Sashe 36
Dukan Ruwa Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
"Aure ai abin so ne saboda sunnar ma'aiki (s.a.w) ne. Ke din ma ba sunnar kika tsana ba, mazan ne. Ban kuma san laifi kwakkwara da suka yi gareki ba."
Taɓe baki Humaira ta yi daidai lokacin da suka fito babban titi.
"Mu bar wannan magana, nikam ba kya ganin lamarin Anti Jannat da É—aure kai?"
Ummita ta yi shiru cikin nazari, tabbas da daure kai, tun bayan sadda ta zo hutun sallah lamarin nan ya afkuwa tsakaninta da ita, ba ta kara dawowa gidan ba sai yanzu. Wannan dawowar kuwa, daidai da kallon Humaira ba ta yi balle har ta jefe ta da kallon banza. Ta lura ko tana wuri Humaira ta shiga, mikewa take ta bar wurin. Haka dai tana ta kaucewa abinda zai haɗa su a inuwa guda.Har Humaira ta tarar musu abin hawa suka shiga ba ta amsa mata tambayarta ba sai da ta ƙara nanatawa kafin ta sauke ajiyar zuciya ta ɗan yi murmushi.
 Â
  "Na lura sosai, amma ni abin da tunanina ya ban ko dai ta sauya ne tana gudun wani abu ya ƙara haɗaku ki maimaita abin da kika yi. Kin san fa ba zai yiwu ace ta mance ba."
Dariya ta yi.
"Ikon Allah, toh ni ai na mance. Kawai dai sauyin ne ya É—an bani mamaki. Babu kyara babu hantara, babu kirana da bare da ta saba yi ba komai. Sai na ke ganin kamar da walakin goro a miya."
"Ki yi mata kyakkyawan zato, Allah yasa sanadin abin da ya kasance ta yiwa kanta faÉ—a. Ni kaina idan kin lura ai ta rage É—oramin aiki tunda wannan zuwan ta sa an nemo mata yarinya mai kula da yara. Kawai dai mun saba da yaranta ba yanda za a yi ta iya raba wannan kaunar."
Humaira ta kalle ta, zuciyar Ummita mai kyau ne, da Allah ya tashi, sai ya yi haɗa ta da mutumin kirki irinta wato Malam Sahabi. Mutum mai hakuri da kunya kamar wani mace. Amma abin mamaki duk kunyarsa idan suka ga saƙonnin soyayyar da yake turowa Ummita sai mamaki ya kusan kashe su ita da Raihana. Har rantsuwa suke kusan yi su ce ba shi ba ne waninsa ne.
Ummita ta harareta.
"Kallon fa?"
Murmushi Humaira ta yi mai kyau da ya fiddo wushiryarta.
"Kawai kina bani mamaki da kike kokarin kare wadannan mutanen da ba su taɓa kaunarmu ba koyaushe."
"Uzurin kenan Humaira. Aure fa zasu yi su bar mu yanzu. Mu ma kuma..."
"Toh naji ya ishe ni hakanan Malama matar Sahabi."
Ummita ta sa dariyar jin abinda ya fito bakinta, ita din ma taya ta ta yi. Har suka isa ƙofar asibitin su na hira abinsu ana iska kaɗan kaɗan mai daɗi.
