Sashe 71
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ta kammala komai Saude tana taimaka mata da miƙa mata abin da ta buƙata na amfani. Bayan sun gama ta ɗora masa a kan dinning ta ɗakko plate da cokali ta ajiye da saving spoon ta bar Saude tana gyara kicin ɗin tare da wanke abubuwan da suka ɓata. Aliya ta ce a ƙoshr take ba za ta ci tuwon ba tun da basu daɗe da cin abincin ba, ranta dai fari ƙal tana murna don ta je ɗakko ruwa a frige ta hangi cokalin da aka ajiye masa sak wanda aka mata magani a jiki kenan ko ta sauya ba za a gane ba.
Hatta Jidda sai da ta fahimci Aliya tana cikin farinciki.
Lokacin da ya dawo Aliya ta gaishe shi ya amsa cikin sakin fuska har yana tambayar Aliya mai gidan nata, ba komai ya sa ta saki fuska ba sai Jidda da ta masa magana ranar nan ta ce bata ji daɗin yadda ya amsawa ƴarnuwarta gaisuwa a daƙile ba, hakan ya sa ya karɓi kuskurensa shi kuma kawai ra,ayin Aliya ne ba ya yi.
Sai da ya yi wanka ya shirya da kayan da ta fitar masa sannan ya ce ta zo ta É—akko masa abincin a sama zai ci, a daidai lokacin Aliya kuma ta fito da cokalin tana shirin zuwa ta sauya sai kawai ta ga Jidda kamar an jefo ta hakan ya sa ta wayince bata sanin bata taki sa,a ba sai da ta ga Jidda ta É—auki kwanon miya da plate mai É—auke da cokolan ta haura sama da su.
Har sai da ta yi ƙwallah don takaici, jim kaɗai sai ga Jidda ta sakko tana cewa bari ta watsa ruwa tana sanar da ita yanzu za ta fito sai ta fito ma za ta zubawa Ibrahim abinci hakan yana nuni da ba za ta daɗe a banɗakin ba. A can sama kuma bayan ta kai masa abincin sai ta samu ya buɗe system yana ɗan wani abu hakan ya sa ya ce kar ta zuba abincin bari ya ɗan kammala sai ta ce za ta sauka ta watsa ruwa sannan ya gama sai ta zo ta zuba masa. Aliya tana zaune jugum abin duniya ya haɗe mata goma da ashirin sai kawai ta hangi Ibrahim ya sakko da waya a kare a kunnensa yana cewa
"Wallahi na manta shi gani yanzu zan duba amma dai kamar na taho da shi daga office, yana buɗe ƙofa ya fita Aliya ta tsam ta tashi tsaye gabanta yana tsananta faɗuwa da sauri ta yi hanyar bedroom ɗin da Jidda ta shiga ta je ta kara kunne a jikin ƙkfar ɗakin tana iya jiyo ƙaran ruwan da take wankan, da sassafa ta fara haura saman tana haɗa matakala biyu, don ta saka a ranta sai ta sauya cokalin nan a yau!
Idan kuna comment tabbas za a ke posting a kan lokaci amma ku ci gaba da karantawa wasu suna yi wasu suna yin ɗifffff ni ma sai in ke ɗiɗifffff😃
MAMAN AFRAH
. 09025576222
https://chat.whatsapp.com/DsxFGh957C5EvfrSjJDdgO?mode=wwt
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 2ï¸âƒ£2ï¸âƒ£
ALIYA
Da tsananin faɗuwar gaba ta ƙarasa hawa saman benen ko fargabar ɗaya daga cikinsu bata yi ya zo ya ganta. Sai da ta gama hawa ta je ta rasa ma wace ƙofa ce za ta buɗe inda za ta ga inda aka ajiye abincin ta canja cokalin tana rarraba ido duk ta rikice burinta kawai ta aikata abin da fa kawo ta sai dai bata san ya za ya yi abin ya tabbata ba tare da wata matsala ta biyo bayan hakan ba.
