Sashe 6
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana daga can inda ta tsallaka tana hango direban nan da yake ta faman ba Jidda haƙuri kafin ya juya zai je ya shiga mota, ita ma Jiddan tana ta ƙoƙarin tafiya Aliya a zuciyar ta ta ce
'Hmmm! Ka ji da shi cuwon ajali a ɗan yatsa, tun da dai ka gama jiƙa mutane ai sai ka san inda dare ya maka, baka san cewa wannan baƙar mummunar da ita da bola mu duk ɗaya muke ganinsu ba, ni ma nan da ka ganni ƙaddara ta haɗani tafiya da ita, saboda kan nan nawa dusa ce ko in ce fanko ne babu komai a ciki, ko bihim ban sani ba wamda zan rubuta a exam ɗin da za mu yi, shi ya sa ma nake so mu tafi tare da ita tana rubutawa ina copy, dama ita take goyani a kowacce exam' Ta faɗa tana ɗan taɓe baki, tare da duba agogon da yake hannun ta.
Ibrahim kuwa da sauri ya saka hannu ya buɗe ƙofar ya fito lokacin Jidda ta fara tafiya, yana zuro ƙafafunsa farare tas da suke cikin baƙin takalmi mai yatsa, Aliya tun daga tsallaken titin da take ta hangi an buɗe bayan haɗaɗɗiyar motar wannan wacce ta gama yi wa direban motar ɗiban albarka, mamaki haɗe da al'ajabi suka haɗe suka cunkushe kwanyarta, wani irin bugawa ƙirjinta ya yi da ƙarfi lokaci guda zuciyarta ta aiko mata da wani saƙon tambaya kamar haka
'Dama akwai wani a cikin motar ba direban ba ne kaɗai, kenan mamallakin motar ne wannan ya fito?' Ta tambaya kwata-kwata ta gagara ƙifta idanunta don gani take idan ta ƙifta tamkar wanda take hangowar ɓacewa zai yi.
Ibrahim kuwa lokacin da ya fito Jidda ta masa É—an nisa, domin ta saka gabata can tana ta zabga sauri, sannan shi bai ma san sunanta ba abu É—aya kawai ya sani shi ne saboda ita ya fito daga motar. Direban ne ya buÉ—e ya fito, cikin hanzari ya gewayo inda Ibrahim É—in yake cike da girmamawa ya ce
"Yallaɓai kana buƙatar wani abu ne?" Ɗan shiru ya yi kafin daga bisani ya ce
"Kawai na ga baka kyautawa yarinyar can ba ne, kuma na ga ita ko uffan bata ce maka ba" Cike da alhini direban ya ce
"Wallahi yallaɓai ta san darajar mutane, duk da na yi abin ne cikin rashin sani kuma dama ɗan adama ajizi ne amma sai na ji ko kaɗan ban kyauta mata ba" Iska ya huro daga bakinsa yana sanya haƙorin gaba na cilin bakinsa ya dantse leɓansa na ƙasa, idanu ya mayar hanyar da Jiddar ta yi yana iya hango gidan da ta shiga daga can gefe wasu gidaje da suke a jere, sai ya ɗan jujjuya kamar mai neman wani abu, sai kuma ya kama ƙofar zai shige motar.
Aliya kuwa da take jin duk kan motsinsa tamkar da bugun zuciyarta yake, hakan ya sa ta fara tunanin ita yake nema, bata yi ƙasa a gwiwa ba ta fara ƙoƙarin tsallakowa, garin sauri har wata mota ta kusa kashe mata ƙafafu, amma hankalin ta ya yi gaba, tana fatan wannan mai kuɗin ya zamana cikar burinta da kuma mafarkinta da na mahaifiyarta, don yanzu ne take ganin za ta cika burin kyawun da Allah ya bata.
Garin sauri har harɗewa take, sai gata ta ƙaraso wajen a 360, Ibrahim ya ja ƙofar yana shirin rufewa don direban tuni ya shige mazaunin direba, kawai sai ya ga mace kamar an jefo ta, tana zuwa ta kama hannun ƙofar motar ta ce
"Gani" Cike da mamaki yake bin ta da kallon rashin fahimta, kunnuwansa suna dawo masa da sautin furucin da ta yi É—azu tun daga kan ashar da kuma cin mutuncin da ta yi wa direbansa, cike da takaici ya ce
"Wa yake neman ki?" Inda-inda ta fara jin tambayar da ya mata, rai ya haÉ—e ya ce
"Dalla matsa zan rufe mota" Da baya ta ja tana jin ƙamshin turarensa na masu aji, ya kaure ko ina na mashaƙar numfashin ta, ba ma wannan ba tsananin kyau da farin da yake da shi gashi kuma a gefe ɗaya ɗan gayu ne wannan ne abin da ya damfaru a zuciyarta, tana jin inama wannan ya zama mallakin ta tabbas da ta huta, babu ita babu kukan muni ko talaucin miji, don ta raɗawa zuciyarta wannan shi ne mijon da ake kan yayi, kuma shi ne wanda za a yi ta yayi har abada!.
