Sashe 65
Dukan Ruwa Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
"Ban iya ƙiyayya ba, kamar yanda ban iya soyayya ba ka san da haka ko? Meyasa ka ke tunanin akwai ranar da zan iya haƙura da Humaira alhalin ba ta yimin laifin da zan ƙi ta ba har yau? Ko ka yi zaton ta taɓa wulaƙantani ko zagina? Toh Humaira ba ni ta wulaƙanta ba, soyayyar da na furta ina yi mata ta wulaƙanta, amma na yi mata uzurin kasancewarta daga jinsin Dan Adam wanda muka riga muka san ajizancinsa. Ka yi hakuri, na sani kana jin babu dadi yadda ake maka ƙorafi akan aurena har da masu nemana da sharri. Please ina son ka toshe kunnuwanka daga garesu. Duk radda ni Fadeel na furta maka cewa na bar Humaira, toh ka sani ina nufin rabuwa ta har abada, amma yanzu bana jin ko ɓurɓushin hakan a zuciyata. Ba na jin kuma wannan mafarki naka mai tabbatuwa ne saboda ba ta yimin kamun wasa ba. Ka bi wannan ɗan uwannaka da addu'a Ya Sheikh, komai zai zamo tarihi fa in sha Allahu."
Harara Ibb ya wurga masa jin ya ambace shi da sunan zolaya, Fadeel kuwa murmushi ya yi mishi yana ƙara yi mishi kirari da Angon Salma. Nan kuma ya saki fuska aka bar maganar gaba ɗaya.
***
Cikin hukuncin Allah, a kwana a tashi har tsawon lokacin da su Abba suka ƙara roƙar alfarma a yi bikin Ummita da Sahabi ya kusa cika, a sannan Humaira ta tattara ta bar gidan Futuha adalilin mijin Futuhar da ko kallo suke sai ya dinga kiran Humaira wai ta fito su yi kar ta ƙumshe a ɗaka. Ko kuma ya yi ta santin girki yana fadin ai kaf gidan su Futuha ta fi su iya girki, Futuha tun tana yaƙe har ta zo ta kasa jure ɓacin ranta ganin tashi guda ya siyo wani rantsetsen leshi dan dubu arba'in ya kawo wa Humaira matsayin ladan girki da take yi musu. Anan ne gaba daya ta sauya fuskarta ta ce Humaira ta tattara ta koma gida, ta sa direba ya kai ta bayan ta karɓe leshin. Ba tare da sanin cewa ita Humaira hakan ya fiye mata komai dadi ba don dama ta gaji da zaman gidan, dadinta daya bai wuce na ibadar da take yawan yi yanzu ba sosai, kuma abin mamaki koda Fadeel ya kira ta ta rage jin wannan tsanar da ɓacin ran sai dai ba yabo ba fallasa.
Tashin hankalin daake gudu dai shi ne ya afku, Abba ya zaunar da Sahabi da wani Kawunsa a dakin baƙi ya sanar da su abin da ke faruwa. Sahabi da yake jin wai wai a gari bai yarda ba ji ya yi har wani jiri na neman kwashe shi daga zaune. Kawunsa kuwa ya jinjina lamarin, ya kuma yi addu'ar Allah ya sauki Ummitan lafiya a karshe ya ce idan ta haihu ta yi aure ban da Sahabi don tuni dama sun yi mishi mata ganin ana ta yawo da hankalinsu akan Ummita. Sahabi ya kasa cewa uffan, idanunsa sun kaɗa. Tsakani da Allah yake son Ummita, ya kuma so aurenta, amma bisa gargadi iyayensa ga Kawu, matukar idan sun je ta tabbata ciki ne a jikin Ummita toh lallai su faɗi hakan. Sun kuma yi barazanar saɓawa Sahabi muddin ya musa zancen. Da wannan aka ƙulle mishi baki ya kasa cewa komai. Sai ma da zai tafi ne ya roƙi arziƙin ganin Ummita, nan Abba ya ba shi hakuri gami da nunamasa ba za ta iya jure ganinsa ba. Ya yi hakuri dai ya bi umarnin iyayensa. Daga wannan Sahabi ya ja jikinsa suka bar gidan bayan Abba ya damƙa musu dukkan wani abu da suka kawo da sunan aure.