A hanzarce ta yi hanyar ƙofar ɗaya ta tura ta shige saboda ƙarfin hali har da karo ƙofar sai dai kash sai bayan ta shiga ta gane ba ɗakin da take nema ba ne don babu alamar wani abinci a ɗakin.Da sauri ta fito tana ta tunanin rashin nuysuwar da take da shi wanda ya sa bata gane inda za ta shiga ba sai dai ta san dama ba za ta samu nutsuwa ba saboda kawai tunaninta ya ta,allaƙa ne ga samun cikar burinta wato canja cokalin ne kawai a gabanta wanda take tunanin daga shi burinta na duniya ya cika.
Ɗaya ƙofar ta tura a nan ne wani farinciki ya baibaye zuciyarte, domin tana buɗewa ta yi arba da system da kayan abincin da Jidda ta kai sannan uwa uba cokalin da yake kan plate ɗin tabbas shi ne dai wanda bokanyan ta yi aiki a kansa, wani daɗi ne ya ziyarci zuciyar Aliya maimakon ma ta yi abin da ya kaita sai ta tsaya ta ƙarea ɗakin kallo tana ƙiyasta nan da wasu kwanaki da basu taka kara sun karya ba ɗakin zai zama ya dawo ƙarƙashinta wato ita take iko da shi.
Ƙarasawa ta yi ta tsugunna a gaban plate ɗin ta saka hannu ta ɗauke cokalin kan plate ɗin ta ɗora na hannunta wanda ta zo da shi, sannan sai ta ɗaga bra ɗinta ta saka wanda ta ɗauke wancan ɗin. Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke ta samun nasara.
Baki ta taɓe tana tashi tsaye har hango ta take yi tana zuba ƙasaita sai motar da ta ga dama kuma ta yi ra,ayi za a ta shiga hatta dangi da ƴan uwan Ibrahim ɗin ma kansa sai sun dawo ƙarƙashinta. Dama Abba ne matsalarta to gashi an ce aikin da aka yi mai gabaɗaya ne wato kowa da kowa.
A zuciyarta ta ce
"Uhmm Aliya rufawa kanki asiri ki koma ƙasa ki zauna ki naɗe ƙafa kamar baki motsa daga wajen ba, tun da dai Allah ya ida nufi kin canja cokalin' Ta faɗa tana zuwa ta miƙa hannu za ta buɗe ƙofar, kamar abin almara kawai sai ta fara jiyo ƙaran takun takalmi alamar ana hayowa saman, idanu ta zaro ƙirjinta yana fatfat waiga bayanta ta yi tana jin faɗuwar gabanta yana tsananta a take ta shiga tunanin waye a cikinsu yake ƙoƙarin hayowa saman shin Jidda ce ko kuma shi mai gabaɗayan ne wato Ibrahim.
A fili kuma a hankali ta furta
"Na shiga uku asirina yana dab da tonuwa" Ta faɗa tana haɗiye wani yawu muƙut.
Tunani ta fara shin idan Ibrahim ne ya same ta a ɗakin nan wane zargi zai yi mata da wane idon ma za ta kalle shi ko da a ce a saman ya same ta ba ma a ɗakin ba mai ya kaita ɗakinsa a lokacin da shi da Jidda basa wajen. A gefe ɗaya tana tunanin idan Jiddar ce kuma fa? Wace amsa za ta bata shin mai Jidda za ta ɗauka dangane da sauya akalar tsanarta zuwa tsantsar ƙaunar ƙarya da suka yi don kawai ta auri mai dukiya, tabbas ta san duk wanda ya yi ido huɗu da ita yanzu to haƙiƙa sai ya mata kallon tuhuma domin gabaɗaya alamomin rashin gaskiya sun bayyana ƙiri-ƙiri a tare da ita.
Jin takun yana matsowa dab alama ce ta mai hayowar ya kusa ƙare tako matakalar da sauri ta koma ta shiga waige waige tana son gano inda za ta ɓuya ta gwammace ta kwana a ɓoye idan har hakan zai yiwu a kan a ganta zargi marar adadi ya hau kanta!.
