← Book details Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 106

Sashe 11

Ruwa Cikin Cokali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Wahalalliya ce wannan yarinyar in banda rashin aikin yi islamiya dai tun ana yara ake abu ɗaya, yanzu an zama ƴanmata har ana shirin shiga ɗakin miji amma ba za a haƙura ba" Aliya ta yi wata dariyar rainin wayo ta ce

"Umma sai faÉ—i kike wai za a shiga É—akin miji to in dai ba ita kaÉ—ai za a saka a É—akin ba waye zai kashi wanann?"

Umma ta ce

"Kuma fa haka ne, ai wallahi malamin nan da ya yi wa yarinyar nan maganin baƙin jini, samari suka daina wannan rawar ƙafar zuwa ƙofar gidan nan ai dole in koma in masa kyauta, yanzu shiru kike ji in ta fita ko kare ba ya biyo ta"

Aliya ta ce

"Wallahi kuwa Umma ai kin yi farar dabarw, da yanzu ni za ta tashi ta bari a gidan ake cewa Æ´arki ta yi kwanta"

Umma ta ce

"Ai sai dai in bana raye, amma matuƙar ina numfashi Aliya Jidda bata isa ta tafi ɗakin miji ta barki a gida ba" Sosai suke ta hira abin su.

Ibrahim tun daga ranar da ya yi tozali da Jidda bai samu sukuni ba, sosai sonta yake azalzalar zuciyarsa, kuma ya yi bakin ƙoƙarinsa wajen zuwa ƙofar gidansu har sau biyu amma bai ga wulginta ba, shi kuma yana jin nauyin ya aika kiranta, kuma ma idan zai aika wa zai ce? Shi bai san sunanta ba. Daga Daddy har Mummy babu wanda ya san wainar da yake toyawa sai dai sun ɗan fara lura da yanayinsa don ya sauya, sai dai da suka tambaye shi dalili amsa ɗaya ce ita ce kawai ba ya jin daɗin jikin sa gar doctor su na gida Abba ya kira a kan ya duba lafiyarsa amma babu abij da yakr damun lafiyarsa.

Kamar kullum yau ma yana zaune a tangameman falonsa da yake part ɗinsa, zaune yake a kan kujera, sai karamin tebur a gabansa, laptop ɗinsa ce da ƙaramin kofi mai ɗauke da coffee. Aiki yake a laptop ɗin amma hankalinsa yana ga tunanin Jidda, ɗan matsar da laptop ɗin gefe ya yi ya ɗauki coffee ɗin ya sha kaɗan ya mayar da kofin kan ƙaramin kofin glass ɗin ya ajiye, ganin ya rasa sukuni ya rufe laptop ɗin ya kashe fitilun duka na falon ya nufi bedroom, toilet ya shiga ya yi alwala ya fito ya hau gadonsa wanda ya sha shimfiɗar lallausan zanin gadon MAMAN AFRAH mai kyau gashi da ƙwari sannan zanin gadon mai ɗauke da bargo ne wanda aka shimfiɗa ɗin ma mai faiba a ciki ne ya yi matuƙar kyau ɗinkin. Hawa ya yi ya kwanta yana ɗakko wayarsa da take ajiye daga gefen gadon ya danna ya duba time, ajiyewa ya yi tare da yin addu,a ya shafe jikinsa tare da lumshe kyawawan idanunsa, cike da tunaninta nannauyan bacci ya ɗauke shi.

Washe gari ko da ya tashi da tunanin ta ya tashi, sai ya ɗaukawa kansa alƙwarin duk inda take in har tana garin Kano sai ya nemo ta ya ba idanunsa abinci ko zai samu salama a zucuya da ruhinsa. Da yamma ya shiga ya yi wanka ya fito ya shirya cikin tsaddaden yadin kufta wanda aka yi wa adon zare na ɗinkin hannu, saƙar ɗinkin ya yj matuƙar amsar ash colour yadin. Bayan ya kamala shiryawa ya ɗakko hula mai ash mai ɗauki da ratsin fari da ɗan blue wanda bai ciza ba da aka ɗan yi wani layi-layi da shi a jikin hular, kallonsa yake a madubi yana yabawa kansa kyau ɗin da ya yi, turarukansa da suka gaji da haɗuwa ya feshe jikinsa da su a take ɗakin ya gauraye da daddaɗan sansanyan ƙamshi mai ratsa zuciya!.