MAMAN AFRAH
09025576222
[10/11, 9:47 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/B6ZgynXRCc3LWNggTkzg7X
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE4ï¸âƒ£
IBRAHIM
Yana gama rufe ƙofar ya ba direban umarnin su tafi, jan motar direban ya yi suka ƙarasa ƙofar tafkeken get ɗin kamfanin yana zuwa ya danna horn aka buɗe musu, ya cilla hancin motar cikin get ɗin.
Aliya da take tsaye a wajen kamar an dasa ta, idanunta ƙurrr a kan motar da take sheƙi tana ɗaukan idon sabunta, har suka shiga bata ɗauke idanunta ba, sai da ta ga an rufo get ɗin sannan ne ta dawo hayyacin ta, wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke, tana rayawa a zuciyarta cewa tabbas idan da rai da rabo ta ci alwashin mallakar wannan kyakkyawar halittar inda kuma take ganin za ta huta domin muddin ta auri wannan ta yi ban kwana da wata kalma wai wahala ko rashin kuɗi. Idanu ta lunshe tana hango kyakkyawan farin hannunsa mai ɗaure da tsadadden agogo a idon zuciyarta, tana iya hango yadda kwantaccen gashin hannun yake a jikin hannun yanayin fatarsa kaɗai tamkar wanda ba a Nigeri'a yake rayuwa ba, bata san lokacin da wani murmushi ya suɓuce mata ba don har ta fara hango irin soyayya da kulawar da za ta samu idan suka mallaki juna a matsayin ma'aurata.
Jidda kuwa lokacin da ta ƙarasa gida da sallama ta shiga, amma maimakon Umma ta amsa mata sai ta mata banza, sai da ta yi sau uku amma Umma ko ɗagowa bata yi ta kalle ta ba, bare ta saka ran za ta amsa mata, hakan ya sa cikin sanyin jiki ta shiga gidan tare da nufar ɗakin nasu don ta sauya kayan ta san matuƙar ta tsaya jiran sai Umma ta amsa mata sallama to har rana ta faɗa bata samu hakan ba. Gashi kuma tana son ta je kar a shiga jarabawa.
Tana shiga ɗakin ta nufi wajen jakar kayanta, dakyar ta ɗakko wata doguwar rigar atamfa roba ta saka duk atamfar ta koɗe, amma a haka ta saka saboda duk kayan nata idan Abba ya ɗinka musu Umma take ƙwace nata ta bayar sai ta sayi mai araha ta bata wani lokacin ma sai ta hanata mai arahar, shi kuma Abba da yake ba a gidan yake wuni ba kullum yana kasuwa ba sanin mai yake faruwa yake yi ba. Hijabi ta ɗauka ta saka shi ma duk ya ɗan yi fari, kayan ta mayar ta rataya a saman ƙofa a cewarta idan ta dawo daga makaranta sai ta wanke tun da yau jarabawa biyu za su yi.
Fitowa ta yi da jakarta a hannu, ganin Umma tana zuba ruwa a buta, ta ce
"Sai mun dawo Umma" Wata uwar harara Umma ta jefa mata, da ba za ta yi magana ba ma sai dai ta ce
"Ko ki dawo ko ki dawwama a can duk uwar ubansu ɗaya" Jikin Jidda sanyi ya yi hakan ya sa ta kalli Ummar kamar za ta yi kuka duk da wannan kalamai ne wanda ta saba jin su amma a koyaushe aka mata su sai ta ji su tamkar sabbi ne dal a leda aka buɗe, suna zame mata sababbi a koyaushe domin kalamai ne mararsa daɗi ƙiri-ƙiri ake nuna maka an tsane ka.