 Â
  Ibb ne tsaye tare da masoyiyarsa Dr Salma, yayinda Fadeel ke zaune cikin mota yana jira su yi sallama. Mahaifiyarta ce kwamce a asibitin inda anan take aiki, suka zo dubiya ta yo musu rakiya har gaban mota. Bayan sallama da Fadeel ya koma mota yayinda suke hirarsu da Ibb tamkar kada su rabu, shi kuwa Fadeel kansa ya kwantar jikin kujera yana ɗan kallonsu yana murmushi. Shakka babu sun dace dari bisa dari. Dogaye ne su duka biyun don zasu kusan yin kai ɗaya, Dakta Salma baƙa ce, kwayoyin idanunta da haƙora ne kawai idan ta bude masu haske a fuskarta. Tana da kyau, ba ta da jiki sosai amma ba za ka kirata da siririya ba. Tana da diri masha Allah, sanya take da doguwar riga sai coat na likitoci da ta sanya saman kayan, sai kuwa mayafi ƙarami da ta yi rolling kanta da shi. Hannunta cikin aljihun rigar, gaba daya hankalinsu ba ya kan Fadeel da ya lula duniyar tunani da jin inama ace shi da Humaira ke wannan hirar ta nishaɗi. Allah kaɗai yasan yanda zai ji a lokacin. Ya soma gajiya, hakurinsa ya soma kai wa karshe amma yana dannewa gudun ɓacin ranta. Ya horu da rashin ganinta ido da ido ba hoto ba, ya sha zuwa ya tsaya a nesa kaɗan da gidansu ko zai ga wulkawarta sai dai ko mai kama da ita Allah bai taɓa ba shi ikon gani ba. Tabbas Raihana na kokari gurin aikamasa hotunanta wasu lokutan ma ba ta san ana ɗaukarta ba. Hatta da karamin video sadda take aikin snacks sai da ta ɗauka ta aikamasa. Yakan ji inama yana da iko da ita, inama matarsa ce yana kusa ya riƙo ƙugunta ya sanya ta a jikinsa ya bayyana mata irin yanda soyayyarta ke cin zuciyarsa sai dai kuma babu hali. Azabar da bidiyon ke sanya shi ciki ne ya sanya shi dakatar da Raihana daga turo bidiyo face hotuna.
 Ya ja dogon numfashi ya furzar gami da kallon gefe guda yana mai kauda kai daga kan lovebirds. Hango wata ya yi kamar Humaira, ya ɗan yi tsai da idanu don so ya tantance abinda yake gani, sai kuma ya kauda kai. Ya fi tunanin gizo Humaira ta soma yi mishi, sai kuma ya kara kallo. Wannan karon ita ce tabbas, tana sanye da doguwar riga na material mai mayafi Jajaye. Yanayin kalar da garin ya yi, sai ya ba wa hasken fuskarta damar sheƙi musamman da ya kasance tana cikin annashuwa da kwanciyar hankali da alama babu wani abu dake damunta. Sai hira suke da abokiyar tafiyarta wadda ya gane ta, Ummita ce. Ya ganta a hoto don ba hoton Humaira kaɗai ba, hatta da ƴan gidan sai da Raihana ta turamishi hotunansu da kuma bayanin alaƙarsu. Har ya kama murfin mota zai fito ya tuna alƙawarin shekara da ya ɗaukar mata kawai ya fasa ya cigaba da kallonta. Dab da motar suka tsaya suna kalle-kalle kasancewar gilasanta tinted ya sa basu ganshi ba, shi kuwa Ibb shalelan Juliet, bai ma gansu ba ya lula wata duniyar sai buɗe haƙora yake yi kamar gonar auduga.
Humaira ta É—an yamutse fuska tana gyara gyalenta da iska ke kaÉ—awa.
"Nikam asibitin nan juyar da kai gareshi, don Allah ƙara kiranta ki ce bamu gane wajen da ta ce ba kinga garin yana kara haɗewa."
Itama Ummita duk ta damu ganin hadari ta fiddo waya ta dannawa Sadiya. Nan ta ce su tsaya inda suke ta gansu.
Suka ja kuwa suka tsaya, Humaira ta zubawa mutanen dake ta shawagi a wurin idanu tana godiya ga Allah a ranta idan ta ga an wuce da marasa lafiya dayake suna daidai Emergency. Ba su wani jima ba sai ga Sadiyar ta iso, bayan sun gaisa ta karɓa ta yi musu godiya suka juya suka kama hanyar fita.
Fadeel kamar wanda aka tsikarawa allura haka ya zabura ya fito daga motar ya dubi Ibb.
