Sashe 86
Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da ta dama kokon, sai ta ɗauki sauran fulawar da ta rage mata wacce ita ta saya ta kwaɓa ta musu waina ta saka a fulas ta gaa sai ta ɗora ruwan zafin wanka wanda ta san ma ba lallai gawayin ya isa dafawa ba. Kicin ɗin ta janyo bayan ta ɗakko jug ɗin kokon da kuma kwanon wainar. A falo ta ajiye sai ta koma ta ɗakko plate da kofi da cokali ta dawo ta zuba wainar da kokon da ta saka sugar ta zauna tana ci bata ma ra,ayjn ci da ya ji sai da ta ji ta ƙoshi ta rufewa Kalifa sauran. Tana jin lokacin da su Husna suka buga gidan aka buɗe musu wajen ƙarfe takwas kuma Meenal ce ta buɗe tana jin yadda take musu masifa wai sun ɓata lokaci ba su zo da wuri ba, haka ta ji suna bata haƙuri kamar wata uwarsu.
Har suka gama suka tafi bata fito ba Kalifa kuma har lokacin bacci yake kasancewar jiyan ya yi ta gijifgijiftu a gidan kaka, saboda gajiya shi ya sa bai tashi da wuri ba. Bayan tafiyarsu sai ta gyara ɗaki ta share tas ta yi goge goge sai ta kunna turaren tsinke, tsakar gidan ta shiga sharewa, sai ta ta je tana tattarawa sai kawai ta ga wani abu da ya bata mamaki, da sauri ta kai hannu ta ɗakko tana juya shi a hannunta gabanta ya buga da ƙarfi domin tabbas ko tantama babu zip ɗin jakarta ne, abin da ya sa ta game shi zip ɗin jakarta daga aarshensa a ɗan lanƙwashe yake ba komai ya lanƙwasa shi sai wani lokaci ya cije ya ƙi ziguwa shi ne ta maƙala shi jikin ƙofa ta cisga da ƙarfi shi ne ya lanƙwashe daga wajen kamawar, abin da ya bambanta wannn da nata shi ne wannn baƙiƙƙitin da shi kamar wanda aka ƙona shi.
Tsaye ta miƙe tana aara ƙare masa kallo fitowar Nasir da Meenal daga ɗaki ya sa ta yi saurin juyowa, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kai kamar ya ga kashi sai dainita ba wannn bane a gabanta saboda yanzu abinnda yake gabanta na mamaki da al,ajabi ya danne komai. Ba ta san lokacin da ta ce
"Wallahi wannna ƙarfen zip ɗin jakata ne" Dududdummm gaban Meenal ya harba da ƙarfi amma saboda ƴar bariki ce sai ta basar tana mayar da kallonta kan Nasir tana wani kashe murya shi kuma yana biye mata bai ma damu da maganar da Sadiyar ta yi ba sai da Sadiya ta ankara da abin da ta ce sannan cike da sanyin murya ta ce
"Ina kwana Abban Kalifa, an tashi lafiya" Ta faÉ—a a tare don gabaÉ—aya ta shiga ruÉ—u da tunanin yadda aka haihu a ragaya.
Amsawa ya yi kamar an masa dole ganin haka sannan kuma ta ga alamar Meenal ba za ta bari su yi maganar ba sai ta ce
"Wallahi jakata da nake ajiye kuɗin cinikina ne ta ɓata rasa ta na yi kuma abin mamaki yanzu da nake shaarar nan sai na ga ƙarfen zip ɗin a can" Ta faɗa tana nuni da inda ta ga zip ɗin. Meenal kai ta kawar gefe domin kar a hango jirginta shi kuma tamkar ta faɗa masa saƙon mutuwa ya gaɗe girar sama da ƙasa ya ce
"To ko ni ne na É—auka?" Ya tambaya cike da gatse. Kai ta girgiza alamar a,a ganin yana neman É—ora mata jakar tsaba kaji su bi ta sai ta ce
"Kawai dai ina mamaki ne wallahi abin kamar almara"Hankalinsa ya mayar kan Meenal da take magana cikin muryar ɓaci duk ta wani shagwaɓe fuska.
Meenal tana ta mamakin yadda aka yi da ta ƙone jakar bata ɗauke da ƙarfen zip ɗin ba.