Ummita na É—aki ban da kuka babu abin da take yi, Humaira wannan karon ta ma kasa rarrashinta, ga ciki ya fito ras ana gani kasancewar bai fi watanni biyu ya yi mata saura ta haihu ba. Ta shiga watanni bakwai cif. Ita kanta Humairar hawayen take yi tana gogewa. Ta dai tabbata shikenan Sahabi ya rabu da Ummita duk kuwa da irin dogon wayar da suke yi da soyayyar da suke nunawa juna.
"Kaddararki ce Ummita, kiyi hakuri mu rungumeta da hannu bibbiyu. Watarana komai zai zama tarihi."
Ta girgiza kai.
"Humaira na sani ƙaddarata ce, amma wallahi Humaira na tsani cikin jikina da abin da ke cikin. Ba zan taɓa sonsa ba. Humaira duk sadda cikina ya yi motsi ji nake kamar na ɗauki wuƙa na caka a cikin abin da ke cikin ya mutu gaba daya koda ace nima nawa ajalin kenan. Allah ya isa, Humaira ba zan taɓa yafewa azzaluman nan ba. Har gobe mummunan fuskokinsu na nan a kwakwalwata, wallahi yau idan Allah zai nunamin su, sai na raba su da numfashinsu."
Hawaye sosai itama Humaira take yi, balle kuma Raihana wacce shigowarta kenan dakin sanye da Uniform ta dawo daga makaranta ta tsinci labarin fasa auren Sahabi da Ummita kwata kwata a bakin Mami, kuka sosai take yi sanin irin kaunar da suke yiwa juna. Ta karaso ta rungume kafadar Ummita tana kuka tamkar ranta zai fita ta ma kasa magana. Sai Humaira ke aikin rarrashinsu cikin ƙarfin hali duk da itama hawayen ne ke zubomata.
"Humaira! Raihana!! Kuna ina?!"
Jin muryar Mubarak yana kiran sunansu murya a sama ya sanya su duban juna kafin su fito zuwa falon gaba daya ban da Ummita da ko motsi ta kasa. Kirjinta ne kawai ke dukan tara-tara, zai wahala ta yi mafarki bai afku ba, tana tsoron kuma yanzun ace mafarkin nata ne ya tabbata. Sai ta hau ambaton Innalillahi a ƙasan ranta.
Ba Mubarak ne kaɗai a falon ba, har da Mami da Abba wanda bai je kasuwa ba saboda lamarin fasa auren Ummita sosai ya taɓa ransa, dama kuma ya san da zuwan ranar, amma babu yanda iya.
"Kai Mubarak, mene ne haka kake ihu a gida?"
Mubarak da idanunsa suka kaɗa gaba daya ba cikin nutsuwarsa yake ba, daga shi sai singilet da wando three quarter, fuskarsa ta yi jazur abinka da farin mutum. Waya kawai ya miƙawa Abba, Mami da su Humaira har su na rige rigen zuwa leƙa saman wayar. Rubutu ne a ka yi dogo, headline din rubutun mai jan hankali sai ko rubutun.
_*GASKIYA TA YI HALINTA..._*
_*Rahina Sani da Humaira Yusuf wadanda kwanakin baya ake tunanin sace su aka yi, a yanzu gaskiya ta yi halinta._* _*Yan matan sun bi samarinsu ne yawon sharholiya inda a karshe har ɗaya ta zubar da cikin da ta yi yayinda ɗayar kuwa Allah ya tona asirinta cikin ya ƙi zubewa tana nan yanzu haihuwa yau ko gobe. Bincikenmu ya tabbatar da cewa ba sace su aka yi ba, dama ƴan hannu ne suka bi abokan watsewarsu ganin asirinsu zai tonu ne ya yi sanadin da suka haɗa baki suka yi ƙaryar an sace su._* *_Tabbas inda ranka za ka sha kallo da mamaki._*
 Sakin wayar Abba ya yi har yana taga-taga zai fadi, da taimakon su Mami dake kusa da shi ya samu ya zauna a kujera mafi kusa saboda rawar jiki. Humaira kuwa zuciyarta ke wani irin tafarfasa ranta idan ya yi dubu ya ɓaci, waye wannan ke kokarin ɓata musu suna a idon duniya? Mene ne ribarsa?
