← Book details Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 106

Sashe 74

Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ko da ta kawo musu sugar suka sha kunun Aliya ta ce tafiya za ta yi Jidda ta saka direba ya kaita gidan, tun da ta san Jidda ta ji Kasim ya kira ya kusa dawowa sannan kuma tun da bata faɗawa Kasim ta fita ba duk da ta san idan ma ya san ta fita ɗin ba wani abu zai mata ba amma kuma dai tun da lallaɓawa take ta samu cikar burinta za ta daure ta kuma cije!.

Ta haɗa mata sha tara ta arziƙi tana cewa sai ta kawo mata nata wunin, ko da ta rako ta bakin motar bayan ta saka dogon hijabia sai Aliya ta ƙame a gefe ta ce direba ya fito daga mazaunin direna ya buɗe mata haka ya fito ya buɗe ta shiga ya rufe wani daɗi take ji lalai mulkar wani akwai daɗi dole ta baza iko iya iko idan ta karɓi ragamar gidan Ibrahim. Da suka zo wucea mai gadi ya buɗe musu get sai da ta buɗe glass ta wurga masa uwar harara.

Ana kiran magriba direba ya kaita ƙofar gidanta ya buɗe mata ta fito tana wani shan ƙamshi tana riƙe da ledar da Jidda ta bata wanda bata ma san mene ne a ciki ba sai kuma jakarta, tana jin ranta fari ƙal don ta yi aikin da ya kaita gidan.

Tana shiga suka ringa waya da Amatullahi suna ta murna Amatullahi har da guɗa Aliya za ta zama matar manya, sai dai kuma sai ta ji tana baƙincikin cewa Aliya ta yi aure ta barta a gida sannan yanzu za ta ƙara yin wani auren ta shiga gidan arziƙi ita tana nan samarin kullum ta ce su fito sai su fita da gudu.

A gidan Ibrahim yana shigowa gidan shi ma ana kiran magriba alwala ya yi ya wuce masalaci, lokacin da ya dawo suka haura sama ya ce Jidda ta zuba masa abincin haja ta zuba masa yana cewa

"Idan na cinye sai kin ƙara mini domin kin san ina son tuwo" Dariya ta yi ta ce

"Ai idan ka cinye na fulas ɗin ma sai a ƙaro maka a kicin" Dariya ya yi ya ce

"Mai kika sanya mini idan na cinye?"
Tana kallonsa ido cikin ido ta ce

"Mai kake so in sanya maka kuÉ—i ko mota?"
Ɗan ɓata rai ya yi ya ce

"Kuɗi abin so ne, saboda da su ne ake abubuwa na rayuwar yau da kullum, mota kuma wani abu ne na ƙawa a duniya sai dai ba dole sai da ita ake rayuwa ba, kamata ya yi ki saka mini abu mai muhimmancin da ya fi wannan" Da alamar mamaki take kallonsa ta ce

"Kamar me?" Kafe ta ya yi da idanunsa wanda take jin suna yawo a duka jikinta tamkar yadda jinin jikinta yake zagayawa a cikin jijiyoyinta ya ce

"Jiddarh,?" Ta ce

"Na'am"

Ya ce
"Kamata ya yi ki bani kyautar kanki ina nufin ki saka mini kanki a cin abincin nan sai na fi ci da yawan da zan baki mamaki" Wani murmushi ne ya ƙwace mata wanda bata yi zato ko tsammani ba ta ce

",Banda abinka ni dama ai taka ce"