Ya fara tafiya Sadiya ta ce
",Ina da magana "
Ya ce
"Za ki iya faɗa tun da babu bare a nan" Kallon fuskar Meenal ta yi wacce ta murmusa fuskarta ta nuna alamar murmushin ƙeta wato da alama ta zama ƙarfen ƙafa komai ma a gabanta za a faɗa. Daurewa ta yi tana danne takaicin da suke ƙunsa mata wanda watarana sai zuciya ta zuga ta a kan ta rama sai kuma wata zuciyar ta ce ta ƙyale watarana saj labari!.
Tana kallon yanayin fuskarsa ta ce
"Gawayina ne ya ƙare ɗazu ma dakyar ya isa na yi amfanj da safe... Numfashin ta ya tara da faɗin
"Sadiya ni ba na son almubazzaranci ta yaya za a yi gawayjn a ce har ya ƙare to ni ba ni da kuɗj yanzu sai dai ko in bada itace a kawo miki" Ƙwalla ta taru a idanunta bayan da gawayi take amfanj Meenal tana amfani da gas sannan kuma tana cancantawa amma kuma yanzu a mata maganar ita ce jin hakan Meenal ta ce
",Gas ɗina ni ma fa ina ga ya kusa ƙarewa" !Wani irin washe baki ya yi ya ce
"Tohm zan saka miki idan na dawo" ,Tana masa bye bye ya fita ya tafj Sadiya kuma ta kasa motsawa ma daga wajen, wannan abubuwa ne masu tarin yawa da suke nuni da cewa Nasir ya gaji da ita, sai dai tana jiran ranar da Allah zai kawo mata mafita a lamuran nan. Tana jin yadda Meenal take dariya har da ƙyaƙyatawa da ta ga ta nufi ɗaki, ko da ta shigo ɗakin zaman dirshan a falon tana tunanin ƙarfen zip ɗin da ta tsinta ta rasa ta yaya haka ya faru ta rasa kalar tunanjn da za ta yi, iya hasashe da tunanin ta bata samu amsar ba da a ce a buɗe ɗakinta yake za ta zargi komai ma sai dai a rufe yake sannn da mukulli ta fita idan ba aljannu ba waye zai ɗauka?. Kukan da Kalifa ya saki ne ya dawo da ita daga tunanin da take.
Zuwa can aka zo sayen manja ganin babu ƙullal ne a leda saj ta buɗe jarkar ta tsiyaya a za ta ƙulla saj ta ji warin kananzir cike da faɗuwar gaba ta kai hancinta jikin ƙofar amma sai ta ji warin tamkar ta shinshina jarkar kananzir, da sauri ta saki murfin jarkar ta nufi ɗayan ta farin mai gabanta yana faɗuwa ta buɗe amma cikin ikon Allah sai ta ji babu warin hamdala ta yi a ranta tana ta kissima abubuwa a ranta duk da an ce zato zunubi amma kam tana ta zargi a zuciyarta.
Ko da ya tafi ko ƙeyarsa babu bare a samu wanda zai kawo mata itacen da ya ce, da rana dai gari da madara da sugar ta haɗa musu suka sha, tana tausayin Nasir ranar da haƙƙi zai tambaye shi musamman haƙƙin ɗansa Kalifa domin shi yaron ko kaɗan bai san daɗin uba ko kulawarsa ba ga shi koyaushe daɗa wayo yake, ita damuwarta ma yadda yaron idan ya ga ana mata abu yake nuna rashin jin daɗi ta hanyar kukansa ko kuma yake goge mata hawaye yana ambaton Momma Abba ne? Duk da tana iya yinta don ganin bata kuka a gabansa.
Tana tsakar gida lokacin almajirin Meenal yana mata sharar baranda, ita kuma ta kinkimo jarkar man mai warin kananzir sai kawai suka yi ido huɗu da Meenal ta mata dariya, hakan ya sa a ƙufule Sadiya ta ce
"Wai mai kika mayar da ni ne Meenal sai kike kallona kina min dariya kamar wata mahaukaciya kika gani?" Dariyar ta ƙara yi a karo na biyu sai Sadiya ta ce
"Ko mai mutum ya yi ya je shi da Allah domin yana can a madakata yana jiransa duk daren daɗewa akwai mutuwa sannan akwai hisabi shi dai ubangiji ba ya yafe haƙƙin wani a kan wani" Ɗan dum Meenal ta yi sai ta ji ta kasa cewa komai domin zuciyarta ta fara raya mata ko dai Sadiya ta gane ita ta mata sata kuma ita ta zuba mata kananzir a cikin jarkar manja, domin yanayin furucinta ya bayyana kamar dai akwai wani abu.