Abin da yake kai kawo aranta shi ne idan kuma Jidda ce dole ai za ta ga bata falon sannan komanta tana falon ita cw bata nan mai za ta ce mata kai abin ya haɗe mata goma da ashirin. Amma hakan ba zai sanya ta karaya ba don cikar burinra da na Ummarta ya fi komai a halin yanzu. Kaf ɗakin bata ga wajen da za ta ɓoye ba tare da an ganta ba hakan ya sa ta yi wajen drower za ta shiga tsakanin drower da bango ta takure ko Allah zai tseratar da ita kar a ganta, sai daj tana zuwa ta ga wajen ya yi mata kaɗan ta shige domin dole za a hango ta a kiɗime ta fito ganin babu mafaka sannan sirinta yana dab da tonuwa sai kawai ta buɗe ƙofar banɗaki ta shige tana shiga ta mayar da ƙofar ta rufe. Jikinta har karkarwa yake da ta ji an turo ƙofar ɗaki ta shiga fargabar sa sai take jin tamkar ko numfashi ta yi sai an ji.
A ɗarare ta samu wata tula a jikin ƙofar ta leƙa taakar ɗakin gabanta ya bada sautin dimmmm ganin Ibrahim ne ya shiga a nan ta tabbatar kashin ta ya bushe domin ta san tun da ya dawo ɗakin dole Jidda ma ta yi wa ɗakin kutse. Yana shigowa ya ajiye wayoyinsa a kan gadon ya hau cire rigar jikinsa a take Aliya ta yi wa idanunta masauki a kan kyakkyawar lallausar fatarsa kasancwar ya bata baya nw yana juyowa sai da ta kusa zaucewa ganin kyakkyawan gargasa shimfiɗe a faffaɗan ƙirjinsa ya kwanta lifet kallon tsari na kyawun halittar da Allah ya masa kawai take a take ta sauke wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sauke tana tunanin lallai Jidda ta more da samun kyakkyawa kuma nagartaccen miji kowacce mace ta samu miji irin wannan tana ganin a duniya an sallame ta ta wannn ɓangaren.
Gaban ta ne ya buga da ƙarfi da ta yi wani tunani cewa ko dai wanka zai yi a take ta ji shagalar da ta yi da kallon nasa tana yaba kyawunsa ta ji ya ɓace mata yawun bakinta ya ƙafa ta ji bakin ya bushe. Jikinta ne shiga karkarwa tana hangowa cewa idan ya buɗe banɗakin ya same ta ya za ta yi tana cikin wannan tunanin sai ta ga ya juya ya nufi wajen drower ya buɗe ya ɗakko wasu kayan ƙanana ya saka coffe ɗin wando da wata farar riga mai hoton damisa coffe a jiki a hanzarce ya ɗauki wayoyinsa tana jin yana waya ya buɗe ƙofar ya fita.
Hatta Jidda sai da ta fahimci Aliya tana cikin farinciki.
Lokacin da ya dawo Aliya ta gaishe shi ya amsa cikin sakin fuska har yana tambayar Aliya mai gidan nata, ba komai ya sa ta saki fuska ba sai Jidda da ta masa magana ranar nan ta ce bata ji daɗin yadda ya amsawa ƴarnuwarta gaisuwa a daƙile ba, hakan ya sa ya karɓi kuskurensa shi kuma kawai ra,ayin Aliya ne ba ya yi.
Sai da ya yi wanka ya shirya da kayan da ta fitar masa sannan ya ce ta zo ta É—akko masa abincin a sama zai ci, a daidai lokacin Aliya kuma ta fito da cokalin tana shirin zuwa ta sauya sai kawai ta ga Jidda kamar an jefo ta hakan ya sa ta wayince bata sanin bata taki sa,a ba sai da ta ga Jidda ta É—auki kwanon miya da plate mai É—auke da cokolan ta haura sama da su.
Har sai da ta yi ƙwallah don takaici, jim kaɗai sai ga Jidda ta sakko tana cewa bari ta watsa ruwa tana sanar da ita yanzu za ta fito sai ta fito ma za ta zubawa Ibrahim abinci hakan yana nuni da ba za ta daɗe a banɗakin ba. A can sama kuma bayan ta kai masa abincin sai ta samu ya buɗe system yana ɗan wani abu hakan ya sa ya ce kar ta zuba abincin bari ya ɗan kammala sai ta ce za ta sauka ta watsa ruwa sannan ya gama sai ta zo ta zuba masa. Aliya tana zaune jugum abin duniya ya haɗe mata goma da ashirin sai kawai ta hangi Ibrahim ya sakko da waya a kare a kunnensa yana cewa
"Wallahi na manta shi gani yanzu zan duba amma dai kamar na taho da shi daga office, yana buɗe ƙofa ya fita Aliya ta tsam ta tashi tsaye gabanta yana tsananta faɗuwa da sauri ta yi hanyar bedroom ɗin da Jidda ta shiga ta je ta kara kunne a jikin ƙkfar ɗakin tana iya jiyo ƙaran ruwan da take wankan, da sassafa ta fara haura saman tana haɗa matakala biyu, don ta saka a ranta sai ta sauya cokalin nan a yau!