"Wannan wace irin rayuwa ce? Daga wannan sai wannan? Waye da wannan aikin? Kai Mubarak a ina ka samo mummunan labari haka?"
Duka wannan zantukan Abba ke yinsu lokaci guda cikin rawar murya mai nuni da zallar ɓacin rai. Mubarak da ya dauki wayarsa ya amsa.
"Abba ina zaune naga an turo group din da nake har da masu bibiyata ta inbox su na tambayar ko dagaske ne. Da na duba naga an yi forwarding sama da sau hamsin. Wannan ya sa na fahimci koda ace ba a jima da baza labarin ba, toh ya samu karɓuwa ainun."
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! A duniya ba ka sanin cewa kana da maƙiya sai irin hakan ta kasance. Ina so maganar nan ta tsaya iya mu da wadanda suka sani a gidan, koda wasa kar a faɗawa yarinyarnan ko don yanayin da take ciki. Mu rufe duk wata ƙofa da za ta tsinci labarin. A karɓe wayarta, ku kuma ku kiyayi tayar da zancen a gabanta. Ni kuma in sha Allahu sai inda ƙarfina ya ƙare wajen ganin an bi maku hakkinku, koda ace abin da na mallaka zai ƙare sai na sanya an bincikomin me wannan aika-aikar an hukuntashi ya kuma faɗi dalilinsa na aikata wannan abu."
Kowa a wurin ya gamsu da batun Abban, Mami kuwa tunani kawai take yi na waye wannan da ya fi ta nuna ƙiyayya ga yaran? Fatanta kar ya kasance wacce take zargi. Ta sani tunda har Abba ya ci akwashin ɗaukar mataki akan al'amarin to fa babu fashi.
Da wannan aka kashe zancen amma fa ran kowa a ɓace, koda su Humaira suka koma ɗaki, sun tarar Ummita ta shiga bandaki wannan ya sanya da sauri ta ɗauke wayarta ta kashe ta jefa a sif, da Ummitan ta fito ma babu wani a cikinsu da ya nuna mata komai. Ita ɗin ma ba ta lura da yanayinsu ba balle ta mayar da hankali, damuwar rashin Sahabi ya rinjayi komai. Tana buƙatar ganin ta samu nutsuwa ko ya ya ne, tana tsoron ciwon da damuwa za ta haifar mata. Wannan dalilin ne ya sanya ta jin tsoron tambayarsu dalilin kiran da Mubarak din ya yi musu, sai ta zaɓi yin shiru gami da kwanciya ta hau jan carbi.
Harara Ibb ya wurga masa jin ya ambace shi da sunan zolaya, Fadeel kuwa murmushi ya yi mishi yana ƙara yi mishi kirari da Angon Salma. Nan kuma ya saki fuska aka bar maganar gaba ɗaya.
***
Cikin hukuncin Allah, a kwana a tashi har tsawon lokacin da su Abba suka ƙara roƙar alfarma a yi bikin Ummita da Sahabi ya kusa cika, a sannan Humaira ta tattara ta bar gidan Futuha adalilin mijin Futuhar da ko kallo suke sai ya dinga kiran Humaira wai ta fito su yi kar ta ƙumshe a ɗaka. Ko kuma ya yi ta santin girki yana fadin ai kaf gidan su Futuha ta fi su iya girki, Futuha tun tana yaƙe har ta zo ta kasa jure ɓacin ranta ganin tashi guda ya siyo wani rantsetsen leshi dan dubu arba'in ya kawo wa Humaira matsayin ladan girki da take yi musu. Anan ne gaba daya ta sauya fuskarta ta ce Humaira ta tattara ta koma gida, ta sa direba ya kai ta bayan ta karɓe leshin. Ba tare da sanin cewa ita Humaira hakan ya fiye mata komai dadi ba don dama ta gaji da zaman gidan, dadinta daya bai wuce na ibadar da take yawan yi yanzu ba sosai, kuma abin mamaki koda Fadeel ya kira ta ta rage jin wannan tsanar da ɓacin ran sai dai ba yabo ba fallasa.