Ɗakinta kawai ta wuce ba tare da ta ce komai ba. Da yamma Sadiya ta masa waya tw ce za ta je gidan Hajiya bai musa ba don ya san wani neman wajen ne za ta je tun da Hajiya dai ba ra,ayinta take yi ba, sannan kuma ya san tana zuwa za ta dawo a kan sawunta tun da ba ma lallai a ƙara mata magana daga gaisuwa ba.
Ko da ta je gidan Hajiya ta samu Hajiya zaune a gindin murhu tana tuƙa tuwo, sai goge ido take saboda hayaƙi, ta amsa mata babu yabo babu fallasa don su Hibba ma ba sa gidan sai ita kaɗai. Tabarmar da aka shimfiɗa a wajen ta zauna, ko Kalifa Hajiya bata wa magana ba. Sai da ta rufe tukunyar bayan ta gama tuƙawa ta taso ta shiga ɗaki ta jima sannan a shelaƙe ta fito ta zo ta zauna daga can bakin barandar
Sadiya ta ce
"Dama wata magana na zo da ita... Hajiya ta tari numfashin ta da faÉ—in
"Sadiya ni ba na sin kinibibi da gutsiri tsoma, wace irin magana ana zaune ƙalau dama duk mace ai sai ta yi haƙuri a gidan miji sannan dama idan kika san ma ba ke kaɗai ba ce sai dai ki kauda kai saboda wani namijin idan ba ya ra,ayin ɗaya ya fi ra,ayin ɗaya a cikin matansa sai dai wacce ba ya ra,ayi ta ɗauki dangana, idan ma ta ce sai ta ga yadda take so tabbas iska tana yawo da mai kayan kara ne!" Ɗago kai Sadiya ta yi suka yi ido huɗu Hajiyar ta kauda kai gefe, sai Sadiya ta ce
"Ba a kan wani abu ba ne dama, kin san ina sana,ar kayan sanyi to shi ne ƴan nepa suka cire wutar ɓangarena shi kuma ya ce sai ina biyan kuɗin wuta ... Hajiya ta tare mata numfashi da faɗin
"Ai ya yi daidai! Kina neman kuÉ—i kuma a ce sai ya biya kuÉ—in wuta? Ko shi kike ba kuÉ—in cinikin yake sakawa a aljihunsa" Girgiza kai Sadiya ta yi daman ta san ba za a mata adalci ba hakan ya sa ta ce
Har suka gama suka tafi bata fito ba Kalifa kuma har lokacin bacci yake kasancewar jiyan ya yi ta gijifgijiftu a gidan kaka, saboda gajiya shi ya sa bai tashi da wuri ba. Bayan tafiyarsu sai ta gyara ɗaki ta share tas ta yi goge goge sai ta kunna turaren tsinke, tsakar gidan ta shiga sharewa, sai ta ta je tana tattarawa sai kawai ta ga wani abu da ya bata mamaki, da sauri ta kai hannu ta ɗakko tana juya shi a hannunta gabanta ya buga da ƙarfi domin tabbas ko tantama babu zip ɗin jakarta ne, abin da ya sa ta game shi zip ɗin jakarta daga aarshensa a ɗan lanƙwashe yake ba komai ya lanƙwasa shi sai wani lokaci ya cije ya ƙi ziguwa shi ne ta maƙala shi jikin ƙofa ta cisga da ƙarfi shi ne ya lanƙwashe daga wajen kamawar, abin da ya bambanta wannn da nata shi ne wannn baƙiƙƙitin da shi kamar wanda aka ƙona shi.
Tsaye ta miƙe tana aara ƙare masa kallo fitowar Nasir da Meenal daga ɗaki ya sa ta yi saurin juyowa, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kai kamar ya ga kashi sai dainita ba wannn bane a gabanta saboda yanzu abinnda yake gabanta na mamaki da al,ajabi ya danne komai. Ba ta san lokacin da ta ce
"Wallahi wannna ƙarfen zip ɗin jakata ne" Dududdummm gaban Meenal ya harba da ƙarfi amma saboda ƴar bariki ce sai ta basar tana mayar da kallonta kan Nasir tana wani kashe murya shi kuma yana biye mata bai ma damu da maganar da Sadiyar ta yi ba sai da Sadiya ta ankara da abin da ta ce sannan cike da sanyin murya ta ce
"Ina kwana Abban Kalifa, an tashi lafiya" Ta faÉ—a a tare don gabaÉ—aya ta shiga ruÉ—u da tunanin yadda aka haihu a ragaya.
