin duk ta baza haka ta shiga haɗa su tana karkarwar jiki don ta san asirin ta zai iya tonuwa tunanin ta ma Sadiya ce ta dawo duba mukullin da ta jefar. Lokar ta mayar ta rufe ta naɗo ƙasan rigarta da ta zuba duka kuɗin sai da ta zo faon a guje sannan ta tuna da mukullin da suri ta juya ta ɗakko har lokacin tana ji an bugawa fitowa ta yi amma bata rufa ɗakin ba ta ce
"A nan ne? Waye?" Ta faÉ—a tana jiran jin muryar Sadiya kawai sai ta ji muryar wata yarinya ta ce
" Mango da zoɓo za a bani" Wani uban tsaki ta ja ta ce
"A kan wani mango za ki zo ki damu jama,a to an dajna siyar da mango da zoɓo a nan" Yarinyar ta ce
"To akwai pure water?"
Meenal ta ce
"Babu pure water sai ubanki" ,Ta faÉ—a a zuciye yarinyar ta ce
"Na gane ki ba anty Sadiya ba ce kishiyarta ce ƴar baƙin ciki wataƙila antyn bata nan" Tana faɗar hakan ta ɗauki dutsi ta buga a ƙofar da ƙarfi ta zuga da gudu, Meenal tana so ta zo ta buɗe ƙofar ta kikkifawa yarinyar mari amma kuma abin da take yi ya fi wancan. Ɗakin ta koma ta ɗakko jakar ta rufe lokar ta tsaya ta tabbatar da komai yana yadda yake ta fito ta zo ta kulle ɗakin. Ɗakinta ta nufa da sauri ta je ta juye kuɗin a jakarta ta fito da pose ɗin a hannunta kicin ta je ta ɗakko ashana ta xo ta kyarta ta sakana jikin pose ɗin ganin jakar ta kama ta sheƙe da dariyar mugunta, sai da ta ƙone ƙurmus ta tattara ta kwshe ta je ta yi fuloshin ɗinsa a toilet.
Mukullan ta ɗakko ta zo wajen zaure ta jefar da su a ƙasa ta koma ta kwanta a bedroom ɗinta tana lissafa kuɗaɗen da ba da guminta ba ta samu tana jin daɗinsu.
A fili ta ce
Abin da bata sani va shi ne Sadiya babu abin da ta riƙe sai addu,a idan ta yi sallah tana ɗaga hannu ta faɗawa ubangiji damuwarta sannan ta roƙe shi ya kawo mata kasuwa me albarka ya ƙara kawo mata masu sayen kayanta ta ko ina, hatta bashi da sauran masu kasuwanci suke kuka da shi idan an karɓi kayansu bashi ba a biyansu ko a basu rabi a hana rabi wata ma ta cinye kenan, to Sadiya babu mai riƙe mata kuɗi kuma addu,a ce makamin saboda tana faɗawa ubangiji ya raba ta da ƴan bashi duk wani wanda zai cinye mata kuɗinta Allah ya nesanta ta da shi.
Yau ya kama Laraba Sadiya ta tambayi Naair zuwa gidan Kaka dubiya saboda Kaka tana zazzaɓi danyake jiya ta faɗa masa da ta ganshi a tsakar gida kuma ya amince, don har yau Nasir bai shiga ɗakinta da sunan tana da baki ko matsayinta na matarsa ba ita bata ma taɓa jin ƙarin aure irin wannan ba a duk da tana ji a labari ana cewa wata idan aka mata kishiya mijin yana neman ta bashi kwananta ya ƙarawa amarya wani ya siya wani kuma ya ƙwata ta ƙarfi, kwanaki ta ji labarin matar da ta ce tun da mijinta ya yi aure shekara uku bai kusance ta ba, kai ɗakinta ma sai ya ga dama zai shiga kuma ba ya yin sama da minti goma zai fita, ashe dai ita ma al,amarin yana zuwa kanta rayuwa kenan.