Tashin hankalin daake gudu dai shi ne ya afku, Abba ya zaunar da Sahabi da wani Kawunsa a dakin baƙi ya sanar da su abin da ke faruwa. Sahabi da yake jin wai wai a gari bai yarda ba ji ya yi har wani jiri na neman kwashe shi daga zaune. Kawunsa kuwa ya jinjina lamarin, ya kuma yi addu'ar Allah ya sauki Ummitan lafiya a karshe ya ce idan ta haihu ta yi aure ban da Sahabi don tuni dama sun yi mishi mata ganin ana ta yawo da hankalinsu akan Ummita. Sahabi ya kasa cewa uffan, idanunsa sun kaɗa. Tsakani da Allah yake son Ummita, ya kuma so aurenta, amma bisa gargadi iyayensa ga Kawu, matukar idan sun je ta tabbata ciki ne a jikin Ummita toh lallai su faɗi hakan. Sun kuma yi barazanar saɓawa Sahabi muddin ya musa zancen. Da wannan aka ƙulle mishi baki ya kasa cewa komai. Sai ma da zai tafi ne ya roƙi arziƙin ganin Ummita, nan Abba ya ba shi hakuri gami da nunamasa ba za ta iya jure ganinsa ba. Ya yi hakuri dai ya bi umarnin iyayensa. Daga wannan Sahabi ya ja jikinsa suka bar gidan bayan Abba ya damƙa musu dukkan wani abu da suka kawo da sunan aure.
Ummita na É—aki ban da kuka babu abin da take yi, Humaira wannan karon ta ma kasa rarrashinta, ga ciki ya fito ras ana gani kasancewar bai fi watanni biyu ya yi mata saura ta haihu ba. Ta shiga watanni bakwai cif. Ita kanta Humairar hawayen take yi tana gogewa. Ta dai tabbata shikenan Sahabi ya rabu da Ummita duk kuwa da irin dogon wayar da suke yi da soyayyar da suke nunawa juna.
"Kaddararki ce Ummita, kiyi hakuri mu rungumeta da hannu bibbiyu. Watarana komai zai zama tarihi."
Ta girgiza kai.
"Humaira na sani ƙaddarata ce, amma wallahi Humaira na tsani cikin jikina da abin da ke cikin. Ba zan taɓa sonsa ba. Humaira duk sadda cikina ya yi motsi ji nake kamar na ɗauki wuƙa na caka a cikin abin da ke cikin ya mutu gaba daya koda ace nima nawa ajalin kenan. Allah ya isa, Humaira ba zan taɓa yafewa azzaluman nan ba. Har gobe mummunan fuskokinsu na nan a kwakwalwata, wallahi yau idan Allah zai nunamin su, sai na raba su da numfashinsu."
Hawaye sosai itama Humaira take yi, balle kuma Raihana wacce shigowarta kenan dakin sanye da Uniform ta dawo daga makaranta ta tsinci labarin fasa auren Sahabi da Ummita kwata kwata a bakin Mami, kuka sosai take yi sanin irin kaunar da suke yiwa juna. Ta karaso ta rungume kafadar Ummita tana kuka tamkar ranta zai fita ta ma kasa magana. Sai Humaira ke aikin rarrashinsu cikin ƙarfin hali duk da itama hawayen ne ke zubomata.
"Humaira! Raihana!! Kuna ina?!"
Jin muryar Mubarak yana kiran sunansu murya a sama ya sanya su duban juna kafin su fito zuwa falon gaba daya ban da Ummita da ko motsi ta kasa. Kirjinta ne kawai ke dukan tara-tara, zai wahala ta yi mafarki bai afku ba, tana tsoron kuma yanzun ace mafarkin nata ne ya tabbata. Sai ta hau ambaton Innalillahi a ƙasan ranta.
Ba Mubarak ne kaɗai a falon ba, har da Mami da Abba wanda bai je kasuwa ba saboda lamarin fasa auren Ummita sosai ya taɓa ransa, dama kuma ya san da zuwan ranar, amma babu yanda iya.
"Kai Mubarak, mene ne haka kake ihu a gida?"
