Sashe 51
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Napep ta samu ta tsare suka kama hanyar gidan. A can gidan kuwa Umma lokacin da ta ƙule a ɗaki tana dokawa Aliya kira tana so ta bata baki, bayan Abba ya fita amma kuma sai ta ji an katse wayar a ƙarshe ma ta ji wayar a kashe. Fitowa tsakar gidan ta yi duk baƙi an karya wato an ci abinci, wasu suna hira wasu kuma suna wankan yaransu don suna cewa tafiya za su yi yau.
Wata daga ciki ta c
"Lubabatu an aurar da Æ´aÆ´a yau an yi bacci fa munshari kowace ta shiga É—akinta lafiya" Umma ta ce
"Wallahi kuwa, ai mun yi waya ma da su ɗazu, ai kam duk wanda ya kai ƴa mace ɗakin miji kam dole ya yi bacci da munshari, saboda fargabar tarbiyar ƴa mace duk da cewa duk tarbiya ɗaya daga ta yarinya mace har ta yaro namij" Nan aka shiga yin hira ana ta yaba gidan Jidda wanda hakan yake haifarwa da Umma wani ɓacin rai kamar ana soka mata ƙahon ƙarfe a zuciya. Tsayuwar napep a ƙofar gidan sai kuma shigowar wani yaro ƙarami yana cewa wai a ba mai adaidaita kuɗi, kafin su samu damar bashi amsar wanda ya aiko shi, kukan Aliya da ya fara ratsa kunnuwansu tamkar an yi mutuwar da ba a ɗauke gawa ba ya saka gabaɗaya idanun kowa ya koma can...
MAMAN AFRAH
*Ina manyan matan? Na buɗe muku adashe mai so ga link nan ya shiga grp, ko a min magana pc idan kin san ba yi za ki yi ba bana son harkar ɓata lokaci.*
*ABUBUWAN DA ZA A YI ADASHEN SU NE*
*Leshi, atamfa jaka, takami kayan yara, takalman, yara, abaya, mayafai na shago, mayafai beadwrk, adire, kamfala, shadda, shaddales sai kuma kayan kicin da zanin gado ga mai buƙata* .
*Amfanin yin adashen domin samun sauƙin siyan abu idan kana zuba kuɗin da kaɗan zai baka damar samun abin da kake so saɓanin za ka ga wahalar siye a dunƙule, Allah sa mu fara a sa,a mu gama cikin nasara.*
[11/13, 12:45 PM] ðŸ˜: https://chat.whatsapp.com/GTq4oSxwxZfLKU7Amx5My1?mode=wwt
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 1ï¸âƒ£7ï¸âƒ£
*ALIYA*
Gabaɗaya kowa baki sake hankali tashe yake binta da kallo, kowa da abih da ya fara rayawa a zuciyarsa, wasu suna raya cewa ko mijin ne ya mutu, wasu suna tunanin ko dai bata kai masa mutuncinta ba ne shi ya sa ya mata shegen duka a koro ta, saɓanin Umma da tuni ta harbo jirgin abin da ya maido da Aliyar gida. Umma a take ta ji wani abu yana juyata tabbas ta san yau Aliya ta gama kunce mata zani a kasuwa ta tona mata asiri ita da take son komai ya zama na sirri amma ta kwaso ƙafa ta taho gida tana ɓare baki kamar dai an sanar da ita mutuwar wani shaƙiƙi nata.
Umma tamkar ta saka kuka haka ta ji don ta fara tunanin yadda za ta ɓoye matsalar nan amma da alama matsalar ba za ta ɓoyu ba, tun da dai gashi nan ta yi wa kanta fallasa auren bashi. Salatin da matan suka kwasa shi ya dakatar da Umma daga saƙa da warwarar jin ana ta jerawa Aliya tambayar lafiya? Sai dai kukan Aliyar ya hana ta bada amsa hakan ya da zargin da yake ran kowanne ya ninku fiye da farko, maganar yaron nan ta sake katse musu zulumi da ya ce
"Wai mai adaidaita sahu ya cw a bashi kuɗin" Umma da wasu kuɗi suke gefenta ta ɗauki ɗari biyar ta cillawa yaron ya ɗauka ya fita da gudu, Aliya ƙarasawa kan baranda ta yi ta zauna zaman dirshan cike da kuka ta ce
"Wallahi Umma ba zan zauna da shi ba" Kowa sai ya matso don jin ba,asin maganar don furucin ta ya nuna ba ita ce da laifi ba kamar yadda zuciyoyinsu suka saƙa musu a farko, kowa sai ya buɗe kunne don jin dalilin.