"Malam ka zo mu tafi ba ka ganin yanda garin ke haÉ—ewa wai?"
Suka dubeshi, Dakta Salma ta yi murmushi.
"We are sorry Amininmu. Bari na kyale shi haka. Nagode sosai ku gaida gida."
Bai ko kalleta ba ya amsa da toh don shi gaba daya hankalinsa na ga su Humaira yana fatan Allah ya sa su amince su sauke su a gida. Ibb ganin an soma yayyafi ya yi mata sallama ya shiga motar ya tayar.
"Please and please ka yi sauri kada su hau abin hawa, so nake ko yaya ka yimin kokari ta amince mu kai su gida."
Ya tayar da motar ya soma tafiya sannan ya dubi Fadeel cikin rashin fahimta ya ce.
"Wa kenan kake magana a kai?"
Fadeel da idanunsa ke kan su Humaira wadanda suka kara ɗaga ƙafa ganin ruwa ya soma sauka bai ce komai ba face nuni da ya yi mishi da hannu. Sam bai ga fuskokinsu ba sai baya, kafin ya yi magana Fadeel ya sake tarar numfashinsa.
"Humaira ce."
"Ohh." Abin da kawai Ibb ya ce kenan.
Yana zuwa daidai saitin inda suke ya tsaya har yana tare musu hanya, Humaira dake saitin wurin ta kalli motar ranta a ɓace don a ganinta ko waye yana sane ya sha gabansu. Ta bude baki da zummar magana Ibb ya sauke gilashi suka kalli juna. A gaggauce ta gaishe shi, itama Ummita haka, ta gane shi saboda tana ganin hotunansa a wayar Raihana, shi ne dai wanda y taimaki Raihanar.
"Gida ku ka nufa ne? Ku shiga na sauke ku don yanzu idan ku ka shiga napep jiƙewa zaku yi."
Ruwan sosai ya ƙara ƙarfi, Humaira ta buɗe baki za ta ja musu Ummita ta dafe hannun da sauri ta amsa.
"Toh mungode." Ta kalli Humaira, a hankali kuma a gaggauce ta ce.
"Muje Humaira, yanzu ba lokacin jan musu ba ne, wallahi nidai ina mura kin sani, ruwannan ya dake ni kuma lafkewa zan yi da bikin nan."
Jin haka Humaira ta amince suka shiga, ita ta soma shigewa sai Ummita. Motar sanyi sakamakon Ac dake aiki. Sai a lokacin ta lura da wanda ke zaune a gefen Ibb din, ji ta yi kirjinta ya buga dam, ta rasa dalilin bugawar kamar yanda ta kasa dauke idanu a kansa. Shi ɗinma ita yake kallo babu ƙakƙautawa har bai iya ya amsa gaisuwar Ummita ba. A bangaren Humaira ji ta yi idan ta cigaba da kallonsa ranta zai iya fita saboda wani irin zafi da take ji a kirjinta ga kanta dake faman sarawa don haka da sauri ta kauda kai ta matsa ta maƙure a kujerar bayansa tana jingina da kofar motar. A hankali Ibb ya dan bubbuga kafaɗar Fadeel, firgigit ya dawo hayyacinsa ya gyara zama, gilashinsa ya zaro a aljihu ya rufe kwayoyin idanun da so da tsananin kauna ga kewa suka haɗu suka galabaitar. Dakyar Humaira ta iya gaida Ibb sannan ta gaida Fadeel din ba tare da ambaton suna ba. Shi ma amsawa ya yi can ƙasa.
Ibb ke tambayar Ummita abin da ya kawo su asibiti.
"Kuna da marar lafiya ne?"
"Aa, aiko mu dai Anti Tasleem ta yi. Ita É—in É—aliba ce a nan. Nursing take karantawa ne."
Dan jinjina kai Ibb ya yi.
"Ok, na fahimta."
Jin motar ta ɗauki shiru sai rediyo dake aiki sai ko ruwa da ke jiƙa gilasan motar yana sauka a guje saboda karfin da ya yi. Ummita ta dubi Humaira.