Ganin yanayin da Jidda ta shiga Umma ta ce
"To baƙa mai baƙar zuciya, kun ƙura min ido ni kar ki cinye ni kurwata kurrr, ni wallahi ban san dalilin da mutum zai ɗakko bare ya kawo cilin iyalinsa ba, ina dalili kawai a ɗakko mana annoba a kawo mana gida shekara da shekaru, ni yanzu ban ma san ranar da zamanki a gidan nan zai yanke ba, to wannan abu baƙiƙƙirin hanci kamar ƙofar gari abu babu fasali ta ko ina wane namijin ne ,ai kwasa? Tun da dai aure shi ne mafita ɗaya da za ki bar mana gida tun da babu dangin iya bare na Baba, babu inda za a kai ki ko ki raɓa mu ɗin dai mu ne ƙaryar taki, amma wallahi ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa, dole idan kuka ƙarasa makarantar nan tun da yanzu jarabawa ta rage idan baki samu mashinshini ba ko sadaka ce ba bayar da ke ko ga ladanin masallaci ne" Umma ta faɗa tana tashi tsaye daga sunkuyon da ta yi tana zuba ruwan a buta.
Jiki sanyi ƙalau Jidda ta juya tana ɗaga ƙafa kamar an mata dabaibayi a ƙafafu, fitowa ta yi daga gidan tana ɗaga ƙafa ta kamo hanya fito da wayarta keypad ta yi daga jaka ta duba ta ga lokaci ya kusa tana fatan kar a samu goslow a hanya.
Hango Aliya tsaye idanu a rufe ya bata mamaki, tana ƙarasowa ta ce
"Aliya lafiyarki kuwa?" Da sauri Aliya da idanunta suke rufe babu abin da take hangowa sai gasu nan sun yi aure da wannan kyakkyawan matashin tana cikin daula tana wulaƙanta ƴan aiki da kuma dangi ƴan uwa, hatta Jidda sai da ta ganta ta zo gidanta tana saka masu tsaron ƙofa su yi waje da ita wai bata santa ba.
Yatsina fuska Aliya ta yj lokacin da ta buɗe idanun, a maimakon ma ta ba Jidda amsa sai ta juya ta fara tafiya, ita Jiddar sai ta take mata baya suka ƙarasa bakin titin, napep suka tsayar suka shiga. Sa'adatu Rimi suka nufa domin a can ne suke karatun N.C.E suna shekararsu ta ƙarshe saura jarabawa biyu ma su kammala karatunsu.
'Hmmm! Ka ji da shi cuwon ajali a ɗan yatsa, tun da dai ka gama jiƙa mutane ai sai ka san inda dare ya maka, baka san cewa wannan baƙar mummunar da ita da bola mu duk ɗaya muke ganinsu ba, ni ma nan da ka ganni ƙaddara ta haɗani tafiya da ita, saboda kan nan nawa dusa ce ko in ce fanko ne babu komai a ciki, ko bihim ban sani ba wamda zan rubuta a exam ɗin da za mu yi, shi ya sa ma nake so mu tafi tare da ita tana rubutawa ina copy, dama ita take goyani a kowacce exam' Ta faɗa tana ɗan taɓe baki, tare da duba agogon da yake hannun ta.
Ibrahim kuwa da sauri ya saka hannu ya buɗe ƙofar ya fito lokacin Jidda ta fara tafiya, yana zuro ƙafafunsa farare tas da suke cikin baƙin takalmi mai yatsa, Aliya tun daga tsallaken titin da take ta hangi an buɗe bayan haɗaɗɗiyar motar wannan wacce ta gama yi wa direban motar ɗiban albarka, mamaki haɗe da al'ajabi suka haɗe suka cunkushe kwanyarta, wani irin bugawa ƙirjinta ya yi da ƙarfi lokaci guda zuciyarta ta aiko mata da wani saƙon tambaya kamar haka
'Dama akwai wani a cikin motar ba direban ba ne kaɗai, kenan mamallakin motar ne wannan ya fito?' Ta tambaya kwata-kwata ta gagara ƙifta idanunta don gani take idan ta ƙifta tamkar wanda take hangowar ɓacewa zai yi.