Mummy ya sanar cewa zai je wajen abokinsa Abeed, yana fitowa ya ɗauki wata sabuwar ash ɗin mota ya shiga sai sheƙi take sai dai glass ɗin kotar baƙi ne ba a ganin wanda yake ciki, mai gadi ya buɗe masa ƙofa yana ɗaga masa hannu da masa fatan alkairi, don da gani an ga tafiya ta musamman saboda ko direba bai bi ta kansa ba, horn kawai ya yi wa mai gadin shi ne amsar maganar da yake masa a zuciyarsa kuma yana amsa addu'ar da mai gadin ya masa.

Kan titi ya nausa motar yana tafiya a hankali karatun qur'ani yana tashi a motar, tun da ya zo inda zai gangara gidan da yakr tsammanin gidan su Jiddan ne, inda ya hanga ta shiga ranar nan, gabansa yake tsanani da mummunar faɗuwa bai san dalili ba amma ya alaƙanta hakan da SO.

Misalin ƙarfe biyar ya zo wajen amma kuma har biyar da rabi babu wanda ya fito ko ya shiga gidan da yake tsammanin ganin Jiddan. Dama ba a ƙofar gidan ya yi parking ba daga can gefe ne, har biyar da arba'in babu kowa sai mutane da suke ta hada -hada da kuma yara suna ficewa sai dai shi bai san ya zai yi ya ce a mata magana ba. Yana nan sai ya hangi wata budurwa ta taho rana zuwa ta nufi gidan, zuciyarsa tana raya masa ya fita ya tambaye ta amma kuma shi ko kaɗan ma yarinyar bata masa ba yanayin shigarta da ma tafiyar da take, hakan ya sa ya koma ya jingina, don hatta karatun ya kashe kawai zaman jiran tsammani yake. Bayan ta shiga gidan jim kaɗan sai gasu sun fito su biyu ransa ne ya ɓaci a lokacin da ya ga Aliya wacce suka fito da Amatullahi wacce ta shiga gidan yanzu. Ko kaɗan ba ya son ma'amalar Aliya da Jidda don a ganinsa basu dace da yin ƙawance ba ji ya yi kamar ta fito ya ce daga yau kar su ƙara zuwa gidan su Jiddan.

Har suka ɓacewa ganinsa ransa a ɓace, daga can ya hango wasu ƴanɓata guda biyu sanye da dogayen hijabi, suna tahowa, idanunsa ƙurrr a kan Jidda don tun daga ganin da ya mata na farko bai taɓa manta kamaninta da kuma yanayin tafiyarta mai nutsuwa ba, ko ƙiftawa ba ya yi gani yake idan ya ƙifta zai rasa ganinta har abada. Zuciyarsa tana masa zillo so yake ya yi amfani da wannan damar ya fito daga motar ya tunkare ta ya faɗa mata sirrin zuciyarsa amma faɗuwar da gabansa yake ba ya ji ma idan ya fito bakinsa zai bashi haɗin kai na gabatar mata da kansa. Jidda wacce suke tafiya da Salama ƙawarta haka suka taho har suka zo daidai motar da Ibrahim yake ciki, dama hira suke abinsu amma maganar da suke basu gama ba kuma za su rabu domin gida Salamar ma za ta wuce.