Yana tafiya kasuwa ta shirya ta shirya Kalifa ta tattara kayan sana,arta ta saka a kicin ta janyo kicin ɗin ta kulle haka ma falonta. Meenal da bata san Sadiya ta tambayi Nasir fita ba sai ganinsu ta yi da shirin fita Sasiyar tana sanye da atamda glitter da ta saya a wajen maman afrah an mata ɗinkin ya yi kyau sai hinabi mai ƙasan net wanda yake pink ya yi daidai da wata ƙananun fulawowi pink da suke jikin atamfar sai takalmin ta marar tudu. Ta yi kyau sosai ga Kalifan ma sanye da riga da wando ƴan kanti sun yi kyau da ɗan takalminsa sosai suka fito abinsu sai kawai ta ji ƙyashi cewa wannan fa da kuɗin sana,a Sadiyar ta saya tun da ta san cewa Nasir ba zai saya musu ba. A zuciyarta ta ce
'Wannan matar matuƙar tana sana,a za ta fara haɗa kafaɗa da ni tabbas amma zan yi maganin abin' Ko kallo bata ishi Sadiya ba ta kama hannun Kalifa suka fice daga gidan sai ƙaran rufowar ƙofar gidan ta ji.
Ranta yana ta ƙuna ta koma ɗakinta. Can zuwan an jima ta ji ana ta buga gidan ta taso rai a ɓace ta zo ta ce
"Wai waye? Bashi ko tara za a damu mutane da buga ƙofa?" Muryar wani namiji ta ji yana tambayar mai gidan yana nan ta ce masa ba ya nan ta juya tana jan wani tsaki ta dawo gidan kamar an ce ta duba ƙasa a gabanta sai kawai ta ga mukullai, kallon mukullin take sosai tana son sanin mukullin mene ne don ta san ba na Nasir ba ne. A zuciyarta ta ce
"Sadiya" Kai ta shiga gyaɗawa alamar tabbayarwa ta tsugunna ta ɗauka tana duba mukullan a take wani tunani ya faɗo mata, da sauri ta koma ta sakawa ƙofar gidan sakata ta dawo da sauri mukulli ɗaya ta saka anjikin ƙofar ɗakin Sadiya sai ya shiga sai dai bai buɗe ba sai da ta sake gwada wani ya buɗe ƙofar wani tsalle ta yo da ihu a fili ta furta
"Tsuntsu daga sama gasasshe" Falon ta shigo wani ƙamashin freshner mai sanyin ƙamshi ya dakar mata hanci ko ina tsaf a gyare wajen freezer ta nufa ta buɗe tana taɓe baki sai ta ga babu komai a ciki an ma goge ta tass. Wani tsaki ta ja a fili ta ce
",Ba ke ce a gabana ba, bakya cikin target ɗina, tun da ke na gama da nake ɓangaren tun da an cire wutar nepar baki da sauran wani amfani sai zama a wajen" Ta faɗa tana jan murfin ta rufe freezer ta nufi cikin bedroom. Yadda gadon yake a ɗame shi ne abin ya bata mamaki sannan zanen gadon fari ne tass mai manyan flowers blue baki ta taɓe tana kallon kayan kan madubin.
A fili ta ce
"Yanzu zan yi abin da ya kawoni" Ta faɗa tana ajiye mukullin hannunta da yake da ta buɗe ƙofar da shi ta shiga, tana ajiyewa a zuciyarta ta ce
'Da zafi-zadi ake dukan ƙarfe, kuma da sanyin safiya ake kama fara, ba zan tsaya kallon ruwa kwaɗo ya mini ƙafa ba, in dai zaman kishi ne ni babu macen da za ta iya gagarawa da ni domin sai na mata kishi da kissa ƴar ƙasa yadda sai ta ji tsanar gidan mijin da kanta don sai na takurawa kishiya" Ta faɗa tare da buɗe drower Sadiya ta shiga bincike kayan kawai take watsowa ƙasa amma bata ga abin da take nema ba. Haka ta gama bincikenta ta mayar da su yadda suke tamksr bata taɓa su ba domin ta iya takunta.