Amsawa ya yi kamar an masa dole ganin haka sannan kuma ta ga alamar Meenal ba za ta bari su yi maganar ba sai ta ce
"Wallahi jakata da nake ajiye kuɗin cinikina ne ta ɓata rasa ta na yi kuma abin mamaki yanzu da nake shaarar nan sai na ga ƙarfen zip ɗin a can" Ta faɗa tana nuni da inda ta ga zip ɗin. Meenal kai ta kawar gefe domin kar a hango jirginta shi kuma tamkar ta faɗa masa saƙon mutuwa ya gaɗe girar sama da ƙasa ya ce
"To ko ni ne na É—auka?" Ya tambaya cike da gatse. Kai ta girgiza alamar a,a ganin yana neman É—ora mata jakar tsaba kaji su bi ta sai ta ce
"Kawai dai ina mamaki ne wallahi abin kamar almara"Hankalinsa ya mayar kan Meenal da take magana cikin muryar ɓaci duk ta wani shagwaɓe fuska.
Meenal tana ta mamakin yadda aka yi da ta ƙone jakar bata ɗauke da ƙarfen zip ɗin ba.
Ya fara tafiya Sadiya ta ce
",Ina da magana "
Ya ce
"Za ki iya faɗa tun da babu bare a nan" Kallon fuskar Meenal ta yi wacce ta murmusa fuskarta ta nuna alamar murmushin ƙeta wato da alama ta zama ƙarfen ƙafa komai ma a gabanta za a faɗa. Daurewa ta yi tana danne takaicin da suke ƙunsa mata wanda watarana sai zuciya ta zuga ta a kan ta rama sai kuma wata zuciyar ta ce ta ƙyale watarana saj labari!.
Tana kallon yanayin fuskarsa ta ce
"Gawayina ne ya ƙare ɗazu ma dakyar ya isa na yi amfanj da safe... Numfashin ta ya tara da faɗin
"Sadiya ni ba na son almubazzaranci ta yaya za a yi gawayjn a ce har ya ƙare to ni ba ni da kuɗj yanzu sai dai ko in bada itace a kawo miki" Ƙwalla ta taru a idanunta bayan da gawayi take amfanj Meenal tana amfani da gas sannan kuma tana cancantawa amma kuma yanzu a mata maganar ita ce jin hakan Meenal ta ce
",Gas ɗina ni ma fa ina ga ya kusa ƙarewa" !Wani irin washe baki ya yi ya ce
"Tohm zan saka miki idan na dawo" ,Tana masa bye bye ya fita ya tafj Sadiya kuma ta kasa motsawa ma daga wajen, wannan abubuwa ne masu tarin yawa da suke nuni da cewa Nasir ya gaji da ita, sai dai tana jiran ranar da Allah zai kawo mata mafita a lamuran nan. Tana jin yadda Meenal take dariya har da ƙyaƙyatawa da ta ga ta nufi ɗaki, ko da ta shigo ɗakin zaman dirshan a falon tana tunanin ƙarfen zip ɗin da ta tsinta ta rasa ta yaya haka ya faru ta rasa kalar tunanjn da za ta yi, iya hasashe da tunanin ta bata samu amsar ba da a ce a buɗe ɗakinta yake za ta zargi komai ma sai dai a rufe yake sannn da mukulli ta fita idan ba aljannu ba waye zai ɗauka?. Kukan da Kalifa ya saki ne ya dawo da ita daga tunanin da take.
Zuwa can aka zo sayen manja ganin babu ƙullal ne a leda saj ta buɗe jarkar ta tsiyaya a za ta ƙulla saj ta ji warin kananzir cike da faɗuwar gaba ta kai hancinta jikin ƙofar amma sai ta ji warin tamkar ta shinshina jarkar kananzir, da sauri ta saki murfin jarkar ta nufi ɗayan ta farin mai gabanta yana faɗuwa ta buɗe amma cikin ikon Allah sai ta ji babu warin hamdala ta yi a ranta tana ta kissima abubuwa a ranta duk da an ce zato zunubi amma kam tana ta zargi a zuciyarta.