Umma ji ta yi kamar ta dannewa Aliya baki don kar ta faɗa domin ta san muddin ta yi maganar to kuwa shuka za ta yi a idon makwarwa don kowa sai ya ji labarin matsalar gidan aurenta, sani ne Aliya bata yi ba yanzu zancen duniya iya faɗawa baba ne, wuyar ta ka yi furuci sai ya bazu wani ma sai ya gama ƙara gishiri da maggi a maganar don ta yi armashi idan zai bada labari.
Umma ta rasa ma mai za ta ce duk da tana ta ƙoƙari wajen ganin ta dakatar da Aliyar daga abin sa take son faɗa, amma Aliya duk yadda Umma ta kai ga mata magana da ido amma ko idanun Ummar ma bata kalla ba,ɗaya daga cikin matan ta ce
"Aliya dama auren ƙiyayya ne aka miki?
Kafin ta bata amsa wata daga cikinsu rai a ɓace ta ce
"Ko auren ƙiyayya ne a kan mai za akai ta gidan miji ta taho gida? Ko ma mene ne ba sai ta zauna a magance matsalar ba, amma ta kamo hanya ta dawo gida wannan ai tonon asiri ne kuma dole idanun mutane ya dawo kanta, tun da yanzu kiwon mutum ake yi ba dabba ba"
Aliya cike da muryar kuka ta ce
"Ba dole in taho gida ba, mutuminnda yake ɗauke da mugun abu" Salati akam kwasa Umma kuwa kai ta ɗauke gefe tana jin kamar ta tsinewa Aliya don takaici gashi bata son ta dakatar da ita su ce bata ɗauke su a matsayi iyayen Aliyar ba tun da daga dangin Abba sai kuma nata ƴan uwan. Wata ƴar uwar Abba da ta zo daga ƙauye tana dafe ƙirji ta ce
"Wayyo Allah, mun shiga uku Allah sa bai kwanta da ke ba Aliya" Matar ita tunaninta mugun abun da Aliya ta ce tana nufin cutar HIV ita kuma Aliya sai ta ji zuciyarta ta ƙara karaya sannan ta ji daɗina ranta a ƙalla ta san dai wannan babban batu da za a raba auren tun da ta ga ana batun bai yi tarayya da ita ba, tana murje idanu ta ce
"Wallahi ganin idanuna na ga wajen facin da aka masa, ba don na gani ba da ba zan taɓa yarda ba" Umma a ƙufule ta ce
"Facin ubanki Aliya, shegiya sai ka ce wata tayar mota za ki ce faci wallahi ki kiyayeni" Ta faÉ—a tana tashi tsaye tana gyara É—aurin zanin ta da yake barazanar barin jikinta, tana jin kunya kamar ta nutse don kunyatawa dai yau Aliya ta kunayata ta a bainar jama,a.
Baki aka hau ba Umma ana faÉ—in ta mata a hankali ai babbar magana ce ta sanyata baro gidanta, Aliya buÉ—ar bakinta sai ta c
"Kuma wallahi da na san mata-maza ne ba zan aure shi ba, wajen ɗinkin tabon nan ba zai taɓa ɓacewa ba har ya mutu, da shi zai koma kabarinsa, ni ba zan ma je in ke haihuwar mata maza ba" Wasu sun ɗauki abin da girma don suna tunanin a mata maza Kasim ɗin ya fi ƙarfi ne ta ɓangaren mace basu san ma namiji ba ne kawai tsanarsa ce ta ƙoƙon ran Aliya har take ganin za ta rabu da shi.
Umma ɗaki ta shige jin kamar za ta nutse don kunya, tsayuwar nape a ƙofar gidan da kuma sallamar Abba da ya yi kana ganinsa ka ga wanda hankalinsa yake a tashe shi ya dakatar da ɗaya daga cikin matan da take ba Aliya baki.