Idan kuna comment tabbas za a ke posting a kan lokaci amma ku ci gaba da karantawa wasu suna yi wasu suna yin ɗifffff ni ma sai in ke ɗiɗifffff😃
MAMAN AFRAH
. 09025576222
https://chat.whatsapp.com/DsxFGh957C5EvfrSjJDdgO?mode=wwt
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 2ï¸âƒ£2ï¸âƒ£
ALIYA
Da tsananin faɗuwar gaba ta ƙarasa hawa saman benen ko fargabar ɗaya daga cikinsu bata yi ya zo ya ganta. Sai da ta gama hawa ta je ta rasa ma wace ƙofa ce za ta buɗe inda za ta ga inda aka ajiye abincin ta canja cokalin tana rarraba ido duk ta rikice burinta kawai ta aikata abin da fa kawo ta sai dai bata san ya za ya yi abin ya tabbata ba tare da wata matsala ta biyo bayan hakan ba.
A hanzarce ta yi hanyar ƙofar ɗaya ta tura ta shige saboda ƙarfin hali har da karo ƙofar sai dai kash sai bayan ta shiga ta gane ba ɗakin da take nema ba ne don babu alamar wani abinci a ɗakin.Da sauri ta fito tana ta tunanin rashin nuysuwar da take da shi wanda ya sa bata gane inda za ta shiga ba sai dai ta san dama ba za ta samu nutsuwa ba saboda kawai tunaninta ya ta,allaƙa ne ga samun cikar burinta wato canja cokalin ne kawai a gabanta wanda take tunanin daga shi burinta na duniya ya cika.
Ɗaya ƙofar ta tura a nan ne wani farinciki ya baibaye zuciyarte, domin tana buɗewa ta yi arba da system da kayan abincin da Jidda ta kai sannan uwa uba cokalin da yake kan plate ɗin tabbas shi ne dai wanda bokanyan ta yi aiki a kansa, wani daɗi ne ya ziyarci zuciyar Aliya maimakon ma ta yi abin da ya kaita sai ta tsaya ta ƙarea ɗakin kallo tana ƙiyasta nan da wasu kwanaki da basu taka kara sun karya ba ɗakin zai zama ya dawo ƙarƙashinta wato ita take iko da shi.
Ƙarasawa ta yi ta tsugunna a gaban plate ɗin ta saka hannu ta ɗauke cokalin kan plate ɗin ta ɗora na hannunta wanda ta zo da shi, sannan sai ta ɗaga bra ɗinta ta saka wanda ta ɗauke wancan ɗin. Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke ta samun nasara.
Baki ta taɓe tana tashi tsaye har hango ta take yi tana zuba ƙasaita sai motar da ta ga dama kuma ta yi ra,ayi za a ta shiga hatta dangi da ƴan uwan Ibrahim ɗin ma kansa sai sun dawo ƙarƙashinta. Dama Abba ne matsalarta to gashi an ce aikin da aka yi mai gabaɗaya ne wato kowa da kowa.
A zuciyarta ta ce
"Uhmm Aliya rufawa kanki asiri ki koma ƙasa ki zauna ki naɗe ƙafa kamar baki motsa daga wajen ba, tun da dai Allah ya ida nufi kin canja cokalin' Ta faɗa tana zuwa ta miƙa hannu za ta buɗe ƙofar, kamar abin almara kawai sai ta fara jiyo ƙaran takun takalmi alamar ana hayowa saman, idanu ta zaro ƙirjinta yana fatfat waiga bayanta ta yi tana jin faɗuwar gabanta yana tsananta a take ta shiga tunanin waye a cikinsu yake ƙoƙarin hayowa saman shin Jidda ce ko kuma shi mai gabaɗayan ne wato Ibrahim.