Mubarak da idanunsa suka kaɗa gaba daya ba cikin nutsuwarsa yake ba, daga shi sai singilet da wando three quarter, fuskarsa ta yi jazur abinka da farin mutum. Waya kawai ya miƙawa Abba, Mami da su Humaira har su na rige rigen zuwa leƙa saman wayar. Rubutu ne a ka yi dogo, headline din rubutun mai jan hankali sai ko rubutun.
_*GASKIYA TA YI HALINTA..._*
_*Rahina Sani da Humaira Yusuf wadanda kwanakin baya ake tunanin sace su aka yi, a yanzu gaskiya ta yi halinta._* _*Yan matan sun bi samarinsu ne yawon sharholiya inda a karshe har ɗaya ta zubar da cikin da ta yi yayinda ɗayar kuwa Allah ya tona asirinta cikin ya ƙi zubewa tana nan yanzu haihuwa yau ko gobe. Bincikenmu ya tabbatar da cewa ba sace su aka yi ba, dama ƴan hannu ne suka bi abokan watsewarsu ganin asirinsu zai tonu ne ya yi sanadin da suka haɗa baki suka yi ƙaryar an sace su._* *_Tabbas inda ranka za ka sha kallo da mamaki._*
 Sakin wayar Abba ya yi har yana taga-taga zai fadi, da taimakon su Mami dake kusa da shi ya samu ya zauna a kujera mafi kusa saboda rawar jiki. Humaira kuwa zuciyarta ke wani irin tafarfasa ranta idan ya yi dubu ya ɓaci, waye wannan ke kokarin ɓata musu suna a idon duniya? Mene ne ribarsa?
"Wannan wace irin rayuwa ce? Daga wannan sai wannan? Waye da wannan aikin? Kai Mubarak a ina ka samo mummunan labari haka?"
Duka wannan zantukan Abba ke yinsu lokaci guda cikin rawar murya mai nuni da zallar ɓacin rai. Mubarak da ya dauki wayarsa ya amsa.
"Abba ina zaune naga an turo group din da nake har da masu bibiyata ta inbox su na tambayar ko dagaske ne. Da na duba naga an yi forwarding sama da sau hamsin. Wannan ya sa na fahimci koda ace ba a jima da baza labarin ba, toh ya samu karɓuwa ainun."
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! A duniya ba ka sanin cewa kana da maƙiya sai irin hakan ta kasance. Ina so maganar nan ta tsaya iya mu da wadanda suka sani a gidan, koda wasa kar a faɗawa yarinyarnan ko don yanayin da take ciki. Mu rufe duk wata ƙofa da za ta tsinci labarin. A karɓe wayarta, ku kuma ku kiyayi tayar da zancen a gabanta. Ni kuma in sha Allahu sai inda ƙarfina ya ƙare wajen ganin an bi maku hakkinku, koda ace abin da na mallaka zai ƙare sai na sanya an bincikomin me wannan aika-aikar an hukuntashi ya kuma faɗi dalilinsa na aikata wannan abu."
Kowa a wurin ya gamsu da batun Abban, Mami kuwa tunani kawai take yi na waye wannan da ya fi ta nuna ƙiyayya ga yaran? Fatanta kar ya kasance wacce take zargi. Ta sani tunda har Abba ya ci akwashin ɗaukar mataki akan al'amarin to fa babu fashi.
Da wannan aka kashe zancen amma fa ran kowa a ɓace, koda su Humaira suka koma ɗaki, sun tarar Ummita ta shiga bandaki wannan ya sanya da sauri ta ɗauke wayarta ta kashe ta jefa a sif, da Ummitan ta fito ma babu wani a cikinsu da ya nuna mata komai. Ita ɗin ma ba ta lura da yanayinsu ba balle ta mayar da hankali, damuwar rashin Sahabi ya rinjayi komai. Tana buƙatar ganin ta samu nutsuwa ko ya ya ne, tana tsoron ciwon da damuwa za ta haifar mata. Wannan dalilin ne ya sanya ta jin tsoron tambayarsu dalilin kiran da Mubarak din ya yi musu, sai ta zaɓi yin shiru gami da kwanciya ta hau jan carbi.