Abba wanda maƙocinsa ya kira shi a waya yana tambayarsa lafiya ya ga Aliya an sauke ta a a daidaita sahu tana kuka ta shiga gida. Nan Abban ya nuna masa bai san ma da dawowar tata gidan ba, tsabar ruɗewa ma kasa kiran Umma ya yi a waya shi ya sa ya kamo hanya ya dawo.
Ransa a matuƙar ɓace ya kalle ta ya ce
"Aliya mai ya dawo da ke gida" Gabaɗaya sai ta ji shakkar Abban ta kamata sannan sai ta tsinci kanta da kasa faɗa masa asalin abin da ya dawo da ita gidan, kallon mutanen wajen ta yi ko wata za ta ari bakin ta ta ci mata albasa amma sai ta ga kowa ya yi shiru hakan yana nuni da ana son waƙa a baki mai ita domin ta fi daɗin ji. Wani irin tsoron Abba ne ya lulluɓe ta tsoron da bata yi tunaninsa ba lokacin da za ta taho don yanayin yadda ta ga fuskar Abba ya nuna mata bai ji daɗin abin da ta yi ba sai dai ya za ta yi a nata ganin bata da wani zaɓi da wuce hakan, wata tsawa da Abba ya duka mata wacce sai da fitsari kaɗan ya ƙwace mata jin ya ce
"Ba magana nake miki mai ya rabo ki da ɗakin mijinki a kwana ɗaya tak da kika yi a gidansa" Ba Aliya ba hatta Umma da take ɗaki maganar yadda ya yi ta cikin ƙaraji ya hargitsa ƴaƴan hanjinta.
Aliya cike da fargaba bakinta yana rawa ta ce
"Abba, ma...ta...ma...za... ne Ka...sim...ɗin" Ta faɗa a tsorace tana danne kuka mai ƙarfin da yake son ƙwace mata, tana fatan ta samu goyan bayan Abba a kan maganar nan. Abba wanda ko kaɗan bai fuskanci abin da ta faɗa ba kasancewar a rarrabe ta yi maganar, juyawa bayansa ya yi ya ga wani bokiti wanda aka yi wanki aka ajiye ya ɗakko zai kwaɗa mata, aka shiga bashi baki yana tada jijiyoyin wuya cike da ɓacin rai ya ce
"Za ki faÉ—a min sakarcin da ya sa kika baro gidanki ko sai na sauya miki kamanni?" Aliya bata san lokacin da ta ce
Wata daga ciki ta c
"Lubabatu an aurar da Æ´aÆ´a yau an yi bacci fa munshari kowace ta shiga É—akinta lafiya" Umma ta ce
"Wallahi kuwa, ai mun yi waya ma da su ɗazu, ai kam duk wanda ya kai ƴa mace ɗakin miji kam dole ya yi bacci da munshari, saboda fargabar tarbiyar ƴa mace duk da cewa duk tarbiya ɗaya daga ta yarinya mace har ta yaro namij" Nan aka shiga yin hira ana ta yaba gidan Jidda wanda hakan yake haifarwa da Umma wani ɓacin rai kamar ana soka mata ƙahon ƙarfe a zuciya. Tsayuwar napep a ƙofar gidan sai kuma shigowar wani yaro ƙarami yana cewa wai a ba mai adaidaita kuɗi, kafin su samu damar bashi amsar wanda ya aiko shi, kukan Aliya da ya fara ratsa kunnuwansu tamkar an yi mutuwar da ba a ɗauke gawa ba ya saka gabaɗaya idanun kowa ya koma can...
MAMAN AFRAH
*Ina manyan matan? Na buɗe muku adashe mai so ga link nan ya shiga grp, ko a min magana pc idan kin san ba yi za ki yi ba bana son harkar ɓata lokaci.*
*ABUBUWAN DA ZA A YI ADASHEN SU NE*
*Leshi, atamfa jaka, takami kayan yara, takalman, yara, abaya, mayafai na shago, mayafai beadwrk, adire, kamfala, shadda, shaddales sai kuma kayan kicin da zanin gado ga mai buƙata* .