Ko da ya tafi ko ƙeyarsa babu bare a samu wanda zai kawo mata itacen da ya ce, da rana dai gari da madara da sugar ta haɗa musu suka sha, tana tausayin Nasir ranar da haƙƙi zai tambaye shi musamman haƙƙin ɗansa Kalifa domin shi yaron ko kaɗan bai san daɗin uba ko kulawarsa ba ga shi koyaushe daɗa wayo yake, ita damuwarta ma yadda yaron idan ya ga ana mata abu yake nuna rashin jin daɗi ta hanyar kukansa ko kuma yake goge mata hawaye yana ambaton Momma Abba ne? Duk da tana iya yinta don ganin bata kuka a gabansa.
Tana tsakar gida lokacin almajirin Meenal yana mata sharar baranda, ita kuma ta kinkimo jarkar man mai warin kananzir sai kawai suka yi ido huɗu da Meenal ta mata dariya, hakan ya sa a ƙufule Sadiya ta ce
"Wai mai kika mayar da ni ne Meenal sai kike kallona kina min dariya kamar wata mahaukaciya kika gani?" Dariyar ta ƙara yi a karo na biyu sai Sadiya ta ce
"Ko mai mutum ya yi ya je shi da Allah domin yana can a madakata yana jiransa duk daren daɗewa akwai mutuwa sannan akwai hisabi shi dai ubangiji ba ya yafe haƙƙin wani a kan wani" Ɗan dum Meenal ta yi sai ta ji ta kasa cewa komai domin zuciyarta ta fara raya mata ko dai Sadiya ta gane ita ta mata sata kuma ita ta zuba mata kananzir a cikin jarkar manja, domin yanayin furucinta ya bayyana kamar dai akwai wani abu.
Ɗakinta kawai ta wuce ba tare da ta ce komai ba. Da yamma Sadiya ta masa waya tw ce za ta je gidan Hajiya bai musa ba don ya san wani neman wajen ne za ta je tun da Hajiya dai ba ra,ayinta take yi ba, sannan kuma ya san tana zuwa za ta dawo a kan sawunta tun da ba ma lallai a ƙara mata magana daga gaisuwa ba.
Ko da ta je gidan Hajiya ta samu Hajiya zaune a gindin murhu tana tuƙa tuwo, sai goge ido take saboda hayaƙi, ta amsa mata babu yabo babu fallasa don su Hibba ma ba sa gidan sai ita kaɗai. Tabarmar da aka shimfiɗa a wajen ta zauna, ko Kalifa Hajiya bata wa magana ba. Sai da ta rufe tukunyar bayan ta gama tuƙawa ta taso ta shiga ɗaki ta jima sannan a shelaƙe ta fito ta zo ta zauna daga can bakin barandar
Sadiya ta ce
"Dama wata magana na zo da ita... Hajiya ta tari numfashin ta da faÉ—in
"Sadiya ni ba na sin kinibibi da gutsiri tsoma, wace irin magana ana zaune ƙalau dama duk mace ai sai ta yi haƙuri a gidan miji sannan dama idan kika san ma ba ke kaɗai ba ce sai dai ki kauda kai saboda wani namijin idan ba ya ra,ayin ɗaya ya fi ra,ayin ɗaya a cikin matansa sai dai wacce ba ya ra,ayi ta ɗauki dangana, idan ma ta ce sai ta ga yadda take so tabbas iska tana yawo da mai kayan kara ne!" Ɗago kai Sadiya ta yi suka yi ido huɗu Hajiyar ta kauda kai gefe, sai Sadiya ta ce
"Ba a kan wani abu ba ne dama, kin san ina sana,ar kayan sanyi to shi ne ƴan nepa suka cire wutar ɓangarena shi kuma ya ce sai ina biyan kuɗin wuta ... Hajiya ta tare mata numfashi da faɗin
"Ai ya yi daidai! Kina neman kuÉ—i kuma a ce sai ya biya kuÉ—in wuta? Ko shi kike ba kuÉ—in cinikin yake sakawa a aljihunsa" Girgiza kai Sadiya ta yi daman ta san ba za a mata adalci ba hakan ya sa ta ce