"Wai, da tuni yanzu fa mun jiƙe."
Taɓe baki Humaira ta yi daidai lokacin da suka fito babban titi.
"Mu bar wannan magana, nikam ba kya ganin lamarin Anti Jannat da É—aure kai?"
Ummita ta yi shiru cikin nazari, tabbas da daure kai, tun bayan sadda ta zo hutun sallah lamarin nan ya afkuwa tsakaninta da ita, ba ta kara dawowa gidan ba sai yanzu. Wannan dawowar kuwa, daidai da kallon Humaira ba ta yi balle har ta jefe ta da kallon banza. Ta lura ko tana wuri Humaira ta shiga, mikewa take ta bar wurin. Haka dai tana ta kaucewa abinda zai haɗa su a inuwa guda.Har Humaira ta tarar musu abin hawa suka shiga ba ta amsa mata tambayarta ba sai da ta ƙara nanatawa kafin ta sauke ajiyar zuciya ta ɗan yi murmushi.
 Â
  "Na lura sosai, amma ni abin da tunanina ya ban ko dai ta sauya ne tana gudun wani abu ya ƙara haɗaku ki maimaita abin da kika yi. Kin san fa ba zai yiwu ace ta mance ba."
Dariya ta yi.
"Ikon Allah, toh ni ai na mance. Kawai dai sauyin ne ya É—an bani mamaki. Babu kyara babu hantara, babu kirana da bare da ta saba yi ba komai. Sai na ke ganin kamar da walakin goro a miya."
"Ki yi mata kyakkyawan zato, Allah yasa sanadin abin da ya kasance ta yiwa kanta faÉ—a. Ni kaina idan kin lura ai ta rage É—oramin aiki tunda wannan zuwan ta sa an nemo mata yarinya mai kula da yara. Kawai dai mun saba da yaranta ba yanda za a yi ta iya raba wannan kaunar."
Humaira ta kalle ta, zuciyar Ummita mai kyau ne, da Allah ya tashi, sai ya yi haɗa ta da mutumin kirki irinta wato Malam Sahabi. Mutum mai hakuri da kunya kamar wani mace. Amma abin mamaki duk kunyarsa idan suka ga saƙonnin soyayyar da yake turowa Ummita sai mamaki ya kusan kashe su ita da Raihana. Har rantsuwa suke kusan yi su ce ba shi ba ne waninsa ne.
Ummita ta harareta.
"Kallon fa?"
Murmushi Humaira ta yi mai kyau da ya fiddo wushiryarta.
"Kawai kina bani mamaki da kike kokarin kare wadannan mutanen da ba su taɓa kaunarmu ba koyaushe."
"Uzurin kenan Humaira. Aure fa zasu yi su bar mu yanzu. Mu ma kuma..."
"Toh naji ya ishe ni hakanan Malama matar Sahabi."
Ummita ta sa dariyar jin abinda ya fito bakinta, ita din ma taya ta ta yi. Har suka isa ƙofar asibitin su na hira abinsu ana iska kaɗan kaɗan mai daɗi.