*Amfanin yin adashen domin samun sauƙin siyan abu idan kana zuba kuɗin da kaɗan zai baka damar samun abin da kake so saɓanin za ka ga wahalar siye a dunƙule, Allah sa mu fara a sa,a mu gama cikin nasara.*
[11/13, 12:45 PM] ðŸ˜: https://chat.whatsapp.com/GTq4oSxwxZfLKU7Amx5My1?mode=wwt
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 1ï¸âƒ£7ï¸âƒ£
*ALIYA*
Gabaɗaya kowa baki sake hankali tashe yake binta da kallo, kowa da abih da ya fara rayawa a zuciyarsa, wasu suna raya cewa ko mijin ne ya mutu, wasu suna tunanin ko dai bata kai masa mutuncinta ba ne shi ya sa ya mata shegen duka a koro ta, saɓanin Umma da tuni ta harbo jirgin abin da ya maido da Aliyar gida. Umma a take ta ji wani abu yana juyata tabbas ta san yau Aliya ta gama kunce mata zani a kasuwa ta tona mata asiri ita da take son komai ya zama na sirri amma ta kwaso ƙafa ta taho gida tana ɓare baki kamar dai an sanar da ita mutuwar wani shaƙiƙi nata.
Umma tamkar ta saka kuka haka ta ji don ta fara tunanin yadda za ta ɓoye matsalar nan amma da alama matsalar ba za ta ɓoyu ba, tun da dai gashi nan ta yi wa kanta fallasa auren bashi. Salatin da matan suka kwasa shi ya dakatar da Umma daga saƙa da warwarar jin ana ta jerawa Aliya tambayar lafiya? Sai dai kukan Aliyar ya hana ta bada amsa hakan ya da zargin da yake ran kowanne ya ninku fiye da farko, maganar yaron nan ta sake katse musu zulumi da ya ce
"Wai mai adaidaita sahu ya cw a bashi kuɗin" Umma da wasu kuɗi suke gefenta ta ɗauki ɗari biyar ta cillawa yaron ya ɗauka ya fita da gudu, Aliya ƙarasawa kan baranda ta yi ta zauna zaman dirshan cike da kuka ta ce
"Wallahi Umma ba zan zauna da shi ba" Kowa sai ya matso don jin ba,asin maganar don furucin ta ya nuna ba ita ce da laifi ba kamar yadda zuciyoyinsu suka saƙa musu a farko, kowa sai ya buɗe kunne don jin dalilin.
Umma ji ta yi kamar ta dannewa Aliya baki don kar ta faɗa domin ta san muddin ta yi maganar to kuwa shuka za ta yi a idon makwarwa don kowa sai ya ji labarin matsalar gidan aurenta, sani ne Aliya bata yi ba yanzu zancen duniya iya faɗawa baba ne, wuyar ta ka yi furuci sai ya bazu wani ma sai ya gama ƙara gishiri da maggi a maganar don ta yi armashi idan zai bada labari.
Umma ta rasa ma mai za ta ce duk da tana ta ƙoƙari wajen ganin ta dakatar da Aliyar daga abin sa take son faɗa, amma Aliya duk yadda Umma ta kai ga mata magana da ido amma ko idanun Ummar ma bata kalla ba,ɗaya daga cikin matan ta ce
"Aliya dama auren ƙiyayya ne aka miki?
Kafin ta bata amsa wata daga cikinsu rai a ɓace ta ce
"Ko auren ƙiyayya ne a kan mai za akai ta gidan miji ta taho gida? Ko ma mene ne ba sai ta zauna a magance matsalar ba, amma ta kamo hanya ta dawo gida wannan ai tonon asiri ne kuma dole idanun mutane ya dawo kanta, tun da yanzu kiwon mutum ake yi ba dabba ba"
Aliya cike da muryar kuka ta ce
"Ba dole in taho gida ba, mutuminnda yake ɗauke da mugun abu" Salati akam kwasa Umma kuwa kai ta ɗauke gefe tana jin kamar ta tsinewa Aliya don takaici gashi bata son ta dakatar da ita su ce bata ɗauke su a matsayi iyayen Aliyar ba tun da daga dangin Abba sai kuma nata ƴan uwan. Wata ƴar uwar Abba da ta zo daga ƙauye tana dafe ƙirji ta ce
"Wayyo Allah, mun shiga uku Allah sa bai kwanta da ke ba Aliya" Matar ita tunaninta mugun abun da Aliya ta ce tana nufin cutar HIV ita kuma Aliya sai ta ji zuciyarta ta ƙara karaya sannan ta ji daɗina ranta a ƙalla ta san dai wannan babban batu da za a raba auren tun da ta ga ana batun bai yi tarayya da ita ba, tana murje idanu ta ce
"Wallahi ganin idanuna na ga wajen facin da aka masa, ba don na gani ba da ba zan taɓa yarda ba" Umma a ƙufule ta ce
"Facin ubanki Aliya, shegiya sai ka ce wata tayar mota za ki ce faci wallahi ki kiyayeni" Ta faÉ—a tana tashi tsaye tana gyara É—aurin zanin ta da yake barazanar barin jikinta, tana jin kunya kamar ta nutse don kunyatawa dai yau Aliya ta kunayata ta a bainar jama,a.