Ibrahim kuwa lokacin da ya fito Jidda ta masa É—an nisa, domin ta saka gabata can tana ta zabga sauri, sannan shi bai ma san sunanta ba abu É—aya kawai ya sani shi ne saboda ita ya fito daga motar. Direban ne ya buÉ—e ya fito, cikin hanzari ya gewayo inda Ibrahim É—in yake cike da girmamawa ya ce
"Yallaɓai kana buƙatar wani abu ne?" Ɗan shiru ya yi kafin daga bisani ya ce
"Kawai na ga baka kyautawa yarinyar can ba ne, kuma na ga ita ko uffan bata ce maka ba" Cike da alhini direban ya ce
"Wallahi yallaɓai ta san darajar mutane, duk da na yi abin ne cikin rashin sani kuma dama ɗan adama ajizi ne amma sai na ji ko kaɗan ban kyauta mata ba" Iska ya huro daga bakinsa yana sanya haƙorin gaba na cilin bakinsa ya dantse leɓansa na ƙasa, idanu ya mayar hanyar da Jiddar ta yi yana iya hango gidan da ta shiga daga can gefe wasu gidaje da suke a jere, sai ya ɗan jujjuya kamar mai neman wani abu, sai kuma ya kama ƙofar zai shige motar.
Aliya kuwa da take jin duk kan motsinsa tamkar da bugun zuciyarta yake, hakan ya sa ta fara tunanin ita yake nema, bata yi ƙasa a gwiwa ba ta fara ƙoƙarin tsallakowa, garin sauri har wata mota ta kusa kashe mata ƙafafu, amma hankalin ta ya yi gaba, tana fatan wannan mai kuɗin ya zamana cikar burinta da kuma mafarkinta da na mahaifiyarta, don yanzu ne take ganin za ta cika burin kyawun da Allah ya bata.
Garin sauri har harɗewa take, sai gata ta ƙaraso wajen a 360, Ibrahim ya ja ƙofar yana shirin rufewa don direban tuni ya shige mazaunin direba, kawai sai ya ga mace kamar an jefo ta, tana zuwa ta kama hannun ƙofar motar ta ce
"Gani" Cike da mamaki yake bin ta da kallon rashin fahimta, kunnuwansa suna dawo masa da sautin furucin da ta yi É—azu tun daga kan ashar da kuma cin mutuncin da ta yi wa direbansa, cike da takaici ya ce
"Wa yake neman ki?" Inda-inda ta fara jin tambayar da ya mata, rai ya haÉ—e ya ce
"Dalla matsa zan rufe mota" Da baya ta ja tana jin ƙamshin turarensa na masu aji, ya kaure ko ina na mashaƙar numfashin ta, ba ma wannan ba tsananin kyau da farin da yake da shi gashi kuma a gefe ɗaya ɗan gayu ne wannan ne abin da ya damfaru a zuciyarta, tana jin inama wannan ya zama mallakin ta tabbas da ta huta, babu ita babu kukan muni ko talaucin miji, don ta raɗawa zuciyarta wannan shi ne mijon da ake kan yayi, kuma shi ne wanda za a yi ta yayi har abada!.
MAMAN AFRAH
09025576222
[10/11, 9:47 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/B6ZgynXRCc3LWNggTkzg7X
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE4ï¸âƒ£
IBRAHIM
Yana gama rufe ƙofar ya ba direban umarnin su tafi, jan motar direban ya yi suka ƙarasa ƙofar tafkeken get ɗin kamfanin yana zuwa ya danna horn aka buɗe musu, ya cilla hancin motar cikin get ɗin.
Aliya da take tsaye a wajen kamar an dasa ta, idanunta ƙurrr a kan motar da take sheƙi tana ɗaukan idon sabunta, har suka shiga bata ɗauke idanunta ba, sai da ta ga an rufo get ɗin sannan ne ta dawo hayyacin ta, wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke, tana rayawa a zuciyarta cewa tabbas idan da rai da rabo ta ci alwashin mallakar wannan kyakkyawar halittar inda kuma take ganin za ta huta domin muddin ta auri wannan ta yi ban kwana da wata kalma wai wahala ko rashin kuɗi. Idanu ta lunshe tana hango kyakkyawan farin hannunsa mai ɗaure da tsadadden agogo a idon zuciyarta, tana iya hango yadda kwantaccen gashin hannun yake a jikin hannun yanayin fatarsa kaɗai tamkar wanda ba a Nigeri'a yake rayuwa ba, bata san lokacin da wani murmushi ya suɓuce mata ba don har ta fara hango irin soyayya da kulawar da za ta samu idan suka mallaki juna a matsayin ma'aurata.