A fili kuma a hankali ta furta
"Na shiga uku asirina yana dab da tonuwa" Ta faɗa tana haɗiye wani yawu muƙut.
Tunani ta fara shin idan Ibrahim ne ya same ta a ɗakin nan wane zargi zai yi mata da wane idon ma za ta kalle shi ko da a ce a saman ya same ta ba ma a ɗakin ba mai ya kaita ɗakinsa a lokacin da shi da Jidda basa wajen. A gefe ɗaya tana tunanin idan Jiddar ce kuma fa? Wace amsa za ta bata shin mai Jidda za ta ɗauka dangane da sauya akalar tsanarta zuwa tsantsar ƙaunar ƙarya da suka yi don kawai ta auri mai dukiya, tabbas ta san duk wanda ya yi ido huɗu da ita yanzu to haƙiƙa sai ya mata kallon tuhuma domin gabaɗaya alamomin rashin gaskiya sun bayyana ƙiri-ƙiri a tare da ita.
Jin takun yana matsowa dab alama ce ta mai hayowar ya kusa ƙare tako matakalar da sauri ta koma ta shiga waige waige tana son gano inda za ta ɓuya ta gwammace ta kwana a ɓoye idan har hakan zai yiwu a kan a ganta zargi marar adadi ya hau kanta!.
Abin da yake kai kawo aranta shi ne idan kuma Jidda ce dole ai za ta ga bata falon sannan komanta tana falon ita cw bata nan mai za ta ce mata kai abin ya haɗe mata goma da ashirin. Amma hakan ba zai sanya ta karaya ba don cikar burinra da na Ummarta ya fi komai a halin yanzu. Kaf ɗakin bata ga wajen da za ta ɓoye ba tare da an ganta ba hakan ya sa ta yi wajen drower za ta shiga tsakanin drower da bango ta takure ko Allah zai tseratar da ita kar a ganta, sai daj tana zuwa ta ga wajen ya yi mata kaɗan ta shige domin dole za a hango ta a kiɗime ta fito ganin babu mafaka sannan sirinta yana dab da tonuwa sai kawai ta buɗe ƙofar banɗaki ta shige tana shiga ta mayar da ƙofar ta rufe. Jikinta har karkarwa yake da ta ji an turo ƙofar ɗaki ta shiga fargabar sa sai take jin tamkar ko numfashi ta yi sai an ji.
A ɗarare ta samu wata tula a jikin ƙofar ta leƙa taakar ɗakin gabanta ya bada sautin dimmmm ganin Ibrahim ne ya shiga a nan ta tabbatar kashin ta ya bushe domin ta san tun da ya dawo ɗakin dole Jidda ma ta yi wa ɗakin kutse. Yana shigowa ya ajiye wayoyinsa a kan gadon ya hau cire rigar jikinsa a take Aliya ta yi wa idanunta masauki a kan kyakkyawar lallausar fatarsa kasancwar ya bata baya nw yana juyowa sai da ta kusa zaucewa ganin kyakkyawan gargasa shimfiɗe a faffaɗan ƙirjinsa ya kwanta lifet kallon tsari na kyawun halittar da Allah ya masa kawai take a take ta sauke wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sauke tana tunanin lallai Jidda ta more da samun kyakkyawa kuma nagartaccen miji kowacce mace ta samu miji irin wannan tana ganin a duniya an sallame ta ta wannn ɓangaren.
Gaban ta ne ya buga da ƙarfi da ta yi wani tunani cewa ko dai wanka zai yi a take ta ji shagalar da ta yi da kallon nasa tana yaba kyawunsa ta ji ya ɓace mata yawun bakinta ya ƙafa ta ji bakin ya bushe. Jikinta ne shiga karkarwa tana hangowa cewa idan ya buɗe banɗakin ya same ta ya za ta yi tana cikin wannan tunanin sai ta ga ya juya ya nufi wajen drower ya buɗe ya ɗakko wasu kayan ƙanana ya saka coffe ɗin wando da wata farar riga mai hoton damisa coffe a jiki a hanzarce ya ɗauki wayoyinsa tana jin yana waya ya buɗe ƙofar ya fita.