Baki aka hau ba Umma ana faÉ—in ta mata a hankali ai babbar magana ce ta sanyata baro gidanta, Aliya buÉ—ar bakinta sai ta c
"Kuma wallahi da na san mata-maza ne ba zan aure shi ba, wajen ɗinkin tabon nan ba zai taɓa ɓacewa ba har ya mutu, da shi zai koma kabarinsa, ni ba zan ma je in ke haihuwar mata maza ba" Wasu sun ɗauki abin da girma don suna tunanin a mata maza Kasim ɗin ya fi ƙarfi ne ta ɓangaren mace basu san ma namiji ba ne kawai tsanarsa ce ta ƙoƙon ran Aliya har take ganin za ta rabu da shi.
Umma ɗaki ta shige jin kamar za ta nutse don kunya, tsayuwar nape a ƙofar gidan da kuma sallamar Abba da ya yi kana ganinsa ka ga wanda hankalinsa yake a tashe shi ya dakatar da ɗaya daga cikin matan da take ba Aliya baki.
Abba wanda maƙocinsa ya kira shi a waya yana tambayarsa lafiya ya ga Aliya an sauke ta a a daidaita sahu tana kuka ta shiga gida. Nan Abban ya nuna masa bai san ma da dawowar tata gidan ba, tsabar ruɗewa ma kasa kiran Umma ya yi a waya shi ya sa ya kamo hanya ya dawo.
Ransa a matuƙar ɓace ya kalle ta ya ce
"Aliya mai ya dawo da ke gida" Gabaɗaya sai ta ji shakkar Abban ta kamata sannan sai ta tsinci kanta da kasa faɗa masa asalin abin da ya dawo da ita gidan, kallon mutanen wajen ta yi ko wata za ta ari bakin ta ta ci mata albasa amma sai ta ga kowa ya yi shiru hakan yana nuni da ana son waƙa a baki mai ita domin ta fi daɗin ji. Wani irin tsoron Abba ne ya lulluɓe ta tsoron da bata yi tunaninsa ba lokacin da za ta taho don yanayin yadda ta ga fuskar Abba ya nuna mata bai ji daɗin abin da ta yi ba sai dai ya za ta yi a nata ganin bata da wani zaɓi da wuce hakan, wata tsawa da Abba ya duka mata wacce sai da fitsari kaɗan ya ƙwace mata jin ya ce
"Ba magana nake miki mai ya rabo ki da ɗakin mijinki a kwana ɗaya tak da kika yi a gidansa" Ba Aliya ba hatta Umma da take ɗaki maganar yadda ya yi ta cikin ƙaraji ya hargitsa ƴaƴan hanjinta.
Aliya cike da fargaba bakinta yana rawa ta ce
"Abba, ma...ta...ma...za... ne Ka...sim...ɗin" Ta faɗa a tsorace tana danne kuka mai ƙarfin da yake son ƙwace mata, tana fatan ta samu goyan bayan Abba a kan maganar nan. Abba wanda ko kaɗan bai fuskanci abin da ta faɗa ba kasancewar a rarrabe ta yi maganar, juyawa bayansa ya yi ya ga wani bokiti wanda aka yi wanki aka ajiye ya ɗakko zai kwaɗa mata, aka shiga bashi baki yana tada jijiyoyin wuya cike da ɓacin rai ya ce
"Za ki faÉ—a min sakarcin da ya sa kika baro gidanki ko sai na sauya miki kamanni?" Aliya bata san lokacin da ta ce