Jidda kuwa lokacin da ta ƙarasa gida da sallama ta shiga, amma maimakon Umma ta amsa mata sai ta mata banza, sai da ta yi sau uku amma Umma ko ɗagowa bata yi ta kalle ta ba, bare ta saka ran za ta amsa mata, hakan ya sa cikin sanyin jiki ta shiga gidan tare da nufar ɗakin nasu don ta sauya kayan ta san matuƙar ta tsaya jiran sai Umma ta amsa mata sallama to har rana ta faɗa bata samu hakan ba. Gashi kuma tana son ta je kar a shiga jarabawa.
Tana shiga ɗakin ta nufi wajen jakar kayanta, dakyar ta ɗakko wata doguwar rigar atamfa roba ta saka duk atamfar ta koɗe, amma a haka ta saka saboda duk kayan nata idan Abba ya ɗinka musu Umma take ƙwace nata ta bayar sai ta sayi mai araha ta bata wani lokacin ma sai ta hanata mai arahar, shi kuma Abba da yake ba a gidan yake wuni ba kullum yana kasuwa ba sanin mai yake faruwa yake yi ba. Hijabi ta ɗauka ta saka shi ma duk ya ɗan yi fari, kayan ta mayar ta rataya a saman ƙofa a cewarta idan ta dawo daga makaranta sai ta wanke tun da yau jarabawa biyu za su yi.
Fitowa ta yi da jakarta a hannu, ganin Umma tana zuba ruwa a buta, ta ce
"Sai mun dawo Umma" Wata uwar harara Umma ta jefa mata, da ba za ta yi magana ba ma sai dai ta ce
"Ko ki dawo ko ki dawwama a can duk uwar ubansu ɗaya" Jikin Jidda sanyi ya yi hakan ya sa ta kalli Ummar kamar za ta yi kuka duk da wannan kalamai ne wanda ta saba jin su amma a koyaushe aka mata su sai ta ji su tamkar sabbi ne dal a leda aka buɗe, suna zame mata sababbi a koyaushe domin kalamai ne mararsa daɗi ƙiri-ƙiri ake nuna maka an tsane ka.
Ganin yanayin da Jidda ta shiga Umma ta ce
"To baƙa mai baƙar zuciya, kun ƙura min ido ni kar ki cinye ni kurwata kurrr, ni wallahi ban san dalilin da mutum zai ɗakko bare ya kawo cilin iyalinsa ba, ina dalili kawai a ɗakko mana annoba a kawo mana gida shekara da shekaru, ni yanzu ban ma san ranar da zamanki a gidan nan zai yanke ba, to wannan abu baƙiƙƙirin hanci kamar ƙofar gari abu babu fasali ta ko ina wane namijin ne ,ai kwasa? Tun da dai aure shi ne mafita ɗaya da za ki bar mana gida tun da babu dangin iya bare na Baba, babu inda za a kai ki ko ki raɓa mu ɗin dai mu ne ƙaryar taki, amma wallahi ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa, dole idan kuka ƙarasa makarantar nan tun da yanzu jarabawa ta rage idan baki samu mashinshini ba ko sadaka ce ba bayar da ke ko ga ladanin masallaci ne" Umma ta faɗa tana tashi tsaye daga sunkuyon da ta yi tana zuba ruwan a buta.
Jiki sanyi ƙalau Jidda ta juya tana ɗaga ƙafa kamar an mata dabaibayi a ƙafafu, fitowa ta yi daga gidan tana ɗaga ƙafa ta kamo hanya fito da wayarta keypad ta yi daga jaka ta duba ta ga lokaci ya kusa tana fatan kar a samu goslow a hanya.
Hango Aliya tsaye idanu a rufe ya bata mamaki, tana ƙarasowa ta ce
"Aliya lafiyarki kuwa?" Da sauri Aliya da idanunta suke rufe babu abin da take hangowa sai gasu nan sun yi aure da wannan kyakkyawan matashin tana cikin daula tana wulaƙanta ƴan aiki da kuma dangi ƴan uwa, hatta Jidda sai da ta ganta ta zo gidanta tana saka masu tsaron ƙofa su yi waje da ita wai bata santa ba.
Yatsina fuska Aliya ta yj lokacin da ta buɗe idanun, a maimakon ma ta ba Jidda amsa sai ta juya ta fara tafiya, ita Jiddar sai ta take mata baya suka ƙarasa bakin titin, napep suka tsayar suka shiga. Sa'adatu Rimi suka nufa domin a can ne suke karatun N.C.E suna shekararsu ta ƙarshe saura jarabawa biyu ma su kammala karatunsu.