Hanunsa biyu ya miƙa ya tallafo gefen fuskarta ya ce

"Na sani Jidda dama ke tawa ce amma ki ce za ki rayuwa da ni za ki kasance da ni rayuwa ta har abada, za ki zauna da ni a runtsi da duk wuya, duk halin da na tsinci kaina ba za ki taɓa guje min ba Jidda, da ke nake rayuwa kr ce sanyin idaniyata na faɗawa Mummy ke ar aljanna ce Jidda na faɗa mata in har miji ne yake ɗaga ƙafa matarsa ta shiga aljanna Jidda ki saka kanki cikin sahun matan aljanna, aljannar ma firdausi" Ƙwalla ce ta taru a idanunta kafin ta cika idanun sai kawainta gangaro saman kumatunta da sauri ya saka manyan yatsunsa ya goge hawayen don ba ya son ganin kukan Jidda.
Muryarsa ce t bayyana cikin rauni ya ce
"Mai ya sa kike kuka Jidda? Wallahi ba na son zubar hawayenki" ,Ƙasa ta yi da idanunta don ta ga damuwa ƙarara a fuskarsa sannan idanunsa sun yi ja, tana ta tunanjn duk da ana cewa a farkon aure ana bada kulawa da nuna damuwa sai tafiya ta yi tafiya zama ya yi zama sannan zaman ya koma zaman haƙuri amma gaskiya a yadda Ibrahim yake nuna mata soyayya da kulawa bata jin har iya numfashin sa zai canja mata.

Muryarta tana rawa ta ce

"Na ji kana min kalamai ne wanda suke nuna kamar kana mini ban kwana ne tamkar dai kalamai ne masu alamta kana mini sallama sai dai ban san wace irin sallama ba ce"

Murmushi ya yi don kauda damuwar fuskarta wacce har ta sa ta zubar masa da hawayenta ya ce

"Kawai dai ina nuna miki girma da muhimmancin Jidda a rayuwar Ibrahim ne" ÆŠagowa ta yi ta kalle shi ya gyaÉ—a mata kai alamar gaskata maganar.
Idanunta ta juya ta ce

"Muhimmancinka a zuciyar Jidda tamkar alaƙar gangar jiki da numfashi ne, idan aka cire rai a jikin gangar jiki to gangar jiki ta zama gawa ba za ta amfanu ba sai cikin ƙasa wato kabari haka kake da girma a zuciyar Jidda" Yana kallonta shi ma ya ce

"Allah ya dawwamar da soyayya da ƙaunar junana har abada ina fatan na riga ki barin wannan duniyar domin idan kika fara tafiya Allah ya sani ni dai rayuwata za ta tagayyara ne"

Jidda ta ce

"Ni ma hakan take" Hannuwansa ya É—auke daga fuskarta ya mayar wuyanta tare da kai fuskarsa ya É—ora goshinsa a kan tana goshin hancinsa yana kan nata hancin ya ce

"Tare za mu rayu kuma tare za mu mutu, don sanarwar mutuwar ɗayanmu shi zai sa zuciyar ɗayar ta buga shi ma a take ya bi ɗan uwansa sai a sakamu a kabari ɗaya" Su duka suka ƙyalƙyale da dariya don wannan ne buri da fatansu kar ɗaya ya mutu ya bar ɗaya baka jin komai a ɗakin sai sautin dariyar su sannan ya koma ya zauna.

Plate É—in ta tura masa gabansa ya É—auki cokalin yana gyara zamansa, gutsiro tuwon ya yi a cokalin ya ya saka miya tare d ambaton

"Bismillah" Nufar bakinsa ya yi da tuwon sai dai ƙaran wayarsa ya katse masa Jidda da wayar take kusa da ita ta furta

"Mummy ce take kira" Ta faɗa tana ɗakko wayar ta miƙa masa. Da hannun hagu ya karɓi wayar hannunsa na dama yana riƙe da tuwon a cokalin, ya danna ok tarw da kai wayar kunnensa.

Kukan Mummy ne ya saka ya saki cokalin hannunsa tare da tashi tsaye yana faÉ—in

"Mummy lafiya?" Jidda ma tsaye ta tashi gabanta yana faÉ—uwa ganin hankalinsa ya tashi...