Ganin motar da take gefe a ajiye kasancewar gilashin baƙi ne basa ganin wanda yake ciki, ƙarasawa suka yi suka jingina da motar, Ibrahim da yake ciki gabaɗaya an dagula masa lissafi da farko ma da ya ga sun nufo motar ga ɗauka suna ganinsa domin ya manta cewa gilashin na waje ba ya ganin wanda yake cikin motar. Kamar ya fito ya gudu haka ya ji sai da ya ga sun tsaya a jikin motar hankalinsa ya kwanta, ya rasa dalili amma dai yana tunanin saboda bai taɓa tunkarar wata ƴa mace da sunan so ba ne. Kasancewar Jidda ba baya ta juyawa motar ba gefen kafaɗarta ne ta jingina ita kuma ƙawar ta juya baya, yanayin tsayuwar da Jidda ta yi ya ba Ibrahim damar kallonta sosai.

Salama ce ta ce

"Ke ma Jidda na faÉ—a miki ki daina damuwa kike addu'a kawai Allah zai baki mafita...

'Jidda?" Ibrahim ya furta a zuciyarsa

'Dama sunanta Jidda,.kenan Hauwa'u ce?' Ya tambayi zuciyarsa.

Yana ƙara jefawa zuciyarsa tambayar

'To mai yake damunta ake bata haƙuri?' Ya jefawa kansa tambayar da bashi da mai bashi amsa. Hannu ya kai jikin gilas ɗin saitin inda take tsaye ya dafa wajen.

Jidda idanunta cike da ƙwalla ta buɗe baki ta ce....

Furucin da Jiddar ta yi suka daki kunnuwan Ibrahim lokaci guda ya ga duhu ya maye hasken da yake gani, gabansa yana faɗuwa jin tashin hankalin da ya kai masa ziyara lokaci guda, da sauri ya koma ya zauna jingine da kujerar saɓanin da da ya ɗan taso yana taɓa jikin gilashin. Kansa ne ya sara da mugun ƙarfi yana jin ba zai jure wannan furucin na Jidda ba...

Wayyo hannuna🥺 10 readmore😫

*Mata masu aji akwai kayayyaki na tashin kan oga fa, akwai haɗaɗɗun tsumi da daka, da matsi ba na sakawa ba matsi da za ki tasafa ki shiga hajia, akwai na gyaran breast wacce breast nata ya kwanta lifet ta zo mu saka labule idan bata son dama kunu ina da na kwaya amma ba ƙwayar bature ba ƙwaya ta gargajiya, ingantattun itace haɗaɗu masu nagarta ki min magana in kina so ga no wayata a ƙasa*

MAMAN AFRAH
09025576222

‎Shin kinason hadaddun hijabs Wanda zaki ratsa ko Ina dasu?❤️kinason sanya hijabs masu fitarda asalin kyau da kyawun fuska?😹hijab din da Ana Ganinki ansan hijab neh?🥰 Anything hijjabs ask FUA ✅ got you covered.💃…Ba hijab kadai ba muna saida: inner caps, jersey veils, chantally veils and materials gowns ,jalbab,Hijab,Umrah set,lefe package,walima anko and lots more✨Muna bada sari a aika maka koina cikin Aminchi.
(location; kaduna,zaria and Gumel jigawa State,Muna delivery koina,niger,Ghana,saudia)

let us be your surest hijjabs plug,we give deliver the best.
[10/11, 9:47 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/CoSIFObGSJeG4TLAuJwo3J?mode=ems_copy_t

*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)

NA

MAMAN AFRAH

. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*

BOOK 1

PAGE 6️⃣

*SADIYA*

Ranta ne ya mata ƙuna tana jin wani zafi da raɗaɗi a zuciyarta, ta fara tunanin shin mai Nasir yake nufi da ita ne? Ta yaya za a yi mace ki dawo gidanki ki haɗu da mijin ki amma ko kallo baki ishe shi ba bare ki sa ran zai miki magana ko ya yi wa ɗan da kika haifa masa.

Kallon ƙaton kwaɗon da ya datse ƙofar ta yi a karo na biyu, tana jimami a zuciyarta ta ce
Chapter 11 · 0% Book details