Haka ta gama dubawa amma bata ga abin da take nema ba, ranta sai wuya yake saboda ta san tabbas yau wata dama ce da ta samu wacce ba lallai ta same ta ba. Ƙarƙashin gado ta shiga dubawa amma bata gani ba, tsaye ta tashi ta tsaya rana riƙe da tsantsa ta damƙe fatar bakinta da haƙorinta na sama. Duk cikin wani abu da take gani za a ɓiye abin da take nema ta duba amma bata gani ba, gadon ta taka ta duba saman drower nan ma babu sai da ta sakko ta lura da ƙaramar lokkar jikin bed side drower da sauri ta jufi can ta buɗe sama da ƙasa amma babu. Kasancewar biyu ne sai ta koma ɗaya gefen ta buɗe ta saman sai ta ga panties ɗin Kakifa ne a ciki wanda suke a laye, tsaki ta yi ta tuƙunɗuna su ta tura ta rufe lokar, tana janyo ta saman sai ta ga wata ƙaramar jaka pose taɓa jakar ta yi ai kuwa ta ji ɗan tudu da sauri
ta fito da jakar tana fatan a dace tana buɗewa kuwa ta ga abin da take nema wani murmushi mai bayyana haƙora ta yi ganin kuɗaɗen a ciki a laye suke kasancewar pose ɗin tana da ɗan girma, ƴan dubu dubu ne a laye sai ƴan ɗari biyar biyar sai ɗari bibiyu da ƴan ɗari ɗari. Ganin kuɗin cunkus sai abun ya bata mamaki a ƙiyasce tana tunanin kuɗin nan zai iya kusan kaiwa dubu ɗari. Fito dansu ta yi duka ta zige zip ɗin ta buɗe ɗaya gefen sai ta ga ƴan hamsin hamsin ne da sauran canjuna a ciki su kuma dai ba su fi dubu biyar ba fito dansu ta yi duka a fili ta furta
"Wai dama sana,ar cikin gida tana kawo kuɗi har haka? Lallai wannan ake cewa bar ganin ka tara ka kiyayi mai nema ashe har tana samun rufin asiri a sana,arta haka lallai na yi sake!" Ƙaran bugun ƙofar gida ne ya ankarar da ita vata san lokacin da ta tashi tsaye daga zaunen da take ba, ga kuɗin duk ta baza haka ta shiga haɗa su tana karkarwar jiki don ta san asirin ta zai iya tonuwa tunanin ta ma Sadiya ce ta dawo duba mukullin da ta jefar. Lokar ta mayar ta rufe ta naɗo ƙasan rigarta da ta zuba duka kuɗin sai da ta zo faon a guje sannan ta tuna da mukullin da suri ta juya ta ɗakko har lokacin tana ji an bugawa fitowa ta yi amma bata rufa ɗakin ba ta ce
"A nan ne? Waye?" Ta faÉ—a tana jiran jin muryar Sadiya kawai sai ta ji muryar wata yarinya ta ce
" Mango da zoɓo za a bani" Wani uban tsaki ta ja ta ce
"A kan wani mango za ki zo ki damu jama,a to an dajna siyar da mango da zoɓo a nan" Yarinyar ta ce
"To akwai pure water?"
Meenal ta ce
"Babu pure water sai ubanki" ,Ta faÉ—a a zuciye yarinyar ta ce
"Na gane ki ba anty Sadiya ba ce kishiyarta ce ƴar baƙin ciki wataƙila antyn bata nan" Tana faɗar hakan ta ɗauki dutsi ta buga a ƙofar da ƙarfi ta zuga da gudu, Meenal tana so ta zo ta buɗe ƙofar ta kikkifawa yarinyar mari amma kuma abin da take yi ya fi wancan. Ɗakin ta koma ta ɗakko jakar ta rufe lokar ta tsaya ta tabbatar da komai yana yadda yake ta fito ta zo ta kulle ɗakin. Ɗakinta ta nufa da sauri ta je ta juye kuɗin a jakarta ta fito da pose ɗin a hannunta kicin ta je ta ɗakko ashana ta xo ta kyarta ta sakana jikin pose ɗin ganin jakar ta kama ta sheƙe da dariyar mugunta, sai da ta ƙone ƙurmus ta tattara ta kwshe ta je ta yi fuloshin ɗinsa a toilet.
Mukullan ta ɗakko ta zo wajen zaure ta jefar da su a ƙasa ta koma ta kwanta a bedroom ɗinta tana lissafa kuɗaɗen da ba da guminta ba ta samu tana jin daɗinsu.
A fili ta ce