*Na muku promo na kayan maganin mata a zo a mini ciniki* 💃💃💃💃💃

*🎉 PROMO NA ƘARSHEN SHEKARA GA MATA! 🎉*
*Ki bar tsohon shekara da matsala, ki shiga sabuwa da gyara!*

Mun yi sabbin kaya don nuna soyayya da kulawa ga wanda suke son mallakar É—aya daga cikin waÉ—annn abubuwan ko kuma duka.
*Ga kayanmu masu inganci da kike bukata:*

1️⃣ *Maganin Matsi Gam-Gam* Don matsi 1500 maimakon 2500
2️⃣ *Maganin Sanyi* Yana kawar da dukkan nau’in infection da wari, ƙaiƙayi, ƙuraje rikicewar al,ada 2500 maimakon 4k.
3️⃣ *Sabaya 3 in 1* Gyara breast, hips sannan tana gyara jiki 5k maimakon 7k.
4️⃣ *Maganin Gyaran Breast* Yana ciko da breast, ga masu shirin yin yaye da kuma wanda breast nasu yake buƙatar gyara 3k maimakon 4500.
5️⃣ *Daka* Tushen ni’ima 1500 maimakon 2500.

🎁 PROMO NA MUSAMMA
Ranar ƙarshe 31 ga Disamba, 2025

Ki gyara jikinki, ki faranta ran mijinki, ki shiga sabuwar shekara da armashi.

09025576222

https://chat.whatsapp.com/DDmSp3AUB7gJnJQLnau59V?mode=hqrt1

*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)

NA

MAMAN AFRAH

. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*

BOOK 1

PAGE 2️⃣3️⃣

SADIYA

Ta jima abin yana bata mamaki sai dai bata san wa za ta faɗawa ba ma tun da abu ne da vai taɓa faruwa da ita ba. Ta so ta tambayi Meenal mai ya sa ita akwai nepa a ɓangarenta ita kuma babu sai dai gudun abin da zai je ya zo ko kuma a bata amsar da za ta mata ciwo sai ta ja bakinta ta tsuke. Meenal kuma dama ta yi hakan ne don ta turawa Sadiya haushi amma abin mamakin sai ya ga bata ga ko alamar damuwa a fuskar Sadiyar ba bare ta kai ga furtawa hakan ya sa ranta ma ya ɓaci ta taso a fusace lokacin Sadiya ta fito ta ɗaurawa wata maƙocoyarsu curry da ta saya curryn nan mai kyau da kala ga ƙamshi wanda ta auna wajen maman afrah, hakan ya sa Meenal faɗin

"Sadiya wai ni ke wace irin ishashshiya da mai ce? Wato saboda girman kai da nuna ɗagawa ke ba jinin sarauta ba amma shi ne koke zaune ɓangarenki babu wuta ko ki tambaya tun da ni ai gashi nan kina jin ƙaran TV a ɓangarena" Ta faɗa tana jifan cikin jikin Sadiya da wani mugun kallo. Matar ta lura da kallon tsanar da Meenal take jifan Sadiya da shi hakan ya sa ta jinjina al,amarin amma sai ta g Sadiya ta yi murmushi irin murmushin nan da ake kira da sa kishiya haushi, ta ce

"To ai na ga ba zaman kaina nake yi ba zaman aure nake, sannan ke ɗinma zaman auren kike ni da ke babu wanda yake zaune a ƙarƙashin wani, don haka nake jiran shi wanda shi ne ginshinƙin gidan sai in ji ta bakinsa" Kallon ashe ke ma dai kin yj baki Mrenal ta mata kafin ta taɓe baki ta ce

"To shiknan zan nuna miki ni nake iko da mijin da kike taƙamar kina zamansa kuma zan nuna miki ni ƴar halak ce matsawar kina son ci gaba da neman taro da sisi da firjinki dole ki biyo ta hannuna ko ki dawwama babu nepa a ɓangarenki" Tana faɗar hakan ta juya fuuuu rai a ɓace, sai matar nan ta ce
Chapter 74 · 0% Book details