 Â
  Ibb ne tsaye tare da masoyiyarsa Dr Salma, yayinda Fadeel ke zaune cikin mota yana jira su yi sallama. Mahaifiyarta ce kwamce a asibitin inda anan take aiki, suka zo dubiya ta yo musu rakiya har gaban mota. Bayan sallama da Fadeel ya koma mota yayinda suke hirarsu da Ibb tamkar kada su rabu, shi kuwa Fadeel kansa ya kwantar jikin kujera yana ɗan kallonsu yana murmushi. Shakka babu sun dace dari bisa dari. Dogaye ne su duka biyun don zasu kusan yin kai ɗaya, Dakta Salma baƙa ce, kwayoyin idanunta da haƙora ne kawai idan ta bude masu haske a fuskarta. Tana da kyau, ba ta da jiki sosai amma ba za ka kirata da siririya ba. Tana da diri masha Allah, sanya take da doguwar riga sai coat na likitoci da ta sanya saman kayan, sai kuwa mayafi ƙarami da ta yi rolling kanta da shi. Hannunta cikin aljihun rigar, gaba daya hankalinsu ba ya kan Fadeel da ya lula duniyar tunani da jin inama ace shi da Humaira ke wannan hirar ta nishaɗi. Allah kaɗai yasan yanda zai ji a lokacin. Ya soma gajiya, hakurinsa ya soma kai wa karshe amma yana dannewa gudun ɓacin ranta. Ya horu da rashin ganinta ido da ido ba hoto ba, ya sha zuwa ya tsaya a nesa kaɗan da gidansu ko zai ga wulkawarta sai dai ko mai kama da ita Allah bai taɓa ba shi ikon gani ba. Tabbas Raihana na kokari gurin aikamasa hotunanta wasu lokutan ma ba ta san ana ɗaukarta ba. Hatta da karamin video sadda take aikin snacks sai da ta ɗauka ta aikamasa. Yakan ji inama yana da iko da ita, inama matarsa ce yana kusa ya riƙo ƙugunta ya sanya ta a jikinsa ya bayyana mata irin yanda soyayyarta ke cin zuciyarsa sai dai kuma babu hali. Azabar da bidiyon ke sanya shi ciki ne ya sanya shi dakatar da Raihana daga turo bidiyo face hotuna.
 Ya ja dogon numfashi ya furzar gami da kallon gefe guda yana mai kauda kai daga kan lovebirds. Hango wata ya yi kamar Humaira, ya ɗan yi tsai da idanu don so ya tantance abinda yake gani, sai kuma ya kauda kai. Ya fi tunanin gizo Humaira ta soma yi mishi, sai kuma ya kara kallo. Wannan karon ita ce tabbas, tana sanye da doguwar riga na material mai mayafi Jajaye. Yanayin kalar da garin ya yi, sai ya ba wa hasken fuskarta damar sheƙi musamman da ya kasance tana cikin annashuwa da kwanciyar hankali da alama babu wani abu dake damunta. Sai hira suke da abokiyar tafiyarta wadda ya gane ta, Ummita ce. Ya ganta a hoto don ba hoton Humaira kaɗai ba, hatta da ƴan gidan sai da Raihana ta turamishi hotunansu da kuma bayanin alaƙarsu. Har ya kama murfin mota zai fito ya tuna alƙawarin shekara da ya ɗaukar mata kawai ya fasa ya cigaba da kallonta. Dab da motar suka tsaya suna kalle-kalle kasancewar gilasanta tinted ya sa basu ganshi ba, shi kuwa Ibb shalelan Juliet, bai ma gansu ba ya lula wata duniyar sai buɗe haƙora yake yi kamar gonar auduga.
Humaira ta É—an yamutse fuska tana gyara gyalenta da iska ke kaÉ—awa.
"Nikam asibitin nan juyar da kai gareshi, don Allah ƙara kiranta ki ce bamu gane wajen da ta ce ba kinga garin yana kara haɗewa."
Itama Ummita duk ta damu ganin hadari ta fiddo waya ta dannawa Sadiya. Nan ta ce su tsaya inda suke ta gansu.
Suka ja kuwa suka tsaya, Humaira ta zubawa mutanen dake ta shawagi a wurin idanu tana godiya ga Allah a ranta idan ta ga an wuce da marasa lafiya dayake suna daidai Emergency. Ba su wani jima ba sai ga Sadiyar ta iso, bayan sun gaisa ta karɓa ta yi musu godiya suka juya suka kama hanyar fita.
Fadeel kamar wanda aka tsikarawa allura haka ya zabura ya fito daga motar ya dubi Ibb.
"Malam ka zo mu tafi ba ka ganin yanda garin ke haÉ—ewa wai?"
Suka dubeshi, Dakta Salma ta yi murmushi.
"We are sorry Amininmu. Bari na kyale shi haka. Nagode sosai ku gaida gida."
Bai ko kalleta ba ya amsa da toh don shi gaba daya hankalinsa na ga su Humaira yana fatan Allah ya sa su amince su sauke su a gida. Ibb ganin an soma yayyafi ya yi mata sallama ya shiga motar ya tayar.
"Please and please ka yi sauri kada su hau abin hawa, so nake ko yaya ka yimin kokari ta amince mu kai su gida."
Ya tayar da motar ya soma tafiya sannan ya dubi Fadeel cikin rashin fahimta ya ce.
"Wa kenan kake magana a kai?"
Fadeel da idanunsa ke kan su Humaira wadanda suka kara ɗaga ƙafa ganin ruwa ya soma sauka bai ce komai ba face nuni da ya yi mishi da hannu. Sam bai ga fuskokinsu ba sai baya, kafin ya yi magana Fadeel ya sake tarar numfashinsa.
"Humaira ce."
"Ohh." Abin da kawai Ibb ya ce kenan.
Yana zuwa daidai saitin inda suke ya tsaya har yana tare musu hanya, Humaira dake saitin wurin ta kalli motar ranta a ɓace don a ganinta ko waye yana sane ya sha gabansu. Ta bude baki da zummar magana Ibb ya sauke gilashi suka kalli juna. A gaggauce ta gaishe shi, itama Ummita haka, ta gane shi saboda tana ganin hotunansa a wayar Raihana, shi ne dai wanda y taimaki Raihanar.
"Gida ku ka nufa ne? Ku shiga na sauke ku don yanzu idan ku ka shiga napep jiƙewa zaku yi."
Ruwan sosai ya ƙara ƙarfi, Humaira ta buɗe baki za ta ja musu Ummita ta dafe hannun da sauri ta amsa.
"Toh mungode." Ta kalli Humaira, a hankali kuma a gaggauce ta ce.
"Muje Humaira, yanzu ba lokacin jan musu ba ne, wallahi nidai ina mura kin sani, ruwannan ya dake ni kuma lafkewa zan yi da bikin nan."
Jin haka Humaira ta amince suka shiga, ita ta soma shigewa sai Ummita. Motar sanyi sakamakon Ac dake aiki. Sai a lokacin ta lura da wanda ke zaune a gefen Ibb din, ji ta yi kirjinta ya buga dam, ta rasa dalilin bugawar kamar yanda ta kasa dauke idanu a kansa. Shi ɗinma ita yake kallo babu ƙakƙautawa har bai iya ya amsa gaisuwar Ummita ba. A bangaren Humaira ji ta yi idan ta cigaba da kallonsa ranta zai iya fita saboda wani irin zafi da take ji a kirjinta ga kanta dake faman sarawa don haka da sauri ta kauda kai ta matsa ta maƙure a kujerar bayansa tana jingina da kofar motar. A hankali Ibb ya dan bubbuga kafaɗar Fadeel, firgigit ya dawo hayyacinsa ya gyara zama, gilashinsa ya zaro a aljihu ya rufe kwayoyin idanun da so da tsananin kauna ga kewa suka haɗu suka galabaitar. Dakyar Humaira ta iya gaida Ibb sannan ta gaida Fadeel din ba tare da ambaton suna ba. Shi ma amsawa ya yi can ƙasa.
Ibb ke tambayar Ummita abin da ya kawo su asibiti.
"Kuna da marar lafiya ne?"
"Aa, aiko mu dai Anti Tasleem ta yi. Ita É—in É—aliba ce a nan. Nursing take karantawa ne."
Dan jinjina kai Ibb ya yi.
"Ok, na fahimta."
Jin motar ta ɗauki shiru sai rediyo dake aiki sai ko ruwa da ke jiƙa gilasan motar yana sauka a guje saboda karfin da ya yi. Ummita ta dubi Humaira.
"Wai, da tuni yanzu fa